Sashe 6
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ba na da wani zab'i da ya wuce na ka, duk abin da ran ka ya ke so shine nawa ya ke so."
"To in hakane sai ki tambayi yarima dan ya raba mana wannan gardamar kamar yanda ya saba."
Cikin shagwab'a tace "Shi ma kan shi yarima zab'in mu shine na shi, dan haka a matsayin ka na shugaba kuma ja gaba dan Allah ka taimaka ka zab'a mana abin da za mu ci."
Hannu ya kai ya ja dogon hancin ta ya na fad'in "Kin ganki ko mai wayo, to shikenan yanzu ki je ki samar mana ko da irin wannan wainar da ki ke had'a ta da miyar kayan ciki."
Dariya ta yi tace "Kwad'ai ko? Wato ka ji dad'in ta?"
Kamo hannun ta ya yi ya sumbata yace "Duk abin da hannun nan zai tab'a to ya kan zama mafi soyuwa a gare ni."
"Shikenan to bara na je na fara aikin, tunda har yanzu *Uwani* ba ta dawo ba bare na tsaya jan jiki."
Rik'o ta ya yi yace "Amma dai ban takura ki ba ko?"
Sai da ta waina idon ta tace "Gaskiya na d'an takura da ka k'i fad'a min abin da ka ke so tun da wuri."
Dariya ya yi ita kuma ta mik'e ta juya, tafin hannun shi ya sa ya daki mazaunan ta, da sauri ta dafe ta juyo ta na kallon shi, far-far ta masa da ido ta juya ta sake juya masa mazaunan da kyau kafin ta fice, tashi ya yi ya haura kan gado ya yi ruf cikin bargo, ita kuma aiki ta fara gadan-gadan.
*A GURGUJE*
Lokaci ya zo na biki, ta kowane b'angare shiri ake yi, yayyun Khadija da mahaifiyar ta sun sake mata kayan d'aki na gani na fad'a, kaya ne yan uban-ubansu, hatta teburin cin abinci sai da Khadija ta cika kud'i aka bata sabo da ya dace da kayan ta, daga falon ta zuwa uwar d'akin ta idan ka shiga sai ka ji kamar ka fito da mai d'akin kai ka zauna, Usman ma kai da kawowa kawai ya ke, tun yanzu Khadija da Bilal su na ganin sauyi a tare da shi na rashin cikakken lokacin shi, amma ta had'e dan ta san na d'an lokaci insha Allah, amarya ma an shafa an goge anyi jawur, ga bala'in magunguna da take ta kaurawa kan ta, Mariya ma taje wajen malam an basu taimako wanda zai sa Usman ya so ta fiye da kowa, hakan yasa dole ta had'a garin maganin da aka bata ta kwab'a lalle da shi ta shafa a k'afar ta kamar yanda aka ce, sai kuma wanda za ta dinga zuba mi shi a abinci ya na ci, sau d'aya ta yi nasarar saka mi shi kuma ya ci lokacin da ya zo gidan su, shi ma sai da ta fara kukan kissa kad'ai ya ci, dan ya fad'a mata shi wallahi bai saba cin abinci a waje ba ko da kuwa gidan su ya je, da k'yar dai ya ci shi ya sa ma ta aje da tunani har ta shiga gidan, da haka har aka fara da shagalin kamu, washe gari kuma d'aurin aure, a ranar in banda dakan uku-uku babu abin da k'irjin Khadija ke yi, amma cikin k'arfin hali haka ta had'e kishin ta ta taimaka mi shi ya shirya cikin manyan kayan shi irin na Bilal komai da komai har takalma da hula iri d'aya suka saka, ta na kallo ya kama hannun Bilal suka fice sai k'amshi suke, su na fita ta zube kan kujera ta fashe da kuka da iya k'arfin ta dan ta rage rad'ad'i, cikin sa'a sai ga Kaltume ta zo tun da wuri, nan fa ta shiga aikin rarrashi da ba ta hak'uri tare da fad'a mata ta taushi zuciyar ta sannan ta dinga anbaton sunan ubangiji, da haka ta samu ta saisaita nutsuwar ta su ka fara hira, angama d'aurin aure kuma wasu k'awayen nata suka