Sashe 63
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya na fad'a ya mik'e ya shiga cikin shagon shi dan ya ba shi dama, Usman kuma na ganin haka saiya mik'e ya tashi ya shiga motar shi shima ya bar wajen, gida ya koma ya na zuwa mai gadi ya bud'e masa k'ofa ya shiga, har ya aje motar a muhallin ta kalaman Murtala na masa yawo, hakan ne ya tilasta masa dafe sitiyari ya rufe ido ya na mayar da nutsuwar sa gare sa, ya jima a haka kafin ya zuba ya bud'e ido saboda ganin Khadija da ya yi cikin doguwar riga bak'a, gefen ta Bilal sai dariya suke suna kallon wani abu da ya birge su, amma ko da ya bud'e ido ya na tuna fuskar ta saiya k'ara had'e fuska, tsaki ya yi kawai ya fito daga motar ya wuce wajen amarya.
Da shigar shi ya samu Haseenah na waya da Mariya akan maganar su, kasancewar a shirye take ya sa tace ta karb'o sak'on ta zo ta amsa ko ta aiko a karb'ar mata, a cewar Haseenah "Zan kira yah Mubarak ya je ya amso min." Da "Sai ya zo." Mariya ta amsa su ka datse wayoyin.
Wanka ya fara shiga ya yi ya fito d'aure da abin tsane ruwa a k'ugu (towel), wayar shi ya d'auka gaban madubi ya danna kiran lambar Bilal, a daidai lokacin Bilal na zaune gaban Khadija su na karatu, ya na fito da wayar daga aljihu ya datse kiran saboda ganin mai kira, irin shi ma wai an tab'a mi shi mahaifiya d'in nan, ganin hakane ya sa Khadija kallon shi tace "Bilal, ba kiran ka ake ba na ga ka na katsewa? Waye haka?"
Turo baki ya yi gaba baice komai ba, dariya Khadija ta yi tace "Ko dai surukata ce ta ke kiran shi ya sa ba ka so ka d'auka gaba na?"
Kamar zai fashe da kuka yace "Mummy."
"To waye ke kira?" Ta fad'a ta na d'aukar wayar da ya aje saman gado, tana dubawa ta ga mahaifin shine ya kira ya katse, da mamaki ta d'ago ta kalle shi tace "Bilal! Mahaifin ka ne dama ya kira ka ke katse shi?"
Kafe ta ya yi da ido, cikin tsawa tace "Da kai na ke magana ka na jina ka yi shiru, ina so na ji hujjar da tasa ka ke datse kiran shi ba ka d'auka."
Cikin turo baki yace "To Mummy ba Abba ne ya daina son mu ba, kuma a gaba na fa ya dakkk..." Kashe shi ta yi da marin da ya sashi saurin dafe kumci ya fashe da kuka, cikin zafin rai ta d'ora yatsanta akan bakin ta tace "Shiiii, kar ka bari na ji sautin muryar ka har zuwa lokacin da zan gama magana."
Gimtse kukan shi ya yi ya na kallon idon ta tace "Bilal matsala ta ce fa da mahaifin ka, kai miye na ka a ciki? Me ya shafe ka da har za ka juyawa mahaifin ka baya a kai na? Kasan me ya faru ne a tsakanin mu? Ko kuma na fad'a ma ka ba na son mahaifin ka ne? To maza kafin na k'irga uku ka kira mahaifin ka ka bashi hak'uri sannan ka nemi gafararsa."
Da sauri ya d'auki wayar ya mayar da kira, Usman da ke cikin saka kaya ne ya ga kiran Bilal, d'auka ya yi kafin yace wani abu Bilal yace "Assalama alaikum, Abba ina wuni."
Wani murmushi Usman ya saki tare da sak'awa a ran shi tabbas Khadija ce ta sashi ya kira shi, dan ya na da yak'ini akan Khadija wajen tarbiyar Bilal, bai iya amsa sallamar sai cewa ya yi "Yariman hushi ka ke da Abban ka?"
