Sashe 66
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tab'e baki Aziza ta yi tace "Ai kam ba shi da maraba da shanyayye."
"To ai ba kama bace, duk alamu sun nuna shegiyar yarinyar nan ita ce mai laifi, wallahi sai yanzu ne nake na tabbatar da tun farko *kallon kitse mu ka yi wa rogo*."
Nura da ke fitowa daga d'akin shi cikin sauri ne ya kalle su dukansu yace "Ku sai yanzu ma ku ka sani kenan? To mu zuba zuwa mu ga mu da ku waye zaiyi nasara, 'yan bayan Khadija ko 'yan bayan wannan mai kama da agwagwar."
Hajia ce tace "Abun bak'in cikin ma wallahi ta yanda gaba d'aya ta raba shi da mutane, d'an taimakon da muke san mu mi shi bamu ma gan shi ba bare mu taimaka d'in, amma ba dan haka ba da yanzu nasan komai ya wuce, kuma kinga shi malam ya ma bar maganar kamar baisan me ke faruwa ba."
Nura dai ficewa ya yi ya kama sabgar gaban shi sai Rabi'a da tace "Ai kuwa ba za mu yarda ba wallahi, ni zanje gidan na ga me ke faruwa, wallahi saina fad'a mata magana."
"Ai kuwa in ban cire ki a cikin dangin shi ba to tabbas zaki sha dukan tsiya." Cewar Aziza, da mamaki Rabi'a tace "Kamar ya duka? Ba shi da lafiya?"
Aziza ce tace "Lafiyar shi lau, amma babu mai tab'a ta ya yi shiru, akan haka fa ya kori Garba mai gadi."
Hajia ce tace "Ni kai na da zan ganshi da sai ran shi ya b'ace, tunda aka fara hidimar nan har yanzu banga k'eyar shi gidan nan ba, kuma ni har yanzu daga Nura har malam banji wanda yace ya bashi gudummuwar bikin nan ba, akwai abubuwa dayawa wanda da shi ne mu ka dogara, ba dan Allah ya rufa mana asiri ba yanzu yarinyar nan sun aiko da wannan gudummuwar ta su da ya za mu yi."
Hassana ce tace "Bai fa bayar da komai ba hajia?"
"Ni dai bai bani ba, kuma Nura da malam ba su fad'a min ba, kinga ko abune mai wuya ace sun kasa fad'a min."
Husseina ce tace "Ah ba ma ta yiwu ai, in har ya bayar dole sai ki sani Hajia."
"To me ya ke nufi? Ba zai bayar ba ko ta hana shi?" Cewar Rabi'a, Hajia ce tace "Gidan fa da za akai amarya ma Murtala ne ya bashi gidan, da ina jin har yanzu ba mu san ina za su zauna ba."
"Wallahi sai naje, sai dai ya kashe ni." Cewar Rabi'a cikin b'acin rai ta na mik'ewa ta yi kam ba b'ata lokaci ta saka hijabin ta, Hassana ce tace ita ma za ta je ta jira ta, Husseina dai cewa ta yi "Allah ya kad'e hau." Ko amsata ba su yi ba su ka tafi, cikin k'ank'anin lokaci su ka isa gidan, sunyi nasarar samun falon Haseenah bud'e, shiga su ka yi da sallama amma ba kowa sai telebijin ita kad'ai, zaune su ka yi sai Rabi'a da ke ci gaba da rumtuma sallama dan suji su fito.
*Alhamdulillah Ala ni'imatul islam.*
27/02/2020 à 13:42 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*33*
Tun su na sallama har su kai su ka yi shiru babu wanda ya amsa, suna magana k'asa kasa su ka ji an bud'a k'ofa, mayar da kallon su su ka yi ga mai fitowa, wa za su gani in ba Usman ba da doguwar riga kamar wanda ya taso daga bacci, da kallo su ka bishi har ya k'araso ya zauna ba su daina kallon shi ba, cikin wani cijewa yace "Ashe kune? Daga ina haka?"
Hassana ce tace "Ina wuni?" Bai amsa ba sai shafa kan shi da ya fara yi, Rabi'a ce tace "Dama Hajia ce tace mu zo mu ga ko kuna lafiya, daga kai har Hassenah ta jima ba ta gan ku ba."
Kamar wanda aka takura wajen maganar ya ke fad'in "Tsohin nan matsala ce da su wallahi, ko shekaran jiya fa na je gidan mun gaisa, lafiya k'alau na ke ni, ita ce ma dai ba ta jin dad'i, yau lafiya gobe ba lafiya."
Hassana ce tace "Shi ya sa har an fara shagulgulan bikin nan amma har yanzu babu wanda ya gan ta? Yah Fodio ka na ganin hakan ya yi daidai domin Allah, akwai fa abubu..."
