Sashe 28
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hannun shi ya kama ya na juyowa ya na kallon Khadija, ita kam wani shegen murgud'a baki ta yi irin ai ba ka ma isa d'in nan ba, daga yanda ya motsa bakin shi ya tabbatar mata da k'wafa ce ya yi, gwalo ta masa tare da d'ora k'afa d'aya kan d'aya ta d'auki wayar ta, su na fita ta ci gaba da latsa wayar ta hankali kwance, kamar daga sama ta ke jin k'amshin daddawar kalwa na bad'e ko ina na gidan, tashi ta yi ta fito farfajiyar gidan sai ta fahimci daga madafar su ne ya ke fitowa, kai tsaye ta shiga ta samu Haseenah ta zage ta na tuk'a tuwon shinkafa, da murmushi Khadija tace "Amarya sannu da aiki, yau kuma tuwo ake mana?"
Wani takaici ne ya taso ma Haseenah wacce ke wahalar tuk'a tuwon, k'ala ba tace mata ba sai Khadija ce ta sake cewa "Sai dai kuma mijinki baya cin tuwo da dare, ko bai tab'a fad'a mi ki ba? Musamman ma na ga wake ne ki ke miyar da shi, kuma ba ya cin wake ko kad'an, amma za ki iya had'a ma sa wani sassauk'an abun, mu sai mu ci tuwon dan munyi kewar shi."
Ran Haseenah ne ya yi mugun b'aci tace "Kutumar uba, baiwar Allah na fad'a mi ki ina neman taimakon ki ne? Kinga Khadija, gaskiya ba na son haka, mijin ki ba ya cin tuwo a lokacin da ke kad'ai ce cikin gidan, yanzu kuma Haseenah ta shigo, dan haka ki barni na yi rayuwa ta mana, ki barni ni ma na kafa salon nawa tarihin a gidan nan kuma a zuciyar miji na, amma ba ki dinga min shishigi ba, ba lallai dan kin saba mi shi da saka kalar fari ba ki ce nima wannan kalar ki ke so na saka mi shi, ki barni na yi abin da ya dace, nan gidan miji na ne."
Wani warrr Khadija ta yi da manyan idon ta kafin ta sa hannun ta tana fifita da shi tana fad'in "Wash Allah, zafi."
Kallon Haseenah ta yi da murmushi tace "Sannu mai miji, Allah ya bar k'auna."
"Ameen." Ta fad'a har da zaburowa, fita Khadija ta yi, tsaf Haseenah ta gama tuwonta ta mulmule, da kan ta ta kawowa Khadija na su tuwon, ko k'ala ita ma ba tace da ita ba har ta fita, Uwani ce ta tashi tafiya tace "Uwani d'auko wani kwano a d'akin can ki tafi da abincin nan."
D'aya d'akin ta shiga da ke da tarkacai abubuwan buk'ata ta fito, juye tuwon ta yi ta tafi da shi bayan sun yi sallama, Bilal ne ya shigo gida shi kad'ai da takarda a hannun shi, rumgume maman shi ya yi ita kuma tace "Wa ya dawo da kai ne?"
" *Bilyaminu* ne Abba ya tura ya d'auko ni, Mummy karb'i wannan." Ya fad'a bata takardar, ta na dubawa tace "Har wata ya k'are kenan?"
Kai kaxai ya d'aga mata, ba shi ta yi tace "To ka aje wurinka idan Abbanka ya dawo sai ka ba shi, amma ni zan iya mantawa."
A tare su ka tashi ita ta shiga d'akin ta saboda magriba ta gabato sosai, kaya kawai Bilal ya canza ya wuce masallaci, Khadija ma na idar da sallah ta shiga wanka, shiryawa ta yi sosai kafin ta lalabi gilashin ta na jiya da Usman ya cilla kan gadon, dan tun jiya bata waiwaye shi, shi ta saka dan ya fi mata kyau sannan ta fito, zaune suke ita da Bilal su na kallo su na hirar su, bayan sallah isha'i ko da su ka yi sallah abincin ranar da Uwani ta kwashe mata a kula ta d'auko ta zuba, tare su ka ci hankali kwance su ka k'oshi, hamdala su ka yi kafin su ka tashi kamar ba su ci ba.