Jiki na rawa Bilal yace "A'a Abba ba hushi na ke da kai ba, dan Allah ka yi hak'uri ka yafe min, ba zan k'ara ba insha Allah."
Murmushi ya yi yace "Ba komai yarima ya wuce, ya ka ke? Ya karatu?"
"Lafiya lau Abba." Ya yi maganar ya na kallon Khadija da ta kafe shi da ido, ta na ji su na wayar su kafin daga bisani Usman yace "Yarima yaushe za ka zo mana gida? Kasan fa mu na kewar ka."
Cikin turo baki yace "Gaskiya Abba ba zan je gida ba ba tare da Mummy ba, kawai kai ka zo nan."
Ba tare da damuwa ba yace "Shikenan to, amma idan naje makaranta zan gan ka?"
Cike da k'aguwa yaron yace "Abba! Me ya sa ba za ka zo gida ba?"
"To to shikenan, na ji zan shigo gidan zuwa gobe."
"Wane lokaci?"
Saida ya d'anyi tunani kafin yace "Umm, ina ga zuwa dare zan shigo."
"To Abba." A hankali Usman yace "Saida safe ko, ka yi bacci lafiya."
"To Abba, ga Mumm..." Bai k'arasa fad'a ba ya ji ya datse kiran, kallon maman shi ya yi yace "Mummy ki yi hak'uri to, Abba ya hak'ura."
Janyo shi ta yi ta rumgume hawaye na fita a idon ta tana fad'in "Bilal ba na so ne abin da ke tsakani na da mahaifin ka ya shafe ka, idan ba ka manta ba a baya haka bata faru ba tsakanin mu, yanzu ne haka ta fara faruwa saboda dama ita rayuwa ta gaji haka, ba lallai mutum ya tabbata cikin farin ciki ba, zan iya cewa a rayuwa ta ban tab'a fuskantar matsalar da ta sani bak'in ciki ba kamar wannan, dan haka zanyi hak'uri da jarabawar da Allah ya d'ora min har na cinye ta, ko da kuwa hakan na nufin k'arshen zama na kenan a gidan mahaifin ka."
Da sauri ya d'ago yace "A'a Mummy, gaskiya ba za ku rabu ba, ni dai wallahi idan ku ka rabu to ba za ki sake wani aure ba." Zaro ido Khadija ta yi ta na kallon shi da mamaki tace "Kai kuma a ina ka samu wannan tunanin?"
Cikin shagwab'a yace "To ba *Beby* (d'iyar Ashir ta farko mai sunan maman su) ce tace mana Maman su za ta yi aure ba."
Girgiza kai ta yi tace "Kenan idan ban koma gidan sa ba saina tabbata a cikin d'akin nan? Kai ba ka kishi na ne? Ko ba kaga shi mahaifin naka ya k'ara aure ba, me ya sa ba ka hana shi?"
"To Mummy ai shi namiji, ni kuma ba na so ki sake min wani Abba, na fi so ku zauna ku biyu abunku yafi dad'i." Shiru ta yi tunda shekarun shi basu kai tace dole saita fahimtar da shi ba, sannan ita kan ta tana wa Usman kishin kan ta ta yanda take fatan ya zama mijinta har abada, da haka suka ci gaba da karatun su har dare ya yi su ka kwanta.
*Washe gari* da safe gidan ya yi shiru sosai aka amshi bak'uncin Murtala, dan gaskiya abun bai masa dad'i ba sosai, a falon Hajia suka zauna tare da Khadija da Hajia ya na basu hak'uri da nuna mu su rashin jin dad'in sa, sannan ya d'ora mu su da sam bai sani ba sai jiya, cikin fara'a suka nuna mi shi babu komai haka Allah ya hukunta, kuma ai da sauk'i tunda ba saki bane Allah zai iya daidaita lamarin, haka dai ya tafi abun ba dad'i sai hak'uri kawai.
Yau Usman ya samu malam a gida bai fita ba saboda jiki da jini, saida ya sha ruwan shi kafin ya mik'e zai bar gidan Hajia ta tambaye shi ko yaje ganin Khadija? A cewar shi dai "A'a ban je ba, amma na ce yau zanje anjima."
