Sashe 30
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta na ganin Haseenah ce sai kuwa ta cakume ta da kokawa,😂 (Allah ya kyauta, mata mu na bawa kan mu wahala wallahi, wata sai ki ga ma mijin da su ke fad'a akai kamar kalangu, amma haka za su yi ta bala'i a kan shi maimakon kwantar mi shi da hankali), k'awayen Haseenah na ganin haka su ka shigarwa k'awar su saboda tuni aka aza Haseenah ga k'asa ana shirgarta, Uwani na ganin haka ta fita da gudu zuwa gidan mak'wabtan da Khadija ke abun arzik'i da su, Bilal kam wayar shi ya d'auka k'arama ya kira mahaifin shi ya fad'a mi shi, mai gadi na daga gefe ya na dan Allah ayi hak'uri amma ko jin shi ba su yi, jin zafin dukan da k'awayen ta ke mata ne ya sa Khadija finciko wata daga cikin k'awayen ta had'a su ta taushe, wuri fa ya kaure ana ta bawa hammata iska sai ga mak'wabtan sun shigo, da gudu su ka k'arasa su ka d'aga Khadija daga kan Haseenah da *Farida*, anyi jina jina sosai kamar filin yak'i, cecekuce aka shiga yi tare da aikawa juna ashar, Khadija na k'ok'arin k'wacewa ta koma ga Haseenah amma an rik'e ta, su na haka fa gida ya kaure Usman ya baro mota waje ya kutso ciki, ganin su duk a yamutse ya sa ya tsaya ya sa hannu ya rufe fuskar shi, ya d'an jima a haka kafin ya k'araso wajen, k'awayen Haseenah ya fara kallo yace "Yamma ta yi, za ku iya tafiya."
Cikin sanyin jiki duka aka watse aka bar shi da matan shi, har Uwani ma ba ta tsaya ba tafiyar ta ta yi gida, falon shi ya nufa ya na fad'in "Ku same ni a falo na."
😂 *Aiki ya samu Usmanu, yanzu ma ka fara cewa a biyo ka falo ai*
Su na shiga daga zaman da Khadija ta yi zai tabbatar maka ba arzik'i, cikin b'acin rai ya yi tsaye yace "Me ku ka zama? Me ku ke son mayar min da gida? Wannan wane irin dabbanci ne?"
Tsaye Khadija ta mik'e tace "Dakata malam, dakata min, a sani na irin haka ba ta tab'a faruwa ba, to akan me sai yanzu haka za ta faru? Akan me ye amaryar ka za ta nemi ta raina ni? Ni sa'ar ta ce? Ko kai ka ce ta raina ni? Saboda rashin sanin darajar mutane har ta bud'e baki tace min wai mi ye anfanin Bilal a gidan nan, bayan kin fad'a ma sa bai da anfanin komai sai dai a dafa a ba shi ya ci, to uwar ki ce ke dafa mi shi ya na ci? To ki kama bakin ki ki dinga sanin me za ki fad'a."
Mayar da kallon ta ta yi ga Usman tace "Kai kuma dan Allah idan kun shiga ciki ka yi k'ok'ari ka sanar da ita mahimmancin d'an ka gare ka da anfanin shi gare ka, ni ba buk'atar sai na fad'a mata anfanin d'ana gare ni, amma ka fad'a mata shi kad'ai gare ni, dan haka bana had'a yaro na da kowa da kuma komai a duniya, a matsayi na na uwa kuma zan iya yin komai saboda shi."
Ta na gama fad'a ta fice ta bar su, juyowa Usman ya yi ya na kallon Haseenah, a hankali ya furta "Haseenah, ki na tambayar anfanin haihuwar Bilal a gidan nan? Ni fa uban sa ne, duk fafutukar da na ke yi saboda shine na ke yi, amma ki bud'e baki ki ce me ye anfanin haihuwar shi."