dinga zuwa wanda tafi kusa da su, tare suka shigo da Bilal su ka canza kaya wata shaddar iri d'aya, k'awayen Khadija kam bayan gaisuwa murna su ka taya shi tare da mi shi addu'a ta alkairi, rana ta farko a *tarihin* rayuwar su da Usman ya shiga d'aki Khadija ta kasa bin bayan shi, bayan rasa kuzari da ya yi sai ya kasa shirya kansa, domin kuwa Khadija ta saba mishi da shirya shi ko ta taimaka masa, hakan ne yasa ko mab'allin riga bai b'alla ba ya fito, kasancewar Kaltume su na wasa ta dinga masa dariya wai zumud'i yasa ya kasa b'alla mab'alli, Khadija kam da ta san komai tashi ta yi ba tare da ta yarda sun had'a ido ba ta b'alla mi shi, juyawa ta yi za ta wuce ya rik'e hannun ta sam ya manta da mutanen da ke wajen, juyowa ta yi amma ba ta kalle shi ba, dan haka yace "Sai yanzu ne na fahimci k'arfin wuta da tartsatsin da ke cikin idon ki, ki kalle ni ko sau d'aya mana, hakan ne zai sa na kasance cikin karsashi da kuzari."
Kasa tausar zuciyar ta tayi har sai da tace "...
*Allah ka nufe mu da sassauk'an kishi mai tsafta da kyawu, Allah kasa mufi k'arfin zuk'atan mu.*
01/01/2020 à 12:14 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*6*
"Hum! Ai yanzu ba ni kad'ai ba ce hakk'in saka ka farin ciki ke kai na, ka je ka samo farin cikin ka a wani wurin, ni ina da abin yi a gaba na da yafi wannan mahimmanci."
Ta na fad'a ta juya ta koma in da ta ke, sam bai ji dad'i har zuciyar shi,sai dai baiga laifin ta ba in ya yi la'akari da yanda kishi ya ke, fita ya yi shi ma zuciya ba dad'i, rana ta yi k'awayen Khadija sun zage sai girki ake ana hira, sam abin da Khadija ba ta yi tsammanin shi bane ya faru, ganin ba kowa ta gayyata ba amma sai ga mutane na ta b'ullowa daga wurare daban-daban, sai dai da gani kasan wani ya zo ya ga me zai faru ne, daga ciki kuma har da dangin Usman wanda sun san ba biki take ba, amma sai ga shi suna zuwa su na yak'e mata bakuna, ita kam da ta fisu sai ta nuna farin ciki take sosai da hakan, musamman da Aziza ta zo tare da Hassana da yan biyun ta Husseina su ma sun zo gidan, kowa da abin da ke ran shi, haka dai aka yage hak'ora kowa ya bar wajen.
A k'alla k'awayen ta kusan goma sha biyar ne su ka jira har a kawo amarya, masha Allah, ba k'aramin shiri Khadija ta yi ba, shaddar da ke jikin ta da aikin da aka ma shaddar kad'ai zai nuna maka an kashe dala sosai, dogayen takalma da kwalliyar da aka watsa mata, gilashin ta da ya k'ara mata kyau da gani, d'aurin d'an kwalin da sai kace tafiye ya ke daga k'asar waje, dare ya yi kuma an kawo amarya, tun da Khadija ta ji ayiriyiri gaban ta ya fara wani sabon dukan, haka dai aka yi duk wani abu da aka san ana yi, an kawo amarya d'akin uwar gidan an gaisa an kuma mu su nasiha, sun saka ango tsaka an sake mu su nasiha tare da hotuna, in dai har za'a fad'i gaskiya to Haseenah ba ta ko kama k'afar Khadija ba, ta kowane b'angare ma dan babu had'i tsakanin su ma, su kan su danginta da k'awayen ta sun girgiza da ganin ta a haka, sai dai kowa ya san Usman ya yi dacen mata, ganin shi d'in ba wani kyakyawa ba, shi ba hasken fata ba, haka dai aka watse aka bar su kowa ya koma d'akin shi, dan dama babban falo shine na Usman, k'ofa ya yi ta yanda kowace za ta iya shigowa daga falon ta zuwa na shi.