"To aiko gwara ka tafi dan kasan halin da take ciki." Da mamaki ya kalli Hajia yace "Hajia wani abun ne ke faruwa da ita?"
Cikin murmushi tace "Ai Khadija Allah ya..." Da sauri malam ya d'aga mata hannu alamar ta yi shiru, girgiza mata kai ya yi kawai bai ce komai ba, jin ba tace komai ba ya sake mu su sallama ya fita, Hajia kuma malam ta kalla tace "Me ya sa ba ka so ya sani? Ya na da hakk'in sani fa."
"Ki barshi kawai, idan ya je saita fad'a ma sa idan ta so ya sani, idan kuma ba ta so ba saiya gano da kan sa." Har ya mik'e zai fita Hajia tace "To amma ni banga anfanin b'oyewar ba."
Juyowa ya yi ya kalle ta yace "Ni kuma na gani, in dai ina fad'a aji to ban yarda ki fad'a ma sa da bakin ki ba, dan halin da Fodio yake ciki yanzu ba ya iya rik'e sirrin kan shi ma bare na wani, a gaskiya ni ban yarda da amaryar nan tasa ba."
Da *yamma* Khadija su na farfajiyar gida yara duk sun cika gidan da hayaniya suka ji sallama, amsawa akayi tare da masa izinin shigowa, Bilal na ganin shi da gudu yaje ya rumgumr shi, Khadija ma na juyowa ta mik'e ta na dariya saboda farin cikin ganin shi ta na fad'in "...
*Addu'ar ku tamkar takobi ce a gare ni mafi kaifi a duniya, ina k'aunar ku masoya.*
25/02/2020 à 21:16 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*32*
"Ango kai ne a gidan namu, lallai babban bak'o, amma dai da alama hanya ce ta d'auka ka ya sa ka biyo nan, ba dan haka ba ni dai na san ka da tsoron bayar da kud'in cefanai."
Dariya ake in da ta nufi falon Mama ta na fad'in "Bismillah Nura shigo." Bayan ta ya bi ya na rik'e da hannu Bilal, saida ya gaisa da mutanen da ke nan kafin ya k'arasa shiga ciki, zaune ya yi akan kujera ita ma ta zauna bayan ta aje ma sa ruwa da lemu, kallon ta ya yi yace "Ke haka ake sai ki tarfani a gaban manyan mutane, sai kisa su d'auka gaske ne abin da ki ka fad'a."
Da shigar shi ya samu Haseenah na waya da Mariya akan maganar su, kasancewar a shirye take ya sa tace ta karb'o sak'on ta zo ta amsa ko ta aiko a karb'ar mata, a cewar Haseenah "Zan kira yah Mubarak ya je ya amso min." Da "Sai ya zo." Mariya ta amsa su ka datse wayoyin.
Wanka ya fara shiga ya yi ya fito d'aure da abin tsane ruwa a k'ugu (towel), wayar shi ya d'auka gaban madubi ya danna kiran lambar Bilal, a daidai lokacin Bilal na zaune gaban Khadija su na karatu, ya na fito da wayar daga aljihu ya datse kiran saboda ganin mai kira, irin shi ma wai an tab'a mi shi mahaifiya d'in nan, ganin hakane ya sa Khadija kallon shi tace "Bilal, ba kiran ka ake ba na ga ka na katsewa? Waye haka?"
Turo baki ya yi gaba baice komai ba, dariya Khadija ta yi tace "Ko dai surukata ce ta ke kiran shi ya sa ba ka so ka d'auka gaba na?"
Kamar zai fashe da kuka yace "Mummy."
"To waye ke kira?" Ta fad'a ta na d'aukar wayar da ya aje saman gado, tana dubawa ta ga mahaifin shine ya kira ya katse, da mamaki ta d'ago ta kalle shi tace "Bilal! Mahaifin ka ne dama ya kira ka ke katse shi?"
Kafe ta ya yi da ido, cikin tsawa tace "Da kai na ke magana ka na jina ka yi shiru, ina so na ji hujjar da tasa ka ke datse kiran shi ba ka d'auka."
