Sashe 79
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da murmushi tace "Insha Allahu Mama zanyi, nima dama na so tun farko na yi hakan, amma yanzu kin k'ara k'arfafa min gwiwa, tunda ko ba komai sun ruga da sun zama d'aya shi da ita tunda ta na d'auke da cikin shi, rabuwar kuma ba dad'i musamman ita da k'ananan shekaru."
"Gaskiya kam, dan hakan zai iya zama tozarci gare ta da b'ata mata suna."
Cikin nutsuwa Khadija tace "Mama ba lallai ma a kalle ta da laifi ba, ni ba zan fita daga zargi ba tunda dama ana ganin na mallake shi, kinga yanzu za'a ce ni ce na fitar da ita daga gidan, babu wanda zai tuna lokacin da ni na d'auka a na mu gidan gaban iyaye na, nata ne yanzu zai fito fili kowa ya ji."
Cike da gamsuwa mama tace "Gaskiya ne kam, dan ko ansan kin zauna a gidan ma za'a d'auka kishin ki ne ya tura ki gidan, mutum, mutum ai sai Allah."
Murmushi Khadija ta yi tace " *Mutum mugun ice, ya mutu ma fa sai an d'aure shi Mama.*"Dariya Mama ta yi kafin suka ci gaba da tattaunawa.
Washe gari da safe ma daga Haseenah sai maman ta a gidan duk kowa ya tafi harkar gaban shi, rana ta fito sosai Mariya ta shigo d'auke da kaya da alaman sabuwar d'auka ce ta yi, gaisawa su ka yi sosai har ta fara hira da maman ta akan kasuwancin na ta, sun jima nan kafin maman su ta tashi ta shiga d'akin su dan yin wani abun, Haseenah na ganin haka tace "Aunty Mariya, muje d'aki ina son magana da ke."
Cikin rad'a tace "To lafiya dai ko?" Saida ta mik'e ta nufi d'akin tace "Ki zo kiji ke dai."
Mik'ewa ta yi ta na fad'in "To na ji alkairi." Suna shiga bakin katifa suka zauna Haseenah ta tsareta da ido tace "Aunty Mariya, na d'auka abin da ya faru da ni za ki taimaka min wajen ganin na koma gidan Usman, amma ke ko a jikin ki ma sai harkokin gaban ki kike."
Cewar Mariya "To me zanyi in ba harkokin gabana ba, sannan wane irin taimako ki ke buk'ata daga gare ni yanzun?"
A daidai lokacin da Haseenah za ta yi magana a lokacin mahaifiyar su ta fito daga nata d'akin, za ta wuce ne taji Haseenah tace "Ki yi wani abu mana na koma gidan shi, Ko so ki ke na haihu gida?"
Kallonta Mariya ta yi tace "Na yi me? Me ki ke nufi? Wai na sake komawa wajen malam? Sam wallahi ba da ni ba, ai na fad'a mi ki tun ranar Haseenah gaskiya ba zan iya binki mu tsunduma kogin da ki ke neman jefa mu a ciki ba, idan na yi haka to fa nan gaba ba naki auren bane zai mutu har da nawa."
Wani kallo Haseenah ke mata amma ba tace komai ba, d'orawa ta yi da "Kinga k'anwa ta, ki yi hak'uri da abin da ya sameki ki rugumi k'addara, sakin aure ba'a kan ki aka fara ba bare ya k'are kan ki, yanzu idan mu ka ce zamu matsanta sosai to wallahi abubuwa ba za su yi kyau ba, dan ko da an sake juyar mi shi da tunani ya dawo kan ki wallahi ranar da ya sake dawowa hankalin shi a karo na biyu to fa zai sake koroki ne, dan haka abin da yafi kawai ki tuba ga Allah tare da rainon cikin ki har ki haihu, domin Allah fa kin cutar da su sosai, kin raba shi da matar shi, kinsa dangi suna mata kallon marar imani kuma mai laifi, alhalin kuma ke ce mai laifin, ke ba ma dangin shi ba kad'ai har dangin har yanzu suna kallon Khadija a matsayin wacce tasa aka sake ki, alhalin kuma duka mutane *kallon kitse su ke wa rogo*, ke da ake gani ba ruwanki ke ce kuma gubar."