An tafi mayar da mutane aka bar amarya da k'awayen ta kafin a zo a d'auke su, nan fa hira ta b'arke tsakanin su, Zeinab ce ta fara da "Wallahi rabin rai sai kin zage damtse, kinga wannan matar ta shi, ni fa har ta ban tsoro."
*Farida* ce tace "Bari kedai, ashe haka ta ke?"
Murmushi Haseenah ta yi tace " Lallai *kallon kitse ku ke wa rogo*, ni kuma ko kad'an ba ta ban tsoro ba, dan na riga da na san komai."
Zeinab ce tace "Kamar me fa? Dama ku na hirar ta da shi?"
"A'a, amma dai akwai wasu abubuwa da su ka nuna min ita d'in shashasha ce."
"Ban gane ba k'awata, ki min gwari-gwari mana."
Cikin nutsuwa tace "Na fahimci mijin ta na son girmamawa, ya na son a dinga ma sa kalaman soyayya, dan in mu na hira da shi sai mu kai k'arfe *11:00* na dare mu na waya, duk kalmar da na fad'a mi shi sai ya gode min tare da godewa Allah da ya sa zai aure ni, shi ya sa na san cewa ita ba ya samun nutsuwa a tare da ita, kyan d'an maciji ne kawai da ita, kuma wallahi na d'aura d'amarar faranta mi shi fiye da ita."
Ajiyar zuciya Zeinab ta sauke sai wata daga ciki mai sunan *Jamila* ce tace "To k'awata, Allah ya sa dai ba *kallon kitse ki ke wa rogo ba*, dan wasu mazan ba kya iya gane cikin su, watak'ila ma shi d'in mai son kulawa ne kawai, shi ya sa ya ke jin dad'i kema za ki bashi farin ciki."
Kallon ta Haseenah ta yi yi tace "Hum! Ba ko d'aya wallahi."
"To in hakane sai ki tambayi yarima dan ya raba mana wannan gardamar kamar yanda ya saba."
Cikin shagwab'a tace "Shi ma kan shi yarima zab'in mu shine na shi, dan haka a matsayin ka na shugaba kuma ja gaba dan Allah ka taimaka ka zab'a mana abin da za mu ci."
Hannu ya kai ya ja dogon hancin ta ya na fad'in "Kin ganki ko mai wayo, to shikenan yanzu ki je ki samar mana ko da irin wannan wainar da ki ke had'a ta da miyar kayan ciki."
Dariya ta yi tace "Kwad'ai ko? Wato ka ji dad'in ta?"
Kamo hannun ta ya yi ya sumbata yace "Duk abin da hannun nan zai tab'a to ya kan zama mafi soyuwa a gare ni."
"Shikenan to bara na je na fara aikin, tunda har yanzu *Uwani* ba ta dawo ba bare na tsaya jan jiki."
Rik'o ta ya yi yace "Amma dai ban takura ki ba ko?"
Sai da ta waina idon ta tace "Gaskiya na d'an takura da ka k'i fad'a min abin da ka ke so tun da wuri."
Dariya ya yi ita kuma ta mik'e ta juya, tafin hannun shi ya sa ya daki mazaunan ta, da sauri ta dafe ta juyo ta na kallon shi, far-far ta masa da ido ta juya ta sake juya masa mazaunan da kyau kafin ta fice, tashi ya yi ya haura kan gado ya yi ruf cikin bargo, ita kuma aiki ta fara gadan-gadan.
