Sashe 48
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Murmushi Mama ta yi tace "Alhaji ka k'yale shi haka, to idan yace ya saka mu su ido suyi yanda su ka dama suna fakewa bayan kishi, ai kuwa kullum da tsiyar da za su b'ullu da ita a gidan, hakan zaisa ba za'a zauna lafiya ba, ni banga laifin shi ba dan hakan shine daidai, ka na ji ko." Mama ta fad'a ta na kallon shi cike da kulawa, kallonta ya yi take kuma ya sunkuyar da kan shi k'asa, d'orawa ta yi da "Ka yi hak'uri dan Allah akan abin da ya faru, insha Allahu zan ja mata kunne hakan ba zai sake faruwa ba, abinka ne da d'an yau ka haife shi baka haifi halinshi ba, babu irin tausar zuciyar da ban mata ba, amma ba ta ji ba ko kad'an, amma ka yi hak'uri kaji, insha Allah za ta kiyaye a gaba."
Kallon malam ta yi tace "Bara na kira mu ku ita sai ku tafi ko." Cike da dattako malam yace "Shikenan Hajia mun gode sosai da karamci, Allah ya bar zumunci."
Mama na wucewa d'akin Khadija dake ta cika ta na batsewa Usman ya d'ago kai a hankali ya kalli su Ashir da duk su ka hakimce su na kallon shi, d'auke kan shi ya yi dan gani yake kamar za su rufe shi da duka, dan ko basu fad'a ba kasan ba haka su ka so ba, musamman Naseer da Habeeb da bakin su ke ta motsi😂, a d'aki kam tuburewa Khadija ta yi wai babu in da za ta je, saida Mama ta fara nuna b'acin ran ta kad'ai ta fito ta na kumburo baki, wajen yan uwan ta ta tsaya ta ja birki ta na kallon su, Naseer ne yace "Ki yi hak'uri kinji auta, Hajia tace ba ta yarda mu ce komai ba."
Kallon Usman ta yi da shima yake kallon ta, har ga Allah kafin ta fito ya ji ya na son ya koma tare da matar shi, amma ya na ganin ta yanzu sai ya ji kamar yace ta yi zamanta ko kuma ya rufe ta da duka, haka kawai ya ji ranshi ya b'ace ko da ya ganta, amma sai ya dake ya mayar da hankalin shi kan Mama da tace "Maza ki bawa mijin ki hak'uri yanzun nan, sannan ki mi shi alk'awarin hakan ba za ta sake faruwa ba, in kuma ki ka sake to fad'an ni da ke ne ba da shi ba."
Kamar za ta yi kuka ta kalli Mama tace "Mama, wai ni ce ma zan ba shi hak'uri? Har fa mari na ya yi mama, kuma dama duk na ji abin da ka fad'a ina d'aki." Ta fad'a ta na mayar da hankalinta kanshi, ci gaba ta yi da cewa "Bansan me ya sa za ku yi tunanin na lalata abincin yarinyar nan ba, domin Allah ku dube ni da kyau ku dubi Haseenah, ace na rasa ta yanda zanyi na yi maganinta akan kishi saita hanyar zuba gishiri a abincin ta, haba dai kuma, wannan ai abune da hankali ba zai d'auka ba, kenan ma ta gagare ni?"
"Khadija." Mama ta fad'a cikin tsawa, shiru ta yi ta kalli Mama, cikin b'acin rai tace "Rashin kunyar da ya fad'a mana ki na masa ita ce za ki nuna mana sanfurin da ki ke ma sa?"
A hankali ta durk'usa duka gwiwoyinta biyu tace "Ki yi hak'uri Mama."
"Ba ni za ki bawa hak'uri ba, mijin ki ne gashi nan."
Saida ta had'e hawayen ta kad'ai ta kalle shi tace "Ka yi hak'uri." Yanda ta turo baki ne ya sa Mama cewa "Anya kuwa Khadija ke ce? Ke ce Khadija auta ta da na sani."
Kallon maman ta tayi ta sake kallon Usman ta saisaita murya tace "Ka yi hak'uri Abban Bilal, insha Allah ba zan sake ba."
Da k'yar ya iya k'arfin halin k'ak'aro mata murmushi yace "Ba komai ai ya wuce, ni ma ki yi hak'uri abisa marin ki da na yi, kuskure ne da b'acin rai."
'Anzo wajen." Cewar Naseer, d'agowa ya yi daga jinginar da ya yi a bayan kujera yace "D'an uwa Usman dan Allah a dinga kiyayewa, shi duka a fuska ya na da had'ari sosai, mari kan iya jayo makanta, mari ya kan iya sanadin rasa ji, mari zai iya sakawa haure ya fita, mari kan saka kai ya yi ciwo, dama wasu matsaloli da dama, ka ga sai a dinga sanin me za ayi idan rai ya b'ace."
