Sashe 65
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai lokacin Usman ya juya ya nufi d'akin Khadija, Bilal kuma zaune ya yi kusan Mama ya d'ora kan shi akan k'irjin ta, ture shi ta yi tace "Kai d'aga min nono malam, k'walelen kare da hantar kura fa, tom."
Saida ya sa hannu ya tab'a nonon yace "To me zanyi da wannan tsohon nono, abin duk ya yamutse, ga na Mummy ta nan sabo dal a leda."
Bushewa su ka yi da dariya dukansu ta janyo shi jikin shi su ka rumgume juna, tabbas kamar yanda ta ke matuk'ar k'aunar Khadija matsayin ta na mace, haka a cikin jikokin ta ma take matuk'ar k'aunar Bilal saboda wayon shi, yaro ne mai shiga rai dan shi ko irin mahaukaciyar k'uruciyar nan baiyi ba, hasalima cikin yara za ka ga shi wasan shi ta dabance, sannan bai cika son hayaniya ba kuma baida yawon surutu, idan kaji bakinshi cacaca to sun had'u ita da shi ne.
Tun kafin Usman ya shiga ya ke tunanin abin da suka fad'a na maganar bébé da haihuwa, me su ke nufi? Khadija ciki gare ta kenan? Dama k'ofar a bud'e ta ke dan haka k'arasa tura ta kawai ya yi ya shiga, zaune take akan gado da littafin *hisnul muslum* ta na karantawa, ta na kallon shi ta d'auke kai ta mayar kan littafin tace "Me ya sa ba za ka nemi izini ba kafin ka shigo?"
Saida ya k'arasa shigowa har ya zo daf da gadon yace "Saboda da kai da kaya duk mallakar wuya ne."
Kallon shi ta yi fuska ba annuri tace "Kan na iya zama na ka amma banda kayan saman shi."
Murmushi kawai ya yi yace "Haka ake tarban bak'o a garin ku?"
"Duk bak'on zai iya shiga kowane lungu da sak'o na gida ba bak'o bane, musamman ma irin ka da ba sa neman izini kafin su shiga, kuma ina da tabbaci ba waje na ka zo ba, dan haka me zai sa na damu kai na?"
Kafe ta ya yo da ido ya na kallo kamar ya na karatun wani abu, jin shirun ya yi yawa ne ya sa tace "Bilal fa ya na farfajiyar gida."
"Na gan shi ai." Kallon shi ta yi tace "Hajia kuma ai ta na falo." Saida ya zura hannayen shi aljihu yace "Ita ma mun gaisa."
Mayar da hankalin ta tayi kan littafin ta tace "Da kyau." Ci gaba ta yi da karatun ta shi kuma yace "Ya beby ya ke?"
Cak ta tsaya amma ba ta kalle shi ba sai rarraba ido da ta fara yi, tambayar da take wa kan ta ita ce ya aka yi ya sani? Dan ba ta san Mama ta je ta fad'awa su Hajia ba, rasa abin fad'a ya sa Usman zaune kusan ta ya na k'are mata kallo yace "Kenan da gaske ne? To amma me ya sa ba'a fad'a min ba?"
Kallon shi ta yi cikin dagiya tace "Waya fad'a ma ka ina da ciki? Ko kuma ka na so ka b'ata min rai ne?"
"Ban gane ba? Bayan da kunnuwa na naji Mama ta na fad'a, gashi kuma na tambaye ki amma duk alamu sun nuna gaskiya ne."
Murmushi ta yi tace "Ka taya ni addu'a Allah ya bani nawa nima, amma yanzu ai amaryar ka ce ke da shi, duk da ka ce ina mata bak'in ciki."
Kafe ta ya yi da ido yace "Ki rantse da Allah ba kya da ciki." Cikin mamaki tace "Rantsuwa kuma? To miye na rantsuwar? Abin da na ke nema ido bud'e zan samu kuma na kasa fad'a ma ka."
"Ba ki ke nema ba dai, mu ke nema, kar ki manta da haka, har yanzu ina son sake ganin abin da zai fito daga tsatsonki." Kallon shi kawai ta yi shi kuma ya mik'e yace "Kin dai tabbatar ba ki da komai?"