*A GURGUJE*
Lokaci ya zo na biki, ta kowane b'angare shiri ake yi, yayyun Khadija da mahaifiyar ta sun sake mata kayan d'aki na gani na fad'a, kaya ne yan uban-ubansu, hatta teburin cin abinci sai da Khadija ta cika kud'i aka bata sabo da ya dace da kayan ta, daga falon ta zuwa uwar d'akin ta idan ka shiga sai ka ji kamar ka fito da mai d'akin kai ka zauna, Usman ma kai da kawowa kawai ya ke, tun yanzu Khadija da Bilal su na ganin sauyi a tare da shi na rashin cikakken lokacin shi, amma ta had'e dan ta san na d'an lokaci insha Allah, amarya ma an shafa an goge anyi jawur, ga bala'in magunguna da take ta kaurawa kan ta, Mariya ma taje wajen malam an basu taimako wanda zai sa Usman ya so ta fiye da kowa, hakan yasa dole ta had'a garin maganin da aka bata ta kwab'a lalle da shi ta shafa a k'afar ta kamar yanda aka ce, sai kuma wanda za ta dinga zuba mi shi a abinci ya na ci, sau d'aya ta yi nasarar saka mi shi kuma ya ci lokacin da ya zo gidan su, shi ma sai da ta fara kukan kissa kad'ai ya ci, dan ya fad'a mata shi wallahi bai saba cin abinci a waje ba ko da kuwa gidan su ya je, da k'yar dai ya ci shi ya sa ma ta aje da tunani har ta shiga gidan, da haka har aka fara da shagalin kamu, washe gari kuma d'aurin aure, a ranar in banda dakan uku-uku babu abin da k'irjin Khadija ke yi, amma cikin k'arfin hali haka ta had'e kishin ta ta taimaka mi shi ya shirya cikin manyan kayan shi irin na Bilal komai da komai har takalma da hula iri d'aya suka saka, ta na kallo ya kama hannun Bilal suka fice sai k'amshi suke, su na fita ta zube kan kujera ta fashe da kuka da iya k'arfin ta dan ta rage rad'ad'i, cikin sa'a sai ga Kaltume ta zo tun da wuri, nan fa ta shiga aikin rarrashi da ba ta hak'uri tare da fad'a mata ta taushi zuciyar ta sannan ta dinga anbaton sunan ubangiji, da haka ta samu ta saisaita nutsuwar ta su ka fara hira, angama d'aurin aure kuma wasu k'awayen nata suka dinga zuwa wanda tafi kusa da su, tare suka shigo da Bilal su ka canza kaya wata shaddar iri d'aya, k'awayen Khadija kam bayan gaisuwa murna su ka taya shi tare da mi shi addu'a ta alkairi, rana ta farko a *tarihin* rayuwar su da Usman ya shiga d'aki Khadija ta kasa bin bayan shi, bayan rasa kuzari da ya yi sai ya kasa shirya kansa, domin kuwa Khadija ta saba mishi da shirya shi ko ta taimaka masa, hakan ne yasa ko mab'allin riga bai b'alla ba ya fito, kasancewar Kaltume su na wasa ta dinga masa dariya wai zumud'i yasa ya kasa b'alla mab'alli, Khadija kam da ta san komai tashi ta yi ba tare da ta yarda sun had'a ido ba ta b'alla mi shi, juyawa ta yi za ta wuce ya rik'e hannun ta sam ya manta da mutanen da ke wajen, juyowa ta yi amma ba ta kalle shi ba, dan haka yace "Sai yanzu ne na fahimci k'arfin wuta da tartsatsin da ke cikin idon ki, ki kalle ni ko sau d'aya mana, hakan ne zai sa na kasance cikin karsashi da kuzari."
Kasa tausar zuciyar ta tayi har sai da tace "...
*Allah ka nufe mu da sassauk'an kishi mai tsafta da kyawu, Allah kasa mufi k'arfin zuk'atan mu.*
01/01/2020 à 12:14 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*6*
"Hum! Ai yanzu ba ni kad'ai ba ce hakk'in saka ka farin ciki ke kai na, ka je ka samo farin cikin ka a wani wurin, ni ina da abin yi a gaba na da yafi wannan mahimmanci."