Cikin jin haushi Haseenah tace "Ni ce ma gubar? To idan ni guba ce ke kuma fa? Ai ke ce babbar guba tunda ke ki ka haddasa komai, ina zamana lafiya ban tab'a tunanin wacece matar shi ba, amma ke ki ka zo min da labarin cewa matar shi yar duniya ce ta mallake shi, sannan waya kai ni wajen malam in ba ke ba, wa yake zuwa har gida na ya na karb'o kud'in da ake kaiwa malam d'in? Ai ke ce da kan ki, amma shine yanzu za ki kira ni da guba, to ke ce babbar guba ba ni ba wallahi."
Tab'e baki Mariya ta yi a ran ta tace "Sakarya kawai." A fili kuma cewa ta yi "Wannan kuma ke ta shafa, ni kinga tafiya ta sai anjima." Ta na fad'a ta mik'e za ta fita sai ga mahaifiyar su ta shigo d'akin dan kaf babu abin da bata ji ba, baya ta rumgume hannaye ta na kallonsu cike da haushi kafin tace "Abin da ku ka aikata kenan? Mariya, Haseenah, wannan ita ce tarbiyyar da mu ka baku a gidan nan? Wannan wane irin zubar da mutumci ne? Kenan mutuwar auren ki ba ya da nasaba da kishiyar ki? Haka kawai kinsa muna kallon ta a matsayin mai laifi, to rashin lafiyar da muke tunanin ki na fama da ita fa har da nemo mi ki magani? Ko dai duk k'arya ce ki ke? Dan babu yanda za ayi mata biyu a gidan miji d'aya su zama mushrikai."
Sosa kai Haseenah take cikin rashin abin fad'a sai tsohuwar ce ta k'ara da "Ko ba ki fad'a ba ya nuna ba ki da gaskiya, amma Haseenah taya ki ka iya shirya makirci irin haka? Ko ni da na haife ki ba zanyi abin da ki kai ba."
Kallon Mariya ta yi sama da k'asa tace "Babbar banza, yanzu idan akwai wanda ya kashe mata aure ai bayanki ya ke."
K'asa ta yi da kanta sosai hakan ya sa tsohuwar juyawa ta fita ta barsu, cikin sanyin jiki Mariya ta fita sai Haseenah da ta fashe da kuka, *Asiya* kuma d'akin ta ta koma ta shirya saida ta fito za ta fita ta lek'a d'akin Haseenah tace "Zan fita yanzu, babu kowa a gidan ki fito ki d'ora girkin rana kafin yaran nan su dawo, daga yau kin bar kwanciya a d'aki da sunan wai ki na da ciki a tausaya mi ki, girki da wanke-wanke ya zama na ki."
Ta na fad'a ta fice abin da har zuwa bakin ti-ti ta samu adaidaita ta hau, kai tsaye gidan Khadija ta isa, duk da ba sosai Khadija tasan ba amma dai ta gane ta, sosai ta tarbe ta kamar za ta had'e ta cikin girmamawa, dama kuma in dai ta wannan fannin ne Khadija gwana ce, hakan ya sa ma take da farin jinin al'uma, har d'akin Bilal ta rakata taga jikin shi kafin su ka dawo falo ta zauna, cike da dattako tsohuwar ta kalli Khadija tace " 'Yata Khadija, na zo ne ganin jikin yaron ki da sai jiya na ke jin bai da lafiya, sai kuma abu na biyu na zo na baki hak'uri akan abin da ya faru, 'yar nan wallahi ba mu tab'a tunanin Haseenah za ta iya cutar da wani ba, amma sai yau kuma yanzu na ke jin irin ta'asar da su ka yi ita da 'yar uwar ta daga bakin su, hak'ik'a yau Allah ya wanke ki daga zargin da mu ke mi ki, muna kallon ki a matsayin wacce take hana 'yar mu zaman gidan aure, ashe ba haka bane komai makircin su ne, ashe har zuwa gidan da take ta nuna bata lafiya ba ta son zaman gidan duk k'arya ne, kawai d'ora mi ki laifi ne suke son yi, dan Allah ki yi hak'uri ki yafe mana kinji 'yar albarka."