Kamar yanda ya yi alk'awarin komawa gida haka ya wuce, ya kuma samu su Kabir Mannir da Nura, hakan ya sa suka bud'a babin hira su ka dinga yi, Haseenah da ke jiran shigowar shi taga shiru sai da ta kai ga kira, amma sai ya d'aga yace ya na gida zai zo ba da jimawa ba, amma fa bai zo d'in ba saboda suna tattaunawa da ahalin shi, sai wajen *22:20* ya baro gidan ya nufi gida, Khadija har sun kwanta ita da Bilal ya shigo, ko da ya ga babu wuta a falon sai ya wuce falon shi kai tsaye, Haseenah na ganin shi ta d'ago kai ta kalle shi, ba fara'a ko sakin fuska tace "Sannu da zuwa."
Sai da ya kamo hannun ta tayi tsaye ya rumgume ta yace "Sannu da gida."
Kamar ba ta son magana ta amsa da "Yawwa."
Kallon fuskarta ya yi yace "Ki yi hak'uri na barki ke kad'ai ko? Ina can gida tare da yaran nan su na ta min shirme."
Cikin shagwab'a tace "Na ji to, yanzu dai mu je ka yi wanka sai ka zo ka ci abinci."
Rimgume ta ya yi yace "Wallahi kamar kinsan kam na d'ebo yunwa, muje ki kintsani yanda ya kamata."
D'akin shi su ka nufa, bayan ta taya shi wanka ya canza kaya su ka fito, ya na jan kujera ya kalle ta yace "Da alama su Bilal har sun kwanta ko?"
Kallon shi ta yi tace "Eh to ban sani ba dai, amma tun da na ji shiru babu hayaniyar tv na ke tunanin haka."
Ba tare da ya kalle ta ba yace "Haseenah me zai hana idan ba na nan ki dinga zuwa wajen su ki na zama ku na hira? Ina ga hakan ai zaifi ko? Tunda daga ke sai sune a gidan, kuma sune abokan rayuwar ki a yanzun."
Ta na aza marar tuwo a farantin ya kalle ta, bai kai ga jin amsarta ba yace "Haseenah tuwo ki ka dafa?"
Kallon shi ta yi tace "Eh, da matsala ne?"
Ya na ci gaba da kallonta yace "Khadija ta ga ki na aikin nan?"
Sam Haseenah ta ma manta da abin da Khadija ta fad'a mata, sai kawai tace "Eh, me ya faru?"
Da wani irin kallo yace "Kuma ba ta fad'a mi ki komai a game da hakan?"
"A'a, wai me ya faru ne?" Ta fad'a cike da k'aguwa, a hankali yace "Shikenan kawai, zo zauna nan."
Janyota ya yi ya zaunar da ita akan cinyar shi ya na kallon fuskarta yace "Haseenah, ki yi hak'uri kinji, ina ganin laifi na ne da har mu ka yi soyayya da kai ba tare da kinsan abubuwa da dama a kai na ba, kuma hakan ya samo asaline saboda ba mu jima tare ba, sannan ni mutum ne da bai cika fad'an abin da ya shafe shi ba, amma a gaskiya ni ba na cin tuwo da dare, ba kuma shi kad'ai ba, akwai abin da ma kwata-kwata ba na cinsu kamar wake da nasan sa, sannan kinga shinkafa ma ban cika son ta ba haka, sannan kifi ma ba na cin shi da dare, wannan shine."
Bushewa ta yi da dariya ta sauka daga cinyar shi taja kujera mai fuskantar shi, da k'yar ta tsayar da dariyar tace "Miji na, ka na d'an africa, a africar ma a niger, kuma ka ce ba ka son shinkafa, lallai ka na jin dad'in ka."
Ganin ta mayar da abun kamar wasa ya sa ya d'an gimtse fuska yace "Ni dai ban son ta, na fad'a mi ki ne dan ki kiyaye."
Ita ma had'e fuska ta yi tace "To yanzu tuwon nan fa ya zanyi da shi?"
Shima dariya ya yi yace "Ku ba kun ci ba? Kawai ki samar min wani abu na ci."
Cike da kasala tace "Kamar me fa?"
"Ko taliyarku ta yara ki d'ora min." Yanda ya yi maganar da zolaya ya sa ta taso ta na dariya ta rumgume shi ta baya ta na fad'in "Yanzu ni yarinya ce a wurin ka?"