Ta na fad'a ta juya ta koma in da ta ke, sam bai ji dad'i har zuciyar shi,sai dai baiga laifin ta ba in ya yi la'akari da yanda kishi ya ke, fita ya yi shi ma zuciya ba dad'i, rana ta yi k'awayen Khadija sun zage sai girki ake ana hira, sam abin da Khadija ba ta yi tsammanin shi bane ya faru, ganin ba kowa ta gayyata ba amma sai ga mutane na ta b'ullowa daga wurare daban-daban, sai dai da gani kasan wani ya zo ya ga me zai faru ne, daga ciki kuma har da dangin Usman wanda sun san ba biki take ba, amma sai ga shi suna zuwa su na yak'e mata bakuna, ita kam da ta fisu sai ta nuna farin ciki take sosai da hakan, musamman da Aziza ta zo tare da Hassana da yan biyun ta Husseina su ma sun zo gidan, kowa da abin da ke ran shi, haka dai aka yage hak'ora kowa ya bar wajen.
A k'alla k'awayen ta kusan goma sha biyar ne su ka jira har a kawo amarya, masha Allah, ba k'aramin shiri Khadija ta yi ba, shaddar da ke jikin ta da aikin da aka ma shaddar kad'ai zai nuna maka an kashe dala sosai, dogayen takalma da kwalliyar da aka watsa mata, gilashin ta da ya k'ara mata kyau da gani, d'aurin d'an kwalin da sai kace tafiye ya ke daga k'asar waje, dare ya yi kuma an kawo amarya, tun da Khadija ta ji ayiriyiri gaban ta ya fara wani sabon dukan, haka dai aka yi duk wani abu da aka san ana yi, an kawo amarya d'akin uwar gidan an gaisa an kuma mu su nasiha, sun saka ango tsaka an sake mu su nasiha tare da hotuna, in dai har za'a fad'i gaskiya to Haseenah ba ta ko kama k'afar Khadija ba, ta kowane b'angare ma dan babu had'i tsakanin su ma, su kan su danginta da k'awayen ta sun girgiza da ganin ta a haka, sai dai kowa ya san Usman ya yi dacen mata, ganin shi d'in ba wani kyakyawa ba, shi ba hasken fata ba, haka dai aka watse aka bar su kowa ya koma d'akin shi, dan dama babban falo shine na Usman, k'ofa ya yi ta yanda kowace za ta iya shigowa daga falon ta zuwa na shi.
An tafi mayar da mutane aka bar amarya da k'awayen ta kafin a zo a d'auke su, nan fa hira ta b'arke tsakanin su, Zeinab ce ta fara da "Wallahi rabin rai sai kin zage damtse, kinga wannan matar ta shi, ni fa har ta ban tsoro."
*Farida* ce tace "Bari kedai, ashe haka ta ke?"
Murmushi Haseenah ta yi tace " Lallai *kallon kitse ku ke wa rogo*, ni kuma ko kad'an ba ta ban tsoro ba, dan na riga da na san komai."
Zeinab ce tace "Kamar me fa? Dama ku na hirar ta da shi?"
"A'a, amma dai akwai wasu abubuwa da su ka nuna min ita d'in shashasha ce."
"Ban gane ba k'awata, ki min gwari-gwari mana."
Cikin nutsuwa tace "Na fahimci mijin ta na son girmamawa, ya na son a dinga ma sa kalaman soyayya, dan in mu na hira da shi sai mu kai k'arfe *11:00* na dare mu na waya, duk kalmar da na fad'a mi shi sai ya gode min tare da godewa Allah da ya sa zai aure ni, shi ya sa na san cewa ita ba ya samun nutsuwa a tare da ita, kyan d'an maciji ne kawai da ita, kuma wallahi na d'aura d'amarar faranta mi shi fiye da ita."
Ajiyar zuciya Zeinab ta sauke sai wata daga ciki mai sunan *Jamila* ce tace "To k'awata, Allah ya sa dai ba *kallon kitse ki ke wa rogo ba*, dan wasu mazan ba kya iya gane cikin su, watak'ila ma shi d'in mai son kulawa ne kawai, shi ya sa ya ke jin dad'i kema za ki bashi farin ciki."
Kallon ta Haseenah ta yi yi tace "Hum! Ba ko d'aya wallahi."