Girgiza kai ya yi cike da damuwa ya dafe k'ugu da hannu d'aya yace "Maganar gaskiya Haseenah ba na so na nuna mi ki b'acin rai na, amma ki sani ko Khadija ba na buran b'acin ran ta bare kuma Bilal da ya fito daga tsatso na, ina k'aunar iyalin nan nawa matuk'a, su ne ni, su suka mayar da ni mutum da har ki ka so ni a haka, ki kiyaye furta abin da zai iya ja mi ki matsala, sannan k'awayen nan naki in har kinsan zuwan su gidan nan ba alkairi bane, to zaifi kyau ki fad'awa kowace ba na son sake ganin k'afar su a gidan nan."
Ya na gama fad'a shima ya fita ya barta, kallon shi ta yi a matuk'ar hassale ta mik'e ta nufi madafa, kashe wutar ta yi ta gyara abin da ya sawak'a ta koma d'akin ta, wayar ta ta d'auka ta kira Mariya ta fad'a mata duk abin da ya faru, nan dai ta girmama abin tare da k'ara tunzurata sannan tace ta bar komai a hannun ta, da haka su ka yi sallama ta yi wanka ta shirya, sai dai ba wata kwalliya ta yi ba dan duk jikin ta ma ciwo ya ke na tsinannan dukan da ta sha.
***************
Bayan sallah isha'i Khadija na zaune tare da Bilal a falo Nura ya shigo gidan da rahar shi kamar yanda ya saba, tun daga bakin k'ofa ya ke fad'in "Dije, Dije ba ta jina ne? Na shigo amma ki kasa tarba ta tun daga k'ofar gida."
Ganin Khadija zaune ta yi shiru sai kallon shi take ya sa yace "Ah lallai ma matar nan, ashe ki na jina na ke ta kwaroronton nan amma ki ka share ni? Ko dan yau ban baki kud'in cefanai ba?"
Khadija da har yanzu ran ta a b'ace ya ke k'ala ba tace mi shi ba, Bilal ne ya tarbe shi da murna sosai, tare su ka zauna ya na kallon Khadija ya kalli Bilal yace "Yaro waya tab'a min maman ka ne haka ta ke ta kumbura?"
Shiru Bilal ya yi ya na kallon ta, a hankali ta maido kallon ta gare shi tace "Sannu ko."
"Ai na ba za ki yi magana ba, da na tabbatar mi ki mijin gaske ne ni."
"Ya su Hajia?" Ta fad'a ba yabo ba fallasa, saida ya sauke ajiyar zuciya yace "Lafiyar su k'alau, kai kawo min lemu mai sanyi na sha." Ya k'arashe da kallon Bilal.
D'auko masa ya yi ya kawo ya ba shi ya amsa, sai da ya fara sha ya kalli Bilal yace "Ina auntyn ka take?"
"Ta na d'akin ta." Cewar Bilal ya na kallon k'ofar falon mahaifin shi, tura shi Nura ya yi yace "Je ka ce ina kiran ta, ka ce ta fito ta kwashi gaisuwa tare da albarka mai gida ya dawo."
Da dariya Bilal ya nufi k'ofar falon mahaifin shi, cikin daka tsawa Khadija tace "Kai Bilal, ka na da hankali kuwa? Dallah malam dawo ka zauna min nan."
Da mamaki duka su ka kalle ta, in da ta nuna masa da hannu ya zauna hakan ya bata damar kama kunnensa tace "Wallahi ka sake zuwa in da matar can take sai na b'ata ma ka rai, kaji ko?"
Yanda ta d'aga murya tare da k'ara murd'e kunnen shi ya sa yace "Na ji Mummy, ki yi hak'uri ba zan k'ara ba."
Nura da ke kallon ikon Allah ne yace "Khadija me ya sa za ki ma sa haka? Naga da ke da ita ai duk d'aya ne, iyayen shi ne ku."
Tsaye khadija ta mik'e tace "Dakata min Nura, ni daban ita daban, wallahi duk yanda za ta kyautata mi shi ba za ta tab'a zama kamar ni uwar shi ba, dan haka kar ka sake had'a min yaro da wata banzar mata da ba ta san darajar shi ba, idan ka zo gani na ne na gode, idan wajen ta ka zo ka shiga ta na ciki."