"Sosai ma." Ya fad'a ya na dariya, cikin kunne ta rad'a ma sa "Ni kam banyi tsammanin za ka iya kira na da yarinya ba."
D'ago kai ya yi ya kalle ta yace "Shekarar ki nawa ne wai dan Allah?"
Saida ta waina idon ta tace "Sha takwas."
Da sauri ya mik'e tsaye ya na k'are mata kallo, har zagayata ya ke ya na kallonta, tab'e baki ya yi yace "Lallai ina da sa'a, gani tsoho amma sai Allah ya dinga had'a ni da yara yan sha takwas shakaf."
Juyawa ta yi ta nufi madafar, d'ora tukunya ta yi duk da ba wani sanin kan indomie ta yi ba, amma dai wani lokaci ta d'an dafawa yayan ta *Mubarak*, yanzun ma yanda take yi a gida haka ta dafa, sai dai da ta zuba a faranti sai ta ga abun bai birge ta ba, dan indomien duk ta dahu sosai kamar za ta narke, to amma ya ta iya haka ta d'auko ta kawo mi shi, dakewa kawai ya yi tamaza ya d'ura indomien nan, amma bai ci sosai ba, ya na gamawa ya mik'e yace "Zan lek'a na ga su Bilal."
Kallon shi ta hi ta kalli farantin indomien, k'ala ba tace masa ba ta tashi ita ma ta wuce d'akin ta dan shirin bacci, shi ma ficewa ya yi bai kula ta ba, d'akin Bilal ya fara shiga, sai da ya k'arewa yaron kallo ya shafi kansa kafin ya fito, da sallama ya shiga d'akin amma shiru, kujerar gaban madubi ya janyo ya zauna bayan ta ya daddab'a ta, bud'a ido ta yi ta tashi zaune ta janyo gilashin ta ta sanya, kallon shi ta yi shi kuma yace "Hajia Khadija ki na lokaci, yanzu har an daina sona ta yanda ba'a jira aga na shigo lafiya ko akasin haka."
Murmushi ta yi tace "Abban Bilal ma ya na lokaci, tun da har zai shigo gidan nan amma ya kasa neman mu."
Da mamaki ya bita da kallo ita kuma tace "K'warai, na ji shigowarka ai."
"Hum." Ya fad'a ya yi shiru, ita kuma tace "Ka daina mantawa, yanzu mu biyu ne da hakk'in kula da kai, in da lokacin kwana na ne zan iya jiran ka har gari ya waye."
"Amma in ba kwananki bane kuma ko oho ko?"
Wani takaici ne ya taso ma Haseenah wacce ke wahalar tuk'a tuwon, k'ala ba tace mata ba sai Khadija ce ta sake cewa "Sai dai kuma mijinki baya cin tuwo da dare, ko bai tab'a fad'a mi ki ba? Musamman ma na ga wake ne ki ke miyar da shi, kuma ba ya cin wake ko kad'an, amma za ki iya had'a ma sa wani sassauk'an abun, mu sai mu ci tuwon dan munyi kewar shi."
Ran Haseenah ne ya yi mugun b'aci tace "Kutumar uba, baiwar Allah na fad'a mi ki ina neman taimakon ki ne? Kinga Khadija, gaskiya ba na son haka, mijin ki ba ya cin tuwo a lokacin da ke kad'ai ce cikin gidan, yanzu kuma Haseenah ta shigo, dan haka ki barni na yi rayuwa ta mana, ki barni ni ma na kafa salon nawa tarihin a gidan nan kuma a zuciyar miji na, amma ba ki dinga min shishigi ba, ba lallai dan kin saba mi shi da saka kalar fari ba ki ce nima wannan kalar ki ke so na saka mi shi, ki barni na yi abin da ya dace, nan gidan miji na ne."
Wani warrr Khadija ta yi da manyan idon ta kafin ta sa hannun ta tana fifita da shi tana fad'in "Wash Allah, zafi."
Kallon Haseenah ta yi da murmushi tace "Sannu mai miji, Allah ya bar k'auna."
"Ameen." Ta fad'a har da zaburowa, fita Khadija ta yi, tsaf Haseenah ta gama tuwonta ta mulmule, da kan ta ta kawowa Khadija na su tuwon, ko k'ala ita ma ba tace da ita ba har ta fita, Uwani ce ta tashi tafiya tace "Uwani d'auko wani kwano a d'akin can ki tafi da abincin nan."