"Ke dakata." Ya katse ta ya na mik'ewa tsaye, da yatsa ya nuna ta yace "Ke ma 'yar hassadar ta ce kenan? To da alama ba Hajia ce ta turo ku ba kun zo ne ku min rashin kunya, to ba na da lokacin ku, idan kun gama ku rufe mana k'ofar."
Ai kuwa ya na gama fad'a ya koma in da ya fito ya bar su nan, kallon juna su ka yi Rabi'a tace "Kutumar bala'i, yanzu haka abin ya zama dama? Lallai."
Mik'ewa Hassana ta yi tace "To ai sai mu tafi ko? Tunda ba gidan uban mu bane."
Fita su ka yi su ka bar gidan ba yanda su ka iya, ko da su ka je gida nan fa aka bud'a sabon shafin hira akan abubuwan da ke faruwa, duk da haka kuma Aziza babu abin da tace dan ita dai kam kunya ma take ji, ana sallah magrib Usman ya dokowa Aziza kira wai ta zo gida ya na son ganin ta, gabanta ne ya dinga fad'uwa tunanin ta kar ace ya yi tunanin ita ta fad'a mu su wani abu, da k'yar ta kimtsa ta fito jiki na rawa ta zo bakin titi kuma ta kasa samun adaidaita da wuri, hakan ya sa ta sake b'ata lokaci kafin ta je, ta na zuwa gidan ran Usman ya gama b'aci saboda Haseenah ce ke neman ta amma ta b'ata lokaci, dan haka ta na shigowa falon saukar mari ne ya mata maraba, bai tsaya iya nan ba saida ya dinga masifa wai ta na can ta samu gulma ta bar aikin gida anan, Haseenah na zaune kan kukera ta kalle su tace "Kai ba ka yi mamakin zuwan su Hassana ba? Ai bayan fitarta ne su ka zo ma'ana ta fad'a mu su wani abu, suna can gidan ku sun baza tabarmar gulmata su na yi da ni, dan nasan dama babu mai so na kafatanin ahalin ka."
Ido ya rufe ya dinga zagin Aziza kamar ba ciki d'aya su ka fito ba, kafin daga bisani yace ta wuce ta gyarawa Haseenah d'akin ta, da "To." Ta amsa, ta na kallo ya kama hannun Haseenah suka nufi falon shi, ta na ganin haka ta shiga d'akin da take kwana ta gama had'a kayanta ta fito ta bar gidan, tunda ba za ta iya rama marin ta ba amma kuma in ba ta bar gidan ba tasan dole wata rana za ta jiwa Haseenah ciwo, dan haka ta bar gidan ba tare da sanin su ba ta koma gida.
Bayan sallah la'asar aka ce ana sallama da Khadija, da mamaki ta fita amma wa za ta gani sai Baba Garba mai gadi, da fara'a kamar za ta had'e shi ta mi shi izinin shiga ciki, har falon Mama ta saule shi in da Mama ke zaune ita ma, gaisawa su ka yi sosai kafin ya fara da "Hajiar yarima bayan barin ki gidan nan abubuwa da dama sun faru, tabbas mijin ki ba'a hayyacin shi ya ke ba, shiga baga ne kawai, amma insha Allahu komai ya k'are tunda har na je gida lafiya na dawo lafiya, kin gan shi nan abin da ya tsayar da ni." Ya fad'a ya na mik'o ma Khadija wani k'ullin magani k'arami, karb'a ta yi ta na kallo kafin ya d'ora da "Wannan maganin na karya sihiri ne, wani kaka na ne ya ke bayar da shi, maganin ya na da wuyar samu sosai, hakan ya sa ya ke da tsada ga wanda zai siya duk da dai ba ya da farashi, amma ke kyauta na karb'o mi ki shi saboda girman ki, Hajiar yarima wannan maganin da ki ka ji da ganin shi wallahi na rantse mi ki ko da bokan india mutum ke tink'aho to anfani da shi saiya karya komai, ba na da tamtama akan shi, tabbas na ke da, ki jaraba shi ki gani da yardar Allah za'a dace."
Ba tare da ta daina kallon shi ba tace "To amma ya ake anfani da shi?"
Da yatsa ya ke mata alama cewa "A buta za'a zuba maganin sai a saka ruwa ya yi wanka da shi, idan ya fito ya tsane jikinshi sai a samu garwashin wuta kuma a zuba maganin ciki a turara, ba dole sai ya shak'a ba ko yaje kusa da wutar, jikin shi ne kawai ake so hayak'in ya shafa lokacin da babu sutura a jikin shi, sai kuma wannan." Ya fad'a ya na sake mik'o mata wata ledar yace "Wanna kuma a tabbatar ya shak'a a hanci sau uku, insha Allahu idan ya shak'e shi zaiyi atshawa, to da izinin Allah duk wani bala'i dake kansa zai bar shi ko ba'a so."
"To ai ba kama bace, duk alamu sun nuna shegiyar yarinyar nan ita ce mai laifi, wallahi sai yanzu ne nake na tabbatar da tun farko *kallon kitse mu ka yi wa rogo*."
Nura da ke fitowa daga d'akin shi cikin sauri ne ya kalle su dukansu yace "Ku sai yanzu ma ku ka sani kenan? To mu zuba zuwa mu ga mu da ku waye zaiyi nasara, 'yan bayan Khadija ko 'yan bayan wannan mai kama da agwagwar."
Hajia ce tace "Abun bak'in cikin ma wallahi ta yanda gaba d'aya ta raba shi da mutane, d'an taimakon da muke san mu mi shi bamu ma gan shi ba bare mu taimaka d'in, amma ba dan haka ba da yanzu nasan komai ya wuce, kuma kinga shi malam ya ma bar maganar kamar baisan me ke faruwa ba."
Nura dai ficewa ya yi ya kama sabgar gaban shi sai Rabi'a da tace "Ai kuwa ba za mu yarda ba wallahi, ni zanje gidan na ga me ke faruwa, wallahi saina fad'a mata magana."
"Ai kuwa in ban cire ki a cikin dangin shi ba to tabbas zaki sha dukan tsiya." Cewar Aziza, da mamaki Rabi'a tace "Kamar ya duka? Ba shi da lafiya?"
Aziza ce tace "Lafiyar shi lau, amma babu mai tab'a ta ya yi shiru, akan haka fa ya kori Garba mai gadi."
Hajia ce tace "Ni kai na da zan ganshi da sai ran shi ya b'ace, tunda aka fara hidimar nan har yanzu banga k'eyar shi gidan nan ba, kuma ni har yanzu daga Nura har malam banji wanda yace ya bashi gudummuwar bikin nan ba, akwai abubuwa dayawa wanda da shi ne mu ka dogara, ba dan Allah ya rufa mana asiri ba yanzu yarinyar nan sun aiko da wannan gudummuwar ta su da ya za mu yi."
Hassana ce tace "Bai fa bayar da komai ba hajia?"
"Ni dai bai bani ba, kuma Nura da malam ba su fad'a min ba, kinga ko abune mai wuya ace sun kasa fad'a min."
Husseina ce tace "Ah ba ma ta yiwu ai, in har ya bayar dole sai ki sani Hajia."
"To me ya ke nufi? Ba zai bayar ba ko ta hana shi?" Cewar Rabi'a, Hajia ce tace "Gidan fa da za akai amarya ma Murtala ne ya bashi gidan, da ina jin har yanzu ba mu san ina za su zauna ba."
"Wallahi sai naje, sai dai ya kashe ni." Cewar Rabi'a cikin b'acin rai ta na mik'ewa ta yi kam ba b'ata lokaci ta saka hijabin ta, Hassana ce tace ita ma za ta je ta jira ta, Husseina dai cewa ta yi "Allah ya kad'e hau." Ko amsata ba su yi ba su ka tafi, cikin k'ank'anin lokaci su ka isa gidan, sunyi nasarar samun falon Haseenah bud'e, shiga su ka yi da sallama amma ba kowa sai telebijin ita kad'ai, zaune su ka yi sai Rabi'a da ke ci gaba da rumtuma sallama dan suji su fito.
*Alhamdulillah Ala ni'imatul islam.*
27/02/2020 à 13:42 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*33*
Tun su na sallama har su kai su ka yi shiru babu wanda ya amsa, suna magana k'asa kasa su ka ji an bud'a k'ofa, mayar da kallon su su ka yi ga mai fitowa, wa za su gani in ba Usman ba da doguwar riga kamar wanda ya taso daga bacci, da kallo su ka bishi har ya k'araso ya zauna ba su daina kallon shi ba, cikin wani cijewa yace "Ashe kune? Daga ina haka?"
Hassana ce tace "Ina wuni?" Bai amsa ba sai shafa kan shi da ya fara yi, Rabi'a ce tace "Dama Hajia ce tace mu zo mu ga ko kuna lafiya, daga kai har Hassenah ta jima ba ta gan ku ba."
Kamar wanda aka takura wajen maganar ya ke fad'in "Tsohin nan matsala ce da su wallahi, ko shekaran jiya fa na je gidan mun gaisa, lafiya k'alau na ke ni, ita ce ma dai ba ta jin dad'i, yau lafiya gobe ba lafiya."
Hassana ce tace "Shi ya sa har an fara shagulgulan bikin nan amma har yanzu babu wanda ya gan ta? Yah Fodio ka na ganin hakan ya yi daidai domin Allah, akwai fa abubu..."