Juyawa ta yi ta shige uwar d'akin ta, mamaki ne ya kusa kashe Nura, dan shi dai a sanin shi wani ma ba su tab'a samun matsala da Khadija ba bare kuma dangin mijin ta, cikin sanyin jiki ya aje robar lemun hannun shi ya mik'e zuciyar shi na tunanin wane irin kishi ne da Khadija haka? Bilal ne ya mik'e yace "Tonton (uncle) Nura zan bika wajen Hajia."
Shafa kan shi ya yi yace "To ka fara fad'awa Maman ka, idan ta amince sai ka d'auko kayan ka mu tafi."
"To." Ya fad'a ya juya da k'arfi ya shiga d'akin, zaune ya same ta yace "Mummy, tonton Nura yace na d'auko kaya na mu tafi gida wajen Hajia."
Cikin jin haushi tace "Babu in da za ka je, ka wuce d'akin ka ka kwanta ko kuma ka yi karatu."
Hawaye ne su ka cika idon shi saboda shi dai haka ba ta tab'a faruwa tsakanin shi da maman shi ba sai yau, juyawa ya yi zai fita sai taji ya bata tausayi, amma kuma hushin ta da duk dangin Usman da suke murnar an mata kishiya, a hankali tace "Bilal."
Juyowa ya yi ya dawo ya tsaya, hannun shi ta kama tace "Ka had'a kayan ka zan kira tonton Naseer ya zo yanzu ya d'auke ka, hakan ya yi?"
Ba tare da sakin fuska ba ya d'aga kai alamar eh, fita ya yi Nura na tsaye yace "To ya? Za mu wuce ne?"
Kamar zai fashe da kuka yace "Mummy ta hana."
Ji ya yi kafin yace "Shikenan kar ka damu, ai gobe juma'a, watak'ila ku tafi gidan tare da Abban ka."
Shiru bai ce komai ba har ya fita daga gidan ba tare da ma ya shiga wajen Haseenah ba, ta na kiran Naseer kam dama bai shiga gida ba, dan haka ya taho d'aukar shi, sai dai lokacin Usman ya shigo gidan, sun gaisa kamar yanda su ka saba tare da wasa da dariya, amma har Khadija ta had'awa Bilal kayan shi su ka tafi babu fara'a a tare da ita bare ta yi magana, a tak'aice dai haka duka gidan su ka gudanar da daren su babu armashi a ciki, dan Usman ya nunawa Haseenah kuskuren ta ma ko abincin ta bai ci ba, haka ma a d'aki da suka kwanta juya mata baya ya yi, dan in har za ta iya cin zarafin d'an shi har haka to fa akwai yiwuwar ya nuna mata ba'a mi shi wasa da gudan jini.
Cikin sanyin jiki duka aka watse aka bar shi da matan shi, har Uwani ma ba ta tsaya ba tafiyar ta ta yi gida, falon shi ya nufa ya na fad'in "Ku same ni a falo na."
😂 *Aiki ya samu Usmanu, yanzu ma ka fara cewa a biyo ka falo ai*
Su na shiga daga zaman da Khadija ta yi zai tabbatar maka ba arzik'i, cikin b'acin rai ya yi tsaye yace "Me ku ka zama? Me ku ke son mayar min da gida? Wannan wane irin dabbanci ne?"
Tsaye Khadija ta mik'e tace "Dakata malam, dakata min, a sani na irin haka ba ta tab'a faruwa ba, to akan me sai yanzu haka za ta faru? Akan me ye amaryar ka za ta nemi ta raina ni? Ni sa'ar ta ce? Ko kai ka ce ta raina ni? Saboda rashin sanin darajar mutane har ta bud'e baki tace min wai mi ye anfanin Bilal a gidan nan, bayan kin fad'a ma sa bai da anfanin komai sai dai a dafa a ba shi ya ci, to uwar ki ce ke dafa mi shi ya na ci? To ki kama bakin ki ki dinga sanin me za ki fad'a."