D'aya d'akin ta shiga da ke da tarkacai abubuwan buk'ata ta fito, juye tuwon ta yi ta tafi da shi bayan sun yi sallama, Bilal ne ya shigo gida shi kad'ai da takarda a hannun shi, rumgume maman shi ya yi ita kuma tace "Wa ya dawo da kai ne?"
" *Bilyaminu* ne Abba ya tura ya d'auko ni, Mummy karb'i wannan." Ya fad'a bata takardar, ta na dubawa tace "Har wata ya k'are kenan?"
Kai kaxai ya d'aga mata, ba shi ta yi tace "To ka aje wurinka idan Abbanka ya dawo sai ka ba shi, amma ni zan iya mantawa."
A tare su ka tashi ita ta shiga d'akin ta saboda magriba ta gabato sosai, kaya kawai Bilal ya canza ya wuce masallaci, Khadija ma na idar da sallah ta shiga wanka, shiryawa ta yi sosai kafin ta lalabi gilashin ta na jiya da Usman ya cilla kan gadon, dan tun jiya bata waiwaye shi, shi ta saka dan ya fi mata kyau sannan ta fito, zaune suke ita da Bilal su na kallo su na hirar su, bayan sallah isha'i ko da su ka yi sallah abincin ranar da Uwani ta kwashe mata a kula ta d'auko ta zuba, tare su ka ci hankali kwance su ka k'oshi, hamdala su ka yi kafin su ka tashi kamar ba su ci ba.
Kamar yanda ya yi alk'awarin komawa gida haka ya wuce, ya kuma samu su Kabir Mannir da Nura, hakan ya sa suka bud'a babin hira su ka dinga yi, Haseenah da ke jiran shigowar shi taga shiru sai da ta kai ga kira, amma sai ya d'aga yace ya na gida zai zo ba da jimawa ba, amma fa bai zo d'in ba saboda suna tattaunawa da ahalin shi, sai wajen *22:20* ya baro gidan ya nufi gida, Khadija har sun kwanta ita da Bilal ya shigo, ko da ya ga babu wuta a falon sai ya wuce falon shi kai tsaye, Haseenah na ganin shi ta d'ago kai ta kalle shi, ba fara'a ko sakin fuska tace "Sannu da zuwa."
Sai da ya kamo hannun ta tayi tsaye ya rumgume ta yace "Sannu da gida."
Kamar ba ta son magana ta amsa da "Yawwa."
Kallon fuskarta ya yi yace "Ki yi hak'uri na barki ke kad'ai ko? Ina can gida tare da yaran nan su na ta min shirme."
Cikin shagwab'a tace "Na ji to, yanzu dai mu je ka yi wanka sai ka zo ka ci abinci."
Rimgume ta ya yi yace "Wallahi kamar kinsan kam na d'ebo yunwa, muje ki kintsani yanda ya kamata."
D'akin shi su ka nufa, bayan ta taya shi wanka ya canza kaya su ka fito, ya na jan kujera ya kalle ta yace "Da alama su Bilal har sun kwanta ko?"
Kallon shi ta yi tace "Eh to ban sani ba dai, amma tun da na ji shiru babu hayaniyar tv na ke tunanin haka."
Ba tare da ya kalle ta ba yace "Haseenah me zai hana idan ba na nan ki dinga zuwa wajen su ki na zama ku na hira? Ina ga hakan ai zaifi ko? Tunda daga ke sai sune a gidan, kuma sune abokan rayuwar ki a yanzun."
Ta na aza marar tuwo a farantin ya kalle ta, bai kai ga jin amsarta ba yace "Haseenah tuwo ki ka dafa?"
Kallon shi ta yi tace "Eh, da matsala ne?"
Ya na ci gaba da kallonta yace "Khadija ta ga ki na aikin nan?"
Sam Haseenah ta ma manta da abin da Khadija ta fad'a mata, sai kawai tace "Eh, me ya faru?"
Da wani irin kallo yace "Kuma ba ta fad'a mi ki komai a game da hakan?"
"A'a, wai me ya faru ne?" Ta fad'a cike da k'aguwa, a hankali yace "Shikenan kawai, zo zauna nan."