"Eh." Ta fad'a, sake jajjadawa ya yi "Kin tabbatar babu?" Cikin k'osawa tace "To! Na ce babu, babu, idan ba ka yarda ba ka je ka tambayi su Maman ka ji, su a zatonsu ne ciki gare ni saboda rashin lafiyar da na yi, ni kuma wahala ce ta sani wannan rashin lafiyar na dukan da ka min."
Murmushin gefen labb'a kawai ya yi ya sunkuyo da kan shi kusan fuskar ta yace "Kin tabbatar dai ba kya tare da ciki na ko?"
K'asa ta sauke idon ta hakan ya sa yace "Sai kin kalli ido na." Kallon shi kam ta yi tace "Eh, babu komai." Tsaye ya mik'e yace "Shikenan, amma ki tabbatar duk ranar da na ji labari yasha bambam wallahi sai kin gane kurenki."
Saida ta sake kallon idon shi tace "Na yarda." Jinjina kai ya yi yace "Shikenan, saida safe."
Juyawa ya yi ya fice daga d'akin ta bishi da kallo, saida ta tabbatar ya bar gidan ta fito ta samu Mama ta tambaye ta, ba ta b'oye mata komai ba hakan ya sa tace dan Allah kar su sake ya san ta na da ciki, dalili Mama ta tambaya saita nuna mata kawai ba ta so ya sani yanzu, dan ta na tsoron rashin imanin yarinyar nan matar shi.
*Bayan kwana biyu* an kai kayan Nura, kuma kamar yanda ya fad'a Khadija ma saida ta halarci kai kayan, kuma da yake a dangi ma ba kowa bane yasan abin da ya faru, Haseenah dama ba ta je ba dan haka ma ba su had'u ba, anje lafiya kuma ayi duk abin da ya dace, lokaci kawai za'a jira *wata uku* mai zuwa lokacin hutun farko na yan makaranta, duk lokacin da biki ya taso irin haka akwai wanda Khadija ce ta ke mu su d'inkin anko, yanzun ma ba ta gaza ba ba ta kuma duba abin da ya faru ba, haka ta d'inka kaya kala takwas ta aikawa kowa na shi daga ciki har da Hajia da kuma k'annan ta guda uku, k'annan Baban Usman biyu sai wasu tsofaffi biyu suma, kamar yanda Nura ya yi alk'awari ya kawo Choukra ta wuni gidan su Khadija, sai dare ya zo ya d'auke ta su ka koma bayan tasha goma ta arzik'i.
*Haka* abubuwan suka ci gaba da tafiya da dad'i ba dad'i, Khadija na kula da cikin ta cikin kulawa sosai, Bilal na karatun shi hankali kwance ba tare da matsala ba, ranar da babu karatu kuma Khadija na kiran Nura ya zo ya d'auke shi ya kai shi wajen su Hajia, amma basu tab'a katarin had'uwa da mahaifin shi saboda yanzu gida sai su yi sati kwana shida ko biyar basu gan shi da idon su ba, wayar ma sai da k'yar ake iya samun shi wani lokacin, kuma har yanzu bai san Khadija na da ciki ba, dan malam yace ba ya so ya sani sai in Khadija ce ta fad'a mi shi ko kuma ya gani da kan shi, a haka har aka cinye wata *uku* wanda ya yi daidai da fara shagulgulan bikin Nura, a lokacin Khadija har ta fara zuwa awo dan cikin ta na wata *biyar* ne har ya fito ta yanda duk wani mai ido zai iya ganin shi, tun kwana biyu saura Khadija ta turo Bilal ya kwana nan har zuwa ranar bikin tare da gudummuwarta da na Mama da kuma ta su Ashir, gudummuwar da suka bayar ko yan uwanshi babu wanda ya mi shi wannan bajin ta.
Wajen Haseenah ma haka abin yake, abin da ranta ya so ta ke ci tasha wanda ya mata, Aziza tuni ta jima da gane kurenta, dan kuwa duk aikin gidan ne ita ce ba dare ba rana, idan ba ta yi ba Usman ya balbale ta da jaraba, Haseenah na zaune ta na gatsar 'ya'yan itatuwa, sa'a d'aya shine ba'a cika yin girki a gidan ba kusan kullum saida a siyo daga waje, wani lokacin Aziza ta ci idan an siyo ko kuma ta d'ora wani abu ta ci, duk wannan bai cika damunta ba kamar yanda ta ga Usman ya zama kamar karan farautar Haseenah, in dai ya na gari to ya na gida nanak'e da ita ko gajiya ba ya yi, duk bak'on da zai zo wajen ta to fa haka zai dinga rawar jiki ya na aikawa ana siyo musu abin tab'awa, idan sun tashi tafiya kuma ya wadata su da kud'i da sunan kud'in taxi, haka ita kan ta Haseenah kud'i yake kashe mata kamar ba gobe, a wata *ukun* nan sai Haseenah ta shirga wata murgujejiyar k'iba, masha Allah ko fa kai mak'iyinta ne ka ganta dole k'ibar da ta yi ta burge ka dan ta mata kyau, hakan kuma ya sa Usman sake narke mata dan abun har kusan haukata shi take, ga magunguna da take aiki da su, ga k'iba (wanda kowa yasan akwai sirrin dake tattare da k'iba ba) ga kuma ciki, duk tsiyar nan da ake tsulawa Aziza ta kasa fad'awa kowa saboda kunya, to idan ita ma tace ta mallake shi kenan tsakanin ita da Khadija wacece ta mallake shi? Hakan ya sa ta yi shiru, ko gida taje idan aka tambaye ta wai ya na nan sai dai tace eh, idan ya na nan d'in, dan yanzu ko balaguro ya yi da k'yar yake iya sati d'aya zuwa kwana goma ya dawo, shiru take yi ba ta fad'a mu su komai inda su kuma su ka damu sosai su ka fara maganganu akai.
*Yau* Alhamis ya rage nan da kwana biyu za'a d'aura auren Nura, su Rabi'a sun hallara ana ta kujuba-kujuba Aziza ta shigo gidan, dukan su kallon ta su ka yi da mamakin ganin ta ita kad'ai, Husseina ce tace "Aziza ke kad'ai ki ka taho?"
Saida ta nemi gurin zama tace "Ni kad'ai na taho."
"Ina Haseenah?" Cewar Rabi'a, tab'e baki ta yi tace "Ta na gida, wai ba ta jin dad'in jikin ta."
Hajia da ita ba wannan ne damuwar ta ba cewa ta yi "Ina shi Alhajin ya ke?"
"Ya na gida na baro shi, na ji ya na cewa ko zai kai ta asibiti." Girgiza kai Hajia ta yi tace "Allah ya kyauta, gaba d'aya ta mayar da shi wani sha-katafi, ko motsi taji a cikin ta sai ta fad'a mi shi shi kuma sai yace aje asibiti."
Saida ya sa hannu ya tab'a nonon yace "To me zanyi da wannan tsohon nono, abin duk ya yamutse, ga na Mummy ta nan sabo dal a leda."
Bushewa su ka yi da dariya dukansu ta janyo shi jikin shi su ka rumgume juna, tabbas kamar yanda ta ke matuk'ar k'aunar Khadija matsayin ta na mace, haka a cikin jikokin ta ma take matuk'ar k'aunar Bilal saboda wayon shi, yaro ne mai shiga rai dan shi ko irin mahaukaciyar k'uruciyar nan baiyi ba, hasalima cikin yara za ka ga shi wasan shi ta dabance, sannan bai cika son hayaniya ba kuma baida yawon surutu, idan kaji bakinshi cacaca to sun had'u ita da shi ne.
Tun kafin Usman ya shiga ya ke tunanin abin da suka fad'a na maganar bébé da haihuwa, me su ke nufi? Khadija ciki gare ta kenan? Dama k'ofar a bud'e ta ke dan haka k'arasa tura ta kawai ya yi ya shiga, zaune take akan gado da littafin *hisnul muslum* ta na karantawa, ta na kallon shi ta d'auke kai ta mayar kan littafin tace "Me ya sa ba za ka nemi izini ba kafin ka shigo?"
Saida ya k'arasa shigowa har ya zo daf da gadon yace "Saboda da kai da kaya duk mallakar wuya ne."
Kallon shi ta yi fuska ba annuri tace "Kan na iya zama na ka amma banda kayan saman shi."
Murmushi kawai ya yi yace "Haka ake tarban bak'o a garin ku?"
"Duk bak'on zai iya shiga kowane lungu da sak'o na gida ba bak'o bane, musamman ma irin ka da ba sa neman izini kafin su shiga, kuma ina da tabbaci ba waje na ka zo ba, dan haka me zai sa na damu kai na?"
Kafe ta ya yo da ido ya na kallo kamar ya na karatun wani abu, jin shirun ya yi yawa ne ya sa tace "Bilal fa ya na farfajiyar gida."
"Na gan shi ai." Kallon shi ta yi tace "Hajia kuma ai ta na falo." Saida ya zura hannayen shi aljihu yace "Ita ma mun gaisa."
Mayar da hankalin ta tayi kan littafin ta tace "Da kyau." Ci gaba ta yi da karatun ta shi kuma yace "Ya beby ya ke?"
Cak ta tsaya amma ba ta kalle shi ba sai rarraba ido da ta fara yi, tambayar da take wa kan ta ita ce ya aka yi ya sani? Dan ba ta san Mama ta je ta fad'awa su Hajia ba, rasa abin fad'a ya sa Usman zaune kusan ta ya na k'are mata kallo yace "Kenan da gaske ne? To amma me ya sa ba'a fad'a min ba?"
Kallon shi ta yi cikin dagiya tace "Waya fad'a ma ka ina da ciki? Ko kuma ka na so ka b'ata min rai ne?"
"Ban gane ba? Bayan da kunnuwa na naji Mama ta na fad'a, gashi kuma na tambaye ki amma duk alamu sun nuna gaskiya ne."
Murmushi ta yi tace "Ka taya ni addu'a Allah ya bani nawa nima, amma yanzu ai amaryar ka ce ke da shi, duk da ka ce ina mata bak'in ciki."
Kafe ta ya yi da ido yace "Ki rantse da Allah ba kya da ciki." Cikin mamaki tace "Rantsuwa kuma? To miye na rantsuwar? Abin da na ke nema ido bud'e zan samu kuma na kasa fad'a ma ka."
"Ba ki ke nema ba dai, mu ke nema, kar ki manta da haka, har yanzu ina son sake ganin abin da zai fito daga tsatsonki." Kallon shi kawai ta yi shi kuma ya mik'e yace "Kin dai tabbatar ba ki da komai?"
"Eh." Ta fad'a, sake jajjadawa ya yi "Kin tabbatar babu?" Cikin k'osawa tace "To! Na ce babu, babu, idan ba ka yarda ba ka je ka tambayi su Maman ka ji, su a zatonsu ne ciki gare ni saboda rashin lafiyar da na yi, ni kuma wahala ce ta sani wannan rashin lafiyar na dukan da ka min."
Murmushin gefen labb'a kawai ya yi ya sunkuyo da kan shi kusan fuskar ta yace "Kin tabbatar dai ba kya tare da ciki na ko?"
K'asa ta sauke idon ta hakan ya sa yace "Sai kin kalli ido na." Kallon shi kam ta yi tace "Eh, babu komai." Tsaye ya mik'e yace "Shikenan, amma ki tabbatar duk ranar da na ji labari yasha bambam wallahi sai kin gane kurenki."
Saida ta sake kallon idon shi tace "Na yarda." Jinjina kai ya yi yace "Shikenan, saida safe."
Juyawa ya yi ya fice daga d'akin ta bishi da kallo, saida ta tabbatar ya bar gidan ta fito ta samu Mama ta tambaye ta, ba ta b'oye mata komai ba hakan ya sa tace dan Allah kar su sake ya san ta na da ciki, dalili Mama ta tambaya saita nuna mata kawai ba ta so ya sani yanzu, dan ta na tsoron rashin imanin yarinyar nan matar shi.
*Bayan kwana biyu* an kai kayan Nura, kuma kamar yanda ya fad'a Khadija ma saida ta halarci kai kayan, kuma da yake a dangi ma ba kowa bane yasan abin da ya faru, Haseenah dama ba ta je ba dan haka ma ba su had'u ba, anje lafiya kuma ayi duk abin da ya dace, lokaci kawai za'a jira *wata uku* mai zuwa lokacin hutun farko na yan makaranta, duk lokacin da biki ya taso irin haka akwai wanda Khadija ce ta ke mu su d'inkin anko, yanzun ma ba ta gaza ba ba ta kuma duba abin da ya faru ba, haka ta d'inka kaya kala takwas ta aikawa kowa na shi daga ciki har da Hajia da kuma k'annan ta guda uku, k'annan Baban Usman biyu sai wasu tsofaffi biyu suma, kamar yanda Nura ya yi alk'awari ya kawo Choukra ta wuni gidan su Khadija, sai dare ya zo ya d'auke ta su ka koma bayan tasha goma ta arzik'i.
*Haka* abubuwan suka ci gaba da tafiya da dad'i ba dad'i, Khadija na kula da cikin ta cikin kulawa sosai, Bilal na karatun shi hankali kwance ba tare da matsala ba, ranar da babu karatu kuma Khadija na kiran Nura ya zo ya d'auke shi ya kai shi wajen su Hajia, amma basu tab'a katarin had'uwa da mahaifin shi saboda yanzu gida sai su yi sati kwana shida ko biyar basu gan shi da idon su ba, wayar ma sai da k'yar ake iya samun shi wani lokacin, kuma har yanzu bai san Khadija na da ciki ba, dan malam yace ba ya so ya sani sai in Khadija ce ta fad'a mi shi ko kuma ya gani da kan shi, a haka har aka cinye wata *uku* wanda ya yi daidai da fara shagulgulan bikin Nura, a lokacin Khadija har ta fara zuwa awo dan cikin ta na wata *biyar* ne har ya fito ta yanda duk wani mai ido zai iya ganin shi, tun kwana biyu saura Khadija ta turo Bilal ya kwana nan har zuwa ranar bikin tare da gudummuwarta da na Mama da kuma ta su Ashir, gudummuwar da suka bayar ko yan uwanshi babu wanda ya mi shi wannan bajin ta.
Wajen Haseenah ma haka abin yake, abin da ranta ya so ta ke ci tasha wanda ya mata, Aziza tuni ta jima da gane kurenta, dan kuwa duk aikin gidan ne ita ce ba dare ba rana, idan ba ta yi ba Usman ya balbale ta da jaraba, Haseenah na zaune ta na gatsar 'ya'yan itatuwa, sa'a d'aya shine ba'a cika yin girki a gidan ba kusan kullum saida a siyo daga waje, wani lokacin Aziza ta ci idan an siyo ko kuma ta d'ora wani abu ta ci, duk wannan bai cika damunta ba kamar yanda ta ga Usman ya zama kamar karan farautar Haseenah, in dai ya na gari to ya na gida nanak'e da ita ko gajiya ba ya yi, duk bak'on da zai zo wajen ta to fa haka zai dinga rawar jiki ya na aikawa ana siyo musu abin tab'awa, idan sun tashi tafiya kuma ya wadata su da kud'i da sunan kud'in taxi, haka ita kan ta Haseenah kud'i yake kashe mata kamar ba gobe, a wata *ukun* nan sai Haseenah ta shirga wata murgujejiyar k'iba, masha Allah ko fa kai mak'iyinta ne ka ganta dole k'ibar da ta yi ta burge ka dan ta mata kyau, hakan kuma ya sa Usman sake narke mata dan abun har kusan haukata shi take, ga magunguna da take aiki da su, ga k'iba (wanda kowa yasan akwai sirrin dake tattare da k'iba ba) ga kuma ciki, duk tsiyar nan da ake tsulawa Aziza ta kasa fad'awa kowa saboda kunya, to idan ita ma tace ta mallake shi kenan tsakanin ita da Khadija wacece ta mallake shi? Hakan ya sa ta yi shiru, ko gida taje idan aka tambaye ta wai ya na nan sai dai tace eh, idan ya na nan d'in, dan yanzu ko balaguro ya yi da k'yar yake iya sati d'aya zuwa kwana goma ya dawo, shiru take yi ba ta fad'a mu su komai inda su kuma su ka damu sosai su ka fara maganganu akai.
*Yau* Alhamis ya rage nan da kwana biyu za'a d'aura auren Nura, su Rabi'a sun hallara ana ta kujuba-kujuba Aziza ta shigo gidan, dukan su kallon ta su ka yi da mamakin ganin ta ita kad'ai, Husseina ce tace "Aziza ke kad'ai ki ka taho?"
Saida ta nemi gurin zama tace "Ni kad'ai na taho."
"Ina Haseenah?" Cewar Rabi'a, tab'e baki ta yi tace "Ta na gida, wai ba ta jin dad'in jikin ta."
Hajia da ita ba wannan ne damuwar ta ba cewa ta yi "Ina shi Alhajin ya ke?"
"Ya na gida na baro shi, na ji ya na cewa ko zai kai ta asibiti." Girgiza kai Hajia ta yi tace "Allah ya kyauta, gaba d'aya ta mayar da shi wani sha-katafi, ko motsi taji a cikin ta sai ta fad'a mi shi shi kuma sai yace aje asibiti."