Khadija da ta yi jim ta na jinjina al'amarin Haseenah, sai yanzu ne take sanin wannan labarin na rashin lafiya, kenan ita ake kallo da wannan laifin ma, murmushi ta yi ta rik'o hannun Asiya tace "Mama, ke fa uwar ce a gare ni, yanda Mama na bata neman gafara na akan duk abin da za ta min to haka ke ma, wallahi na yafe mu ku dukan ku, ni dama ban tab'a rik'e kowa a zuciya ta ba saboda ina so nima Allah ya kalle ni da idon rahama, dan haka ku kwantar da hankalin ku yanzu mun zama d'aya ni da ku, kuma ita rayuwa dama haka take, wanda wautar shi ta fito fili shi ake kamawa da laifi, wanda kuma ya iya takon shi to ko shine mai laifin sai kaga babu mai gani bare ayi magana, kuma ita dama ance *fahimta fuska* ce."
"Hakane kam, Allah ya mi ki albarka, Allah ya sa ki gama da duniya lafiya, Allah ya kare ki daga sharrin abokan zama irin su Haseenah." Sakin hannun ta Khadija ta yi ta mik'e tace "Ni zan tafi, dama ko mahaifinsu bai san na zo ba."
D'aki Khadija ta shiga ta tarkato kaya sabulu da turaruka da turmin atamfa mai kyau, sannan ta had'o da wani k'aton mayafi da ita bai birge ta ba tunda mama ta siyo mata shi daga Dubai, haka ta had'a tsohuwar nan da su ta rakata har k'ofar gida, Rabe da ke zaune tace ya d'aukar mata kayan har saida ta samu adaidaita, Asiya kam a adaidaita har kuka ta yi ganin irin alherin da Khadija ta yi mata, ta na komawa gida ta samu mahaifinsu ya dawo zaune a tsakar gidan, tun bata gama shigowa ba yace "Daga ina ki ke Asiya?"
Kai tsaye tace "Daga gidan Usman."
Da sauri ya kalle ta haka ma Haseenah da ke bakin murhu ta na girki duk ta yi gumi, cikin hushi yace "Yanzu da na ce kar ki jr shine ki ka wanke k'afa ki ka tafi ba da izini na ba? Asiya yaushe ki ka fara yin watsi da maganata? Akan matar da ta kashe ma yar ki aure ne za ki wulak'anta ni haka?"
"Gaskiya kam, dan hakan zai iya zama tozarci gare ta da b'ata mata suna."
Cikin nutsuwa Khadija tace "Mama ba lallai ma a kalle ta da laifi ba, ni ba zan fita daga zargi ba tunda dama ana ganin na mallake shi, kinga yanzu za'a ce ni ce na fitar da ita daga gidan, babu wanda zai tuna lokacin da ni na d'auka a na mu gidan gaban iyaye na, nata ne yanzu zai fito fili kowa ya ji."
Cike da gamsuwa mama tace "Gaskiya ne kam, dan ko ansan kin zauna a gidan ma za'a d'auka kishin ki ne ya tura ki gidan, mutum, mutum ai sai Allah."
Murmushi Khadija ta yi tace " *Mutum mugun ice, ya mutu ma fa sai an d'aure shi Mama.*"Dariya Mama ta yi kafin suka ci gaba da tattaunawa.
Washe gari da safe ma daga Haseenah sai maman ta a gidan duk kowa ya tafi harkar gaban shi, rana ta fito sosai Mariya ta shigo d'auke da kaya da alaman sabuwar d'auka ce ta yi, gaisawa su ka yi sosai har ta fara hira da maman ta akan kasuwancin na ta, sun jima nan kafin maman su ta tashi ta shiga d'akin su dan yin wani abun, Haseenah na ganin haka tace "Aunty Mariya, muje d'aki ina son magana da ke."
Cikin rad'a tace "To lafiya dai ko?" Saida ta mik'e ta nufi d'akin tace "Ki zo kiji ke dai."
Mik'ewa ta yi ta na fad'in "To na ji alkairi." Suna shiga bakin katifa suka zauna Haseenah ta tsareta da ido tace "Aunty Mariya, na d'auka abin da ya faru da ni za ki taimaka min wajen ganin na koma gidan Usman, amma ke ko a jikin ki ma sai harkokin gaban ki kike."