Mayar da kallon ta ta yi ga Usman tace "Kai kuma dan Allah idan kun shiga ciki ka yi k'ok'ari ka sanar da ita mahimmancin d'an ka gare ka da anfanin shi gare ka, ni ba buk'atar sai na fad'a mata anfanin d'ana gare ni, amma ka fad'a mata shi kad'ai gare ni, dan haka bana had'a yaro na da kowa da kuma komai a duniya, a matsayi na na uwa kuma zan iya yin komai saboda shi."
Ta na gama fad'a ta fice ta bar su, juyowa Usman ya yi ya na kallon Haseenah, a hankali ya furta "Haseenah, ki na tambayar anfanin haihuwar Bilal a gidan nan? Ni fa uban sa ne, duk fafutukar da na ke yi saboda shine na ke yi, amma ki bud'e baki ki ce me ye anfanin haihuwar shi."
Girgiza kai ya yi cike da damuwa ya dafe k'ugu da hannu d'aya yace "Maganar gaskiya Haseenah ba na so na nuna mi ki b'acin rai na, amma ki sani ko Khadija ba na buran b'acin ran ta bare kuma Bilal da ya fito daga tsatso na, ina k'aunar iyalin nan nawa matuk'a, su ne ni, su suka mayar da ni mutum da har ki ka so ni a haka, ki kiyaye furta abin da zai iya ja mi ki matsala, sannan k'awayen nan naki in har kinsan zuwan su gidan nan ba alkairi bane, to zaifi kyau ki fad'awa kowace ba na son sake ganin k'afar su a gidan nan."
Ya na gama fad'a shima ya fita ya barta, kallon shi ta yi a matuk'ar hassale ta mik'e ta nufi madafa, kashe wutar ta yi ta gyara abin da ya sawak'a ta koma d'akin ta, wayar ta ta d'auka ta kira Mariya ta fad'a mata duk abin da ya faru, nan dai ta girmama abin tare da k'ara tunzurata sannan tace ta bar komai a hannun ta, da haka su ka yi sallama ta yi wanka ta shirya, sai dai ba wata kwalliya ta yi ba dan duk jikin ta ma ciwo ya ke na tsinannan dukan da ta sha.
***************
Bayan sallah isha'i Khadija na zaune tare da Bilal a falo Nura ya shigo gidan da rahar shi kamar yanda ya saba, tun daga bakin k'ofa ya ke fad'in "Dije, Dije ba ta jina ne? Na shigo amma ki kasa tarba ta tun daga k'ofar gida."
Ganin Khadija zaune ta yi shiru sai kallon shi take ya sa yace "Ah lallai ma matar nan, ashe ki na jina na ke ta kwaroronton nan amma ki ka share ni? Ko dan yau ban baki kud'in cefanai ba?"
Khadija da har yanzu ran ta a b'ace ya ke k'ala ba tace mi shi ba, Bilal ne ya tarbe shi da murna sosai, tare su ka zauna ya na kallon Khadija ya kalli Bilal yace "Yaro waya tab'a min maman ka ne haka ta ke ta kumbura?"
Shiru Bilal ya yi ya na kallon ta, a hankali ta maido kallon ta gare shi tace "Sannu ko."
"Ai na ba za ki yi magana ba, da na tabbatar mi ki mijin gaske ne ni."
"Ya su Hajia?" Ta fad'a ba yabo ba fallasa, saida ya sauke ajiyar zuciya yace "Lafiyar su k'alau, kai kawo min lemu mai sanyi na sha." Ya k'arashe da kallon Bilal.
D'auko masa ya yi ya kawo ya ba shi ya amsa, sai da ya fara sha ya kalli Bilal yace "Ina auntyn ka take?"