Janyota ya yi ya zaunar da ita akan cinyar shi ya na kallon fuskarta yace "Haseenah, ki yi hak'uri kinji, ina ganin laifi na ne da har mu ka yi soyayya da kai ba tare da kinsan abubuwa da dama a kai na ba, kuma hakan ya samo asaline saboda ba mu jima tare ba, sannan ni mutum ne da bai cika fad'an abin da ya shafe shi ba, amma a gaskiya ni ba na cin tuwo da dare, ba kuma shi kad'ai ba, akwai abin da ma kwata-kwata ba na cinsu kamar wake da nasan sa, sannan kinga shinkafa ma ban cika son ta ba haka, sannan kifi ma ba na cin shi da dare, wannan shine."
Bushewa ta yi da dariya ta sauka daga cinyar shi taja kujera mai fuskantar shi, da k'yar ta tsayar da dariyar tace "Miji na, ka na d'an africa, a africar ma a niger, kuma ka ce ba ka son shinkafa, lallai ka na jin dad'in ka."
Ganin ta mayar da abun kamar wasa ya sa ya d'an gimtse fuska yace "Ni dai ban son ta, na fad'a mi ki ne dan ki kiyaye."
Ita ma had'e fuska ta yi tace "To yanzu tuwon nan fa ya zanyi da shi?"
Shima dariya ya yi yace "Ku ba kun ci ba? Kawai ki samar min wani abu na ci."
Cike da kasala tace "Kamar me fa?"
"Ko taliyarku ta yara ki d'ora min." Yanda ya yi maganar da zolaya ya sa ta taso ta na dariya ta rumgume shi ta baya ta na fad'in "Yanzu ni yarinya ce a wurin ka?"
"Sosai ma." Ya fad'a ya na dariya, cikin kunne ta rad'a ma sa "Ni kam banyi tsammanin za ka iya kira na da yarinya ba."
D'ago kai ya yi ya kalle ta yace "Shekarar ki nawa ne wai dan Allah?"
Saida ta waina idon ta tace "Sha takwas."
Da sauri ya mik'e tsaye ya na k'are mata kallo, har zagayata ya ke ya na kallonta, tab'e baki ya yi yace "Lallai ina da sa'a, gani tsoho amma sai Allah ya dinga had'a ni da yara yan sha takwas shakaf."
Juyawa ta yi ta nufi madafar, d'ora tukunya ta yi duk da ba wani sanin kan indomie ta yi ba, amma dai wani lokaci ta d'an dafawa yayan ta *Mubarak*, yanzun ma yanda take yi a gida haka ta dafa, sai dai da ta zuba a faranti sai ta ga abun bai birge ta ba, dan indomien duk ta dahu sosai kamar za ta narke, to amma ya ta iya haka ta d'auko ta kawo mi shi, dakewa kawai ya yi tamaza ya d'ura indomien nan, amma bai ci sosai ba, ya na gamawa ya mik'e yace "Zan lek'a na ga su Bilal."
Kallon shi ta hi ta kalli farantin indomien, k'ala ba tace masa ba ta tashi ita ma ta wuce d'akin ta dan shirin bacci, shi ma ficewa ya yi bai kula ta ba, d'akin Bilal ya fara shiga, sai da ya k'arewa yaron kallo ya shafi kansa kafin ya fito, da sallama ya shiga d'akin amma shiru, kujerar gaban madubi ya janyo ya zauna bayan ta ya daddab'a ta, bud'a ido ta yi ta tashi zaune ta janyo gilashin ta ta sanya, kallon shi ta yi shi kuma yace "Hajia Khadija ki na lokaci, yanzu har an daina sona ta yanda ba'a jira aga na shigo lafiya ko akasin haka."
Murmushi ta yi tace "Abban Bilal ma ya na lokaci, tun da har zai shigo gidan nan amma ya kasa neman mu."
Da mamaki ya bita da kallo ita kuma tace "K'warai, na ji shigowarka ai."
"Hum." Ya fad'a ya yi shiru, ita kuma tace "Ka daina mantawa, yanzu mu biyu ne da hakk'in kula da kai, in da lokacin kwana na ne zan iya jiran ka har gari ya waye."
"Amma in ba kwananki bane kuma ko oho ko?"