Cewar Mariya "To me zanyi in ba harkokin gabana ba, sannan wane irin taimako ki ke buk'ata daga gare ni yanzun?"
A daidai lokacin da Haseenah za ta yi magana a lokacin mahaifiyar su ta fito daga nata d'akin, za ta wuce ne taji Haseenah tace "Ki yi wani abu mana na koma gidan shi, Ko so ki ke na haihu gida?"
Kallonta Mariya ta yi tace "Na yi me? Me ki ke nufi? Wai na sake komawa wajen malam? Sam wallahi ba da ni ba, ai na fad'a mi ki tun ranar Haseenah gaskiya ba zan iya binki mu tsunduma kogin da ki ke neman jefa mu a ciki ba, idan na yi haka to fa nan gaba ba naki auren bane zai mutu har da nawa."
Wani kallo Haseenah ke mata amma ba tace komai ba, d'orawa ta yi da "Kinga k'anwa ta, ki yi hak'uri da abin da ya sameki ki rugumi k'addara, sakin aure ba'a kan ki aka fara ba bare ya k'are kan ki, yanzu idan mu ka ce zamu matsanta sosai to wallahi abubuwa ba za su yi kyau ba, dan ko da an sake juyar mi shi da tunani ya dawo kan ki wallahi ranar da ya sake dawowa hankalin shi a karo na biyu to fa zai sake koroki ne, dan haka abin da yafi kawai ki tuba ga Allah tare da rainon cikin ki har ki haihu, domin Allah fa kin cutar da su sosai, kin raba shi da matar shi, kinsa dangi suna mata kallon marar imani kuma mai laifi, alhalin kuma ke ce mai laifin, ke ba ma dangin shi ba kad'ai har dangin har yanzu suna kallon Khadija a matsayin wacce tasa aka sake ki, alhalin kuma duka mutane *kallon kitse su ke wa rogo*, ke da ake gani ba ruwanki ke ce kuma gubar."
Cikin jin haushi Haseenah tace "Ni ce ma gubar? To idan ni guba ce ke kuma fa? Ai ke ce babbar guba tunda ke ki ka haddasa komai, ina zamana lafiya ban tab'a tunanin wacece matar shi ba, amma ke ki ka zo min da labarin cewa matar shi yar duniya ce ta mallake shi, sannan waya kai ni wajen malam in ba ke ba, wa yake zuwa har gida na ya na karb'o kud'in da ake kaiwa malam d'in? Ai ke ce da kan ki, amma shine yanzu za ki kira ni da guba, to ke ce babbar guba ba ni ba wallahi."
Tab'e baki Mariya ta yi a ran ta tace "Sakarya kawai." A fili kuma cewa ta yi "Wannan kuma ke ta shafa, ni kinga tafiya ta sai anjima." Ta na fad'a ta mik'e za ta fita sai ga mahaifiyar su ta shigo d'akin dan kaf babu abin da bata ji ba, baya ta rumgume hannaye ta na kallonsu cike da haushi kafin tace "Abin da ku ka aikata kenan? Mariya, Haseenah, wannan ita ce tarbiyyar da mu ka baku a gidan nan? Wannan wane irin zubar da mutumci ne? Kenan mutuwar auren ki ba ya da nasaba da kishiyar ki? Haka kawai kinsa muna kallon ta a matsayin mai laifi, to rashin lafiyar da muke tunanin ki na fama da ita fa har da nemo mi ki magani? Ko dai duk k'arya ce ki ke? Dan babu yanda za ayi mata biyu a gidan miji d'aya su zama mushrikai."
Sosa kai Haseenah take cikin rashin abin fad'a sai tsohuwar ce ta k'ara da "Ko ba ki fad'a ba ya nuna ba ki da gaskiya, amma Haseenah taya ki ka iya shirya makirci irin haka? Ko ni da na haife ki ba zanyi abin da ki kai ba."
Kallon Mariya ta yi sama da k'asa tace "Babbar banza, yanzu idan akwai wanda ya kashe mata aure ai bayanki ya ke."