"Ke dakata." Ya katse ta ya na mik'ewa tsaye, da yatsa ya nuna ta yace "Ke ma 'yar hassadar ta ce kenan? To da alama ba Hajia ce ta turo ku ba kun zo ne ku min rashin kunya, to ba na da lokacin ku, idan kun gama ku rufe mana k'ofar."
Ai kuwa ya na gama fad'a ya koma in da ya fito ya bar su nan, kallon juna su ka yi Rabi'a tace "Kutumar bala'i, yanzu haka abin ya zama dama? Lallai."
Mik'ewa Hassana ta yi tace "To ai sai mu tafi ko? Tunda ba gidan uban mu bane."
Fita su ka yi su ka bar gidan ba yanda su ka iya, ko da su ka je gida nan fa aka bud'a sabon shafin hira akan abubuwan da ke faruwa, duk da haka kuma Aziza babu abin da tace dan ita dai kam kunya ma take ji, ana sallah magrib Usman ya dokowa Aziza kira wai ta zo gida ya na son ganin ta, gabanta ne ya dinga fad'uwa tunanin ta kar ace ya yi tunanin ita ta fad'a mu su wani abu, da k'yar ta kimtsa ta fito jiki na rawa ta zo bakin titi kuma ta kasa samun adaidaita da wuri, hakan ya sa ta sake b'ata lokaci kafin ta je, ta na zuwa gidan ran Usman ya gama b'aci saboda Haseenah ce ke neman ta amma ta b'ata lokaci, dan haka ta na shigowa falon saukar mari ne ya mata maraba, bai tsaya iya nan ba saida ya dinga masifa wai ta na can ta samu gulma ta bar aikin gida anan, Haseenah na zaune kan kukera ta kalle su tace "Kai ba ka yi mamakin zuwan su Hassana ba? Ai bayan fitarta ne su ka zo ma'ana ta fad'a mu su wani abu, suna can gidan ku sun baza tabarmar gulmata su na yi da ni, dan nasan dama babu mai so na kafatanin ahalin ka."
Ido ya rufe ya dinga zagin Aziza kamar ba ciki d'aya su ka fito ba, kafin daga bisani yace ta wuce ta gyarawa Haseenah d'akin ta, da "To." Ta amsa, ta na kallo ya kama hannun Haseenah suka nufi falon shi, ta na ganin haka ta shiga d'akin da take kwana ta gama had'a kayanta ta fito ta bar gidan, tunda ba za ta iya rama marin ta ba amma kuma in ba ta bar gidan ba tasan dole wata rana za ta jiwa Haseenah ciwo, dan haka ta bar gidan ba tare da sanin su ba ta koma gida.
Bayan sallah la'asar aka ce ana sallama da Khadija, da mamaki ta fita amma wa za ta gani sai Baba Garba mai gadi, da fara'a kamar za ta had'e shi ta mi shi izinin shiga ciki, har falon Mama ta saule shi in da Mama ke zaune ita ma, gaisawa su ka yi sosai kafin ya fara da "Hajiar yarima bayan barin ki gidan nan abubuwa da dama sun faru, tabbas mijin ki ba'a hayyacin shi ya ke ba, shiga baga ne kawai, amma insha Allahu komai ya k'are tunda har na je gida lafiya na dawo lafiya, kin gan shi nan abin da ya tsayar da ni." Ya fad'a ya na mik'o ma Khadija wani k'ullin magani k'arami, karb'a ta yi ta na kallo kafin ya d'ora da "Wannan maganin na karya sihiri ne, wani kaka na ne ya ke bayar da shi, maganin ya na da wuyar samu sosai, hakan ya sa ya ke da tsada ga wanda zai siya duk da dai ba ya da farashi, amma ke kyauta na karb'o mi ki shi saboda girman ki, Hajiar yarima wannan maganin da ki ka ji da ganin shi wallahi na rantse mi ki ko da bokan india mutum ke tink'aho to anfani da shi saiya karya komai, ba na da tamtama akan shi, tabbas na ke da, ki jaraba shi ki gani da yardar Allah za'a dace."
Ba tare da ta daina kallon shi ba tace "To amma ya ake anfani da shi?"
Da yatsa ya ke mata alama cewa "A buta za'a zuba maganin sai a saka ruwa ya yi wanka da shi, idan ya fito ya tsane jikinshi sai a samu garwashin wuta kuma a zuba maganin ciki a turara, ba dole sai ya shak'a ba ko yaje kusa da wutar, jikin shi ne kawai ake so hayak'in ya shafa lokacin da babu sutura a jikin shi, sai kuma wannan." Ya fad'a ya na sake mik'o mata wata ledar yace "Wanna kuma a tabbatar ya shak'a a hanci sau uku, insha Allahu idan ya shak'e shi zaiyi atshawa, to da izinin Allah duk wani bala'i dake kansa zai bar shi ko ba'a so."