Yasan ba lallai Mama ta yi shiru ba, dan haka ya na fad'a ya tashi ya bar falon ya nufi b'angaren shi, da murmushi Usman ya bishi ya kalli sauran yace "In Allah ya yarda ma ba za ta sake faruwa ba, wannan ma tsautsayi ne."
"Allah ya kiyaye gaba." Cewar Ashir, haka suka tashi su ka koma gida, saida ya ajeta gida kafin ya wuce ya kai malam, Bilal ya yi farin cikin ganin mahaifiyar shi, Haseenah kam ba ta ji dad'i ba ko kad'an, sai dai tasan nan ba da jimawa ba za ta koma tunda yanzu sai yanda ta yi da Usman.
A matsayin kwanan Khadija ne yau ta shirya ta kuma je har d'akin shi kamar yanda ta saba, tabbas ya kwana d'akin, amma da kwanan shi da rashin kwanan duk d'aya, dan kuwa baya ya juya mata ko uhum ba ta ji daga bakin shi ba har ya yi bacci, amma ita ba ta yi baccin ba sai nafila da ta kwana ta na yi ta na kaiwa Allah kukanta, har asuba tana nan kafin ya tafi masallaci ita kuma tayi sallah, bayan ta kammala ta shiga madafa ta d'ora girki.
Usman kuma na dawowa daga masallaci d'akin Haseenah ya nufa su ka gaisa, daga nan ya fad'a mata gobe fa zai yi tafiyar nan ta shirya in tana zuwa, amma bayan tunani da tayi sai taga za'a zargeta idan suka tafi tare, dan haka ta marairaice tace "Um,um gaskiya ni na fasa tafiyar ma, ka ga kai kasuwancin ka ne zai kai ka, bai kamata muje tare ba kuma na hana ka sabgar gaban ka, kawai kaje Allah ya tsare mana kai, ranar da na haihu sai mu tafi tare da yaronmu mushak'ata."
Saida ya rumgume ta yace "Gaskiya ban ji dad'i ba, Haseenah ba zan iya farin ciki ba ki na nesa da ni, me ya sa ba za ki je ba? Zan iya yin wata d'aya fa ko sati uku ban dawo ba, ki na ganin zan iya rik'e kai na bayan na saba da ke a d'an lokacin nan."
Cike da gatsali tace "To ba ga aunty Khadija ba, ku je tare mana, ni kuma sai mu zauna abunmu ni da yarona Bilal, ko ya ka ce?"
Tunda ta ambaci sunan ya ji kamar ta jefe shi da mashi akan tsohon ciwon shi, b'ata rai ya yi yace "Ya ina magana da ke za ki kawo min maganar matar can? Gaskiya ba na so kar ki sake."
Saida ta shafi fuskar shi tace "To shikenan yi hak'uri ba zan sake ba."
"To yanzu fad'a min za ki je ne?" Ya fad'a ya na k'ara cukuikuyeta, ba alamar wasa tace "Gaskiya ba zan je ba, kawai ka tafi kai kad'ai."
"Shikenan, amma taya zan barki ki zauna tare da matar can? Na ga fa ba wani sakin jiki ki ke da ita ba."
Shiru ta yi ta na tunanin abinyi ita ma, da sauri yace "Ko na kira Hajia ta turo mi ki Aziza? Tunda kinga dama ita ce ke zuwa nan idan zanyi tafiya."
Wani murmushi ta yi da bai kai ciki ba tace "To shikenan ba damuwa, hakan ma ya yi ai."
Da haka ya fito ya shiga d'akin shi ya yi wanka ya shirya ya fito kan teburi, saida Haseenah ta fito kafin su ka fara cin abincin, tabbas daga yanda ya ke cin abincin za ka san ya masa dad'i, amma da zaran ya had'a ido da wacce ta dafa abincin saiya d'aure fuska, haka su ka gama ya tashi ya fita su ka bishi da addu'a, Khadija da ta bi bayan shi har wajen mota sannan ya juyo ya kalle ta yace "Ya dai malama ki ke bina haka?"
Murmushi ta yi tace "Abban Bilal hushi ka ke dani har yanzu akan abin da ya faru?"
Wani d'auke kai ya yi yace "Mtsss, ba komai kawai, kawai dai ki na ba ni mamaki ne."
A hankali ta janyo hannun shi ta na shafawa, in da shi kuma ya ke jin kamar hannun wuta ne da ita, cikin taushin muryar da tasan ta na tasiri akan mijin ta ta fara magana "Dan Allah ka yi hak'uri ka yafe min, insha Allah ba zan sake b'ata ma ka rai ba, ka ji? Ka yafe min, kasan hankali na ba ya kwanciya idan ina ganin ka haka."
Saida ya raba hannunshi da na ta yace "Shikenan ba komai, Allah ya sa haka."
Juyawa ya yi zai shiga mota tace "Shikenan kuma ba komai za ka tafi."
"Kamar me fa?"
Cikin yanayin jan hankali tace "Ba rumgumewa, ba sumbata, abun ba armashi."
Kallon malam ta yi tace "Bara na kira mu ku ita sai ku tafi ko." Cike da dattako malam yace "Shikenan Hajia mun gode sosai da karamci, Allah ya bar zumunci."
Mama na wucewa d'akin Khadija dake ta cika ta na batsewa Usman ya d'ago kai a hankali ya kalli su Ashir da duk su ka hakimce su na kallon shi, d'auke kan shi ya yi dan gani yake kamar za su rufe shi da duka, dan ko basu fad'a ba kasan ba haka su ka so ba, musamman Naseer da Habeeb da bakin su ke ta motsi😂, a d'aki kam tuburewa Khadija ta yi wai babu in da za ta je, saida Mama ta fara nuna b'acin ran ta kad'ai ta fito ta na kumburo baki, wajen yan uwan ta ta tsaya ta ja birki ta na kallon su, Naseer ne yace "Ki yi hak'uri kinji auta, Hajia tace ba ta yarda mu ce komai ba."
Kallon Usman ta yi da shima yake kallon ta, har ga Allah kafin ta fito ya ji ya na son ya koma tare da matar shi, amma ya na ganin ta yanzu sai ya ji kamar yace ta yi zamanta ko kuma ya rufe ta da duka, haka kawai ya ji ranshi ya b'ace ko da ya ganta, amma sai ya dake ya mayar da hankalin shi kan Mama da tace "Maza ki bawa mijin ki hak'uri yanzun nan, sannan ki mi shi alk'awarin hakan ba za ta sake faruwa ba, in kuma ki ka sake to fad'an ni da ke ne ba da shi ba."
Kamar za ta yi kuka ta kalli Mama tace "Mama, wai ni ce ma zan ba shi hak'uri? Har fa mari na ya yi mama, kuma dama duk na ji abin da ka fad'a ina d'aki." Ta fad'a ta na mayar da hankalinta kanshi, ci gaba ta yi da cewa "Bansan me ya sa za ku yi tunanin na lalata abincin yarinyar nan ba, domin Allah ku dube ni da kyau ku dubi Haseenah, ace na rasa ta yanda zanyi na yi maganinta akan kishi saita hanyar zuba gishiri a abincin ta, haba dai kuma, wannan ai abune da hankali ba zai d'auka ba, kenan ma ta gagare ni?"
"Khadija." Mama ta fad'a cikin tsawa, shiru ta yi ta kalli Mama, cikin b'acin rai tace "Rashin kunyar da ya fad'a mana ki na masa ita ce za ki nuna mana sanfurin da ki ke ma sa?"
A hankali ta durk'usa duka gwiwoyinta biyu tace "Ki yi hak'uri Mama."
"Ba ni za ki bawa hak'uri ba, mijin ki ne gashi nan."
Saida ta had'e hawayen ta kad'ai ta kalle shi tace "Ka yi hak'uri." Yanda ta turo baki ne ya sa Mama cewa "Anya kuwa Khadija ke ce? Ke ce Khadija auta ta da na sani."
Kallon maman ta tayi ta sake kallon Usman ta saisaita murya tace "Ka yi hak'uri Abban Bilal, insha Allah ba zan sake ba."
Da k'yar ya iya k'arfin halin k'ak'aro mata murmushi yace "Ba komai ai ya wuce, ni ma ki yi hak'uri abisa marin ki da na yi, kuskure ne da b'acin rai."
'Anzo wajen." Cewar Naseer, d'agowa ya yi daga jinginar da ya yi a bayan kujera yace "D'an uwa Usman dan Allah a dinga kiyayewa, shi duka a fuska ya na da had'ari sosai, mari kan iya jayo makanta, mari ya kan iya sanadin rasa ji, mari zai iya sakawa haure ya fita, mari kan saka kai ya yi ciwo, dama wasu matsaloli da dama, ka ga sai a dinga sanin me za ayi idan rai ya b'ace."
Yasan ba lallai Mama ta yi shiru ba, dan haka ya na fad'a ya tashi ya bar falon ya nufi b'angaren shi, da murmushi Usman ya bishi ya kalli sauran yace "In Allah ya yarda ma ba za ta sake faruwa ba, wannan ma tsautsayi ne."
"Allah ya kiyaye gaba." Cewar Ashir, haka suka tashi su ka koma gida, saida ya ajeta gida kafin ya wuce ya kai malam, Bilal ya yi farin cikin ganin mahaifiyar shi, Haseenah kam ba ta ji dad'i ba ko kad'an, sai dai tasan nan ba da jimawa ba za ta koma tunda yanzu sai yanda ta yi da Usman.
A matsayin kwanan Khadija ne yau ta shirya ta kuma je har d'akin shi kamar yanda ta saba, tabbas ya kwana d'akin, amma da kwanan shi da rashin kwanan duk d'aya, dan kuwa baya ya juya mata ko uhum ba ta ji daga bakin shi ba har ya yi bacci, amma ita ba ta yi baccin ba sai nafila da ta kwana ta na yi ta na kaiwa Allah kukanta, har asuba tana nan kafin ya tafi masallaci ita kuma tayi sallah, bayan ta kammala ta shiga madafa ta d'ora girki.
Usman kuma na dawowa daga masallaci d'akin Haseenah ya nufa su ka gaisa, daga nan ya fad'a mata gobe fa zai yi tafiyar nan ta shirya in tana zuwa, amma bayan tunani da tayi sai taga za'a zargeta idan suka tafi tare, dan haka ta marairaice tace "Um,um gaskiya ni na fasa tafiyar ma, ka ga kai kasuwancin ka ne zai kai ka, bai kamata muje tare ba kuma na hana ka sabgar gaban ka, kawai kaje Allah ya tsare mana kai, ranar da na haihu sai mu tafi tare da yaronmu mushak'ata."
Saida ya rumgume ta yace "Gaskiya ban ji dad'i ba, Haseenah ba zan iya farin ciki ba ki na nesa da ni, me ya sa ba za ki je ba? Zan iya yin wata d'aya fa ko sati uku ban dawo ba, ki na ganin zan iya rik'e kai na bayan na saba da ke a d'an lokacin nan."
Cike da gatsali tace "To ba ga aunty Khadija ba, ku je tare mana, ni kuma sai mu zauna abunmu ni da yarona Bilal, ko ya ka ce?"
Tunda ta ambaci sunan ya ji kamar ta jefe shi da mashi akan tsohon ciwon shi, b'ata rai ya yi yace "Ya ina magana da ke za ki kawo min maganar matar can? Gaskiya ba na so kar ki sake."
Saida ta shafi fuskar shi tace "To shikenan yi hak'uri ba zan sake ba."
"To yanzu fad'a min za ki je ne?" Ya fad'a ya na k'ara cukuikuyeta, ba alamar wasa tace "Gaskiya ba zan je ba, kawai ka tafi kai kad'ai."
"Shikenan, amma taya zan barki ki zauna tare da matar can? Na ga fa ba wani sakin jiki ki ke da ita ba."
Shiru ta yi ta na tunanin abinyi ita ma, da sauri yace "Ko na kira Hajia ta turo mi ki Aziza? Tunda kinga dama ita ce ke zuwa nan idan zanyi tafiya."
Wani murmushi ta yi da bai kai ciki ba tace "To shikenan ba damuwa, hakan ma ya yi ai."
Da haka ya fito ya shiga d'akin shi ya yi wanka ya shirya ya fito kan teburi, saida Haseenah ta fito kafin su ka fara cin abincin, tabbas daga yanda ya ke cin abincin za ka san ya masa dad'i, amma da zaran ya had'a ido da wacce ta dafa abincin saiya d'aure fuska, haka su ka gama ya tashi ya fita su ka bishi da addu'a, Khadija da ta bi bayan shi har wajen mota sannan ya juyo ya kalle ta yace "Ya dai malama ki ke bina haka?"
Murmushi ta yi tace "Abban Bilal hushi ka ke dani har yanzu akan abin da ya faru?"
Wani d'auke kai ya yi yace "Mtsss, ba komai kawai, kawai dai ki na ba ni mamaki ne."
A hankali ta janyo hannun shi ta na shafawa, in da shi kuma ya ke jin kamar hannun wuta ne da ita, cikin taushin muryar da tasan ta na tasiri akan mijin ta ta fara magana "Dan Allah ka yi hak'uri ka yafe min, insha Allah ba zan sake b'ata ma ka rai ba, ka ji? Ka yafe min, kasan hankali na ba ya kwanciya idan ina ganin ka haka."
Saida ya raba hannunshi da na ta yace "Shikenan ba komai, Allah ya sa haka."
Juyawa ya yi zai shiga mota tace "Shikenan kuma ba komai za ka tafi."
"Kamar me fa?"
Cikin yanayin jan hankali tace "Ba rumgumewa, ba sumbata, abun ba armashi."