Cikin turo baki yace "To Mummy ba Abba ne ya daina son mu ba, kuma a gaba na fa ya dakkk..." Kashe shi ta yi da marin da ya sashi saurin dafe kumci ya fashe da kuka, cikin zafin rai ta d'ora yatsanta akan bakin ta tace "Shiiii, kar ka bari na ji sautin muryar ka har zuwa lokacin da zan gama magana."
Gimtse kukan shi ya yi ya na kallon idon ta tace "Bilal matsala ta ce fa da mahaifin ka, kai miye na ka a ciki? Me ya shafe ka da har za ka juyawa mahaifin ka baya a kai na? Kasan me ya faru ne a tsakanin mu? Ko kuma na fad'a ma ka ba na son mahaifin ka ne? To maza kafin na k'irga uku ka kira mahaifin ka ka bashi hak'uri sannan ka nemi gafararsa."
Da sauri ya d'auki wayar ya mayar da kira, Usman da ke cikin saka kaya ne ya ga kiran Bilal, d'auka ya yi kafin yace wani abu Bilal yace "Assalama alaikum, Abba ina wuni."
Wani murmushi Usman ya saki tare da sak'awa a ran shi tabbas Khadija ce ta sashi ya kira shi, dan ya na da yak'ini akan Khadija wajen tarbiyar Bilal, bai iya amsa sallamar sai cewa ya yi "Yariman hushi ka ke da Abban ka?"
Jiki na rawa Bilal yace "A'a Abba ba hushi na ke da kai ba, dan Allah ka yi hak'uri ka yafe min, ba zan k'ara ba insha Allah."
Murmushi ya yi yace "Ba komai yarima ya wuce, ya ka ke? Ya karatu?"
"Lafiya lau Abba." Ya yi maganar ya na kallon Khadija da ta kafe shi da ido, ta na ji su na wayar su kafin daga bisani Usman yace "Yarima yaushe za ka zo mana gida? Kasan fa mu na kewar ka."
Cikin turo baki yace "Gaskiya Abba ba zan je gida ba ba tare da Mummy ba, kawai kai ka zo nan."
Ba tare da damuwa ba yace "Shikenan to, amma idan naje makaranta zan gan ka?"
Cike da k'aguwa yaron yace "Abba! Me ya sa ba za ka zo gida ba?"
"To to shikenan, na ji zan shigo gidan zuwa gobe."
"Wane lokaci?"
Saida ya d'anyi tunani kafin yace "Umm, ina ga zuwa dare zan shigo."
"To Abba." A hankali Usman yace "Saida safe ko, ka yi bacci lafiya."
"To Abba, ga Mumm..." Bai k'arasa fad'a ba ya ji ya datse kiran, kallon maman shi ya yi yace "Mummy ki yi hak'uri to, Abba ya hak'ura."
Janyo shi ta yi ta rumgume hawaye na fita a idon ta tana fad'in "Bilal ba na so ne abin da ke tsakani na da mahaifin ka ya shafe ka, idan ba ka manta ba a baya haka bata faru ba tsakanin mu, yanzu ne haka ta fara faruwa saboda dama ita rayuwa ta gaji haka, ba lallai mutum ya tabbata cikin farin ciki ba, zan iya cewa a rayuwa ta ban tab'a fuskantar matsalar da ta sani bak'in ciki ba kamar wannan, dan haka zanyi hak'uri da jarabawar da Allah ya d'ora min har na cinye ta, ko da kuwa hakan na nufin k'arshen zama na kenan a gidan mahaifin ka."
Da sauri ya d'ago yace "A'a Mummy, gaskiya ba za ku rabu ba, ni dai wallahi idan ku ka rabu to ba za ki sake wani aure ba." Zaro ido Khadija ta yi ta na kallon shi da mamaki tace "Kai kuma a ina ka samu wannan tunanin?"
Cikin shagwab'a yace "To ba *Beby* (d'iyar Ashir ta farko mai sunan maman su) ce tace mana Maman su za ta yi aure ba."
Girgiza kai ta yi tace "Kenan idan ban koma gidan sa ba saina tabbata a cikin d'akin nan? Kai ba ka kishi na ne? Ko ba kaga shi mahaifin naka ya k'ara aure ba, me ya sa ba ka hana shi?"
"To Mummy ai shi namiji, ni kuma ba na so ki sake min wani Abba, na fi so ku zauna ku biyu abunku yafi dad'i." Shiru ta yi tunda shekarun shi basu kai tace dole saita fahimtar da shi ba, sannan ita kan ta tana wa Usman kishin kan ta ta yanda take fatan ya zama mijinta har abada, da haka suka ci gaba da karatun su har dare ya yi su ka kwanta.
*Washe gari* da safe gidan ya yi shiru sosai aka amshi bak'uncin Murtala, dan gaskiya abun bai masa dad'i ba sosai, a falon Hajia suka zauna tare da Khadija da Hajia ya na basu hak'uri da nuna mu su rashin jin dad'in sa, sannan ya d'ora mu su da sam bai sani ba sai jiya, cikin fara'a suka nuna mi shi babu komai haka Allah ya hukunta, kuma ai da sauk'i tunda ba saki bane Allah zai iya daidaita lamarin, haka dai ya tafi abun ba dad'i sai hak'uri kawai.
Yau Usman ya samu malam a gida bai fita ba saboda jiki da jini, saida ya sha ruwan shi kafin ya mik'e zai bar gidan Hajia ta tambaye shi ko yaje ganin Khadija? A cewar shi dai "A'a ban je ba, amma na ce yau zanje anjima."
"To aiko gwara ka tafi dan kasan halin da take ciki." Da mamaki ya kalli Hajia yace "Hajia wani abun ne ke faruwa da ita?"
Cikin murmushi tace "Ai Khadija Allah ya..." Da sauri malam ya d'aga mata hannu alamar ta yi shiru, girgiza mata kai ya yi kawai bai ce komai ba, jin ba tace komai ba ya sake mu su sallama ya fita, Hajia kuma malam ta kalla tace "Me ya sa ba ka so ya sani? Ya na da hakk'in sani fa."
"Ki barshi kawai, idan ya je saita fad'a ma sa idan ta so ya sani, idan kuma ba ta so ba saiya gano da kan sa." Har ya mik'e zai fita Hajia tace "To amma ni banga anfanin b'oyewar ba."
Juyowa ya yi ya kalle ta yace "Ni kuma na gani, in dai ina fad'a aji to ban yarda ki fad'a ma sa da bakin ki ba, dan halin da Fodio yake ciki yanzu ba ya iya rik'e sirrin kan shi ma bare na wani, a gaskiya ni ban yarda da amaryar nan tasa ba."
Da *yamma* Khadija su na farfajiyar gida yara duk sun cika gidan da hayaniya suka ji sallama, amsawa akayi tare da masa izinin shigowa, Bilal na ganin shi da gudu yaje ya rumgumr shi, Khadija ma na juyowa ta mik'e ta na dariya saboda farin cikin ganin shi ta na fad'in "...
*Addu'ar ku tamkar takobi ce a gare ni mafi kaifi a duniya, ina k'aunar ku masoya.*
25/02/2020 à 21:16 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*32*
"Ango kai ne a gidan namu, lallai babban bak'o, amma dai da alama hanya ce ta d'auka ka ya sa ka biyo nan, ba dan haka ba ni dai na san ka da tsoron bayar da kud'in cefanai."
Dariya ake in da ta nufi falon Mama ta na fad'in "Bismillah Nura shigo." Bayan ta ya bi ya na rik'e da hannu Bilal, saida ya gaisa da mutanen da ke nan kafin ya k'arasa shiga ciki, zaune ya yi akan kujera ita ma ta zauna bayan ta aje ma sa ruwa da lemu, kallon ta ya yi yace "Ke haka ake sai ki tarfani a gaban manyan mutane, sai kisa su d'auka gaske ne abin da ki ka fad'a."