K'asa ta yi da kanta sosai hakan ya sa tsohuwar juyawa ta fita ta barsu, cikin sanyin jiki Mariya ta fita sai Haseenah da ta fashe da kuka, *Asiya* kuma d'akin ta ta koma ta shirya saida ta fito za ta fita ta lek'a d'akin Haseenah tace "Zan fita yanzu, babu kowa a gidan ki fito ki d'ora girkin rana kafin yaran nan su dawo, daga yau kin bar kwanciya a d'aki da sunan wai ki na da ciki a tausaya mi ki, girki da wanke-wanke ya zama na ki."
Ta na fad'a ta fice abin da har zuwa bakin ti-ti ta samu adaidaita ta hau, kai tsaye gidan Khadija ta isa, duk da ba sosai Khadija tasan ba amma dai ta gane ta, sosai ta tarbe ta kamar za ta had'e ta cikin girmamawa, dama kuma in dai ta wannan fannin ne Khadija gwana ce, hakan ya sa ma take da farin jinin al'uma, har d'akin Bilal ta rakata taga jikin shi kafin su ka dawo falo ta zauna, cike da dattako tsohuwar ta kalli Khadija tace " 'Yata Khadija, na zo ne ganin jikin yaron ki da sai jiya na ke jin bai da lafiya, sai kuma abu na biyu na zo na baki hak'uri akan abin da ya faru, 'yar nan wallahi ba mu tab'a tunanin Haseenah za ta iya cutar da wani ba, amma sai yau kuma yanzu na ke jin irin ta'asar da su ka yi ita da 'yar uwar ta daga bakin su, hak'ik'a yau Allah ya wanke ki daga zargin da mu ke mi ki, muna kallon ki a matsayin wacce take hana 'yar mu zaman gidan aure, ashe ba haka bane komai makircin su ne, ashe har zuwa gidan da take ta nuna bata lafiya ba ta son zaman gidan duk k'arya ne, kawai d'ora mi ki laifi ne suke son yi, dan Allah ki yi hak'uri ki yafe mana kinji 'yar albarka."
Khadija da ta yi jim ta na jinjina al'amarin Haseenah, sai yanzu ne take sanin wannan labarin na rashin lafiya, kenan ita ake kallo da wannan laifin ma, murmushi ta yi ta rik'o hannun Asiya tace "Mama, ke fa uwar ce a gare ni, yanda Mama na bata neman gafara na akan duk abin da za ta min to haka ke ma, wallahi na yafe mu ku dukan ku, ni dama ban tab'a rik'e kowa a zuciya ta ba saboda ina so nima Allah ya kalle ni da idon rahama, dan haka ku kwantar da hankalin ku yanzu mun zama d'aya ni da ku, kuma ita rayuwa dama haka take, wanda wautar shi ta fito fili shi ake kamawa da laifi, wanda kuma ya iya takon shi to ko shine mai laifin sai kaga babu mai gani bare ayi magana, kuma ita dama ance *fahimta fuska* ce."
"Hakane kam, Allah ya mi ki albarka, Allah ya sa ki gama da duniya lafiya, Allah ya kare ki daga sharrin abokan zama irin su Haseenah." Sakin hannun ta Khadija ta yi ta mik'e tace "Ni zan tafi, dama ko mahaifinsu bai san na zo ba."
D'aki Khadija ta shiga ta tarkato kaya sabulu da turaruka da turmin atamfa mai kyau, sannan ta had'o da wani k'aton mayafi da ita bai birge ta ba tunda mama ta siyo mata shi daga Dubai, haka ta had'a tsohuwar nan da su ta rakata har k'ofar gida, Rabe da ke zaune tace ya d'aukar mata kayan har saida ta samu adaidaita, Asiya kam a adaidaita har kuka ta yi ganin irin alherin da Khadija ta yi mata, ta na komawa gida ta samu mahaifinsu ya dawo zaune a tsakar gidan, tun bata gama shigowa ba yace "Daga ina ki ke Asiya?"
Kai tsaye tace "Daga gidan Usman."
Da sauri ya kalle ta haka ma Haseenah da ke bakin murhu ta na girki duk ta yi gumi, cikin hushi yace "Yanzu da na ce kar ki jr shine ki ka wanke k'afa ki ka tafi ba da izini na ba? Asiya yaushe ki ka fara yin watsi da maganata? Akan matar da ta kashe ma yar ki aure ne za ki wulak'anta ni haka?"