"Ta na d'akin ta." Cewar Bilal ya na kallon k'ofar falon mahaifin shi, tura shi Nura ya yi yace "Je ka ce ina kiran ta, ka ce ta fito ta kwashi gaisuwa tare da albarka mai gida ya dawo."
Da dariya Bilal ya nufi k'ofar falon mahaifin shi, cikin daka tsawa Khadija tace "Kai Bilal, ka na da hankali kuwa? Dallah malam dawo ka zauna min nan."
Da mamaki duka su ka kalle ta, in da ta nuna masa da hannu ya zauna hakan ya bata damar kama kunnensa tace "Wallahi ka sake zuwa in da matar can take sai na b'ata ma ka rai, kaji ko?"
Yanda ta d'aga murya tare da k'ara murd'e kunnen shi ya sa yace "Na ji Mummy, ki yi hak'uri ba zan k'ara ba."
Nura da ke kallon ikon Allah ne yace "Khadija me ya sa za ki ma sa haka? Naga da ke da ita ai duk d'aya ne, iyayen shi ne ku."
Tsaye khadija ta mik'e tace "Dakata min Nura, ni daban ita daban, wallahi duk yanda za ta kyautata mi shi ba za ta tab'a zama kamar ni uwar shi ba, dan haka kar ka sake had'a min yaro da wata banzar mata da ba ta san darajar shi ba, idan ka zo gani na ne na gode, idan wajen ta ka zo ka shiga ta na ciki."
Juyawa ta yi ta shige uwar d'akin ta, mamaki ne ya kusa kashe Nura, dan shi dai a sanin shi wani ma ba su tab'a samun matsala da Khadija ba bare kuma dangin mijin ta, cikin sanyin jiki ya aje robar lemun hannun shi ya mik'e zuciyar shi na tunanin wane irin kishi ne da Khadija haka? Bilal ne ya mik'e yace "Tonton (uncle) Nura zan bika wajen Hajia."
Shafa kan shi ya yi yace "To ka fara fad'awa Maman ka, idan ta amince sai ka d'auko kayan ka mu tafi."
"To." Ya fad'a ya juya da k'arfi ya shiga d'akin, zaune ya same ta yace "Mummy, tonton Nura yace na d'auko kaya na mu tafi gida wajen Hajia."
Cikin jin haushi tace "Babu in da za ka je, ka wuce d'akin ka ka kwanta ko kuma ka yi karatu."
Hawaye ne su ka cika idon shi saboda shi dai haka ba ta tab'a faruwa tsakanin shi da maman shi ba sai yau, juyawa ya yi zai fita sai taji ya bata tausayi, amma kuma hushin ta da duk dangin Usman da suke murnar an mata kishiya, a hankali tace "Bilal."
Juyowa ya yi ya dawo ya tsaya, hannun shi ta kama tace "Ka had'a kayan ka zan kira tonton Naseer ya zo yanzu ya d'auke ka, hakan ya yi?"
Ba tare da sakin fuska ba ya d'aga kai alamar eh, fita ya yi Nura na tsaye yace "To ya? Za mu wuce ne?"
Kamar zai fashe da kuka yace "Mummy ta hana."
Ji ya yi kafin yace "Shikenan kar ka damu, ai gobe juma'a, watak'ila ku tafi gidan tare da Abban ka."
Shiru bai ce komai ba har ya fita daga gidan ba tare da ma ya shiga wajen Haseenah ba, ta na kiran Naseer kam dama bai shiga gida ba, dan haka ya taho d'aukar shi, sai dai lokacin Usman ya shigo gidan, sun gaisa kamar yanda su ka saba tare da wasa da dariya, amma har Khadija ta had'awa Bilal kayan shi su ka tafi babu fara'a a tare da ita bare ta yi magana, a tak'aice dai haka duka gidan su ka gudanar da daren su babu armashi a ciki, dan Usman ya nunawa Haseenah kuskuren ta ma ko abincin ta bai ci ba, haka ma a d'aki da suka kwanta juya mata baya ya yi, dan in har za ta iya cin zarafin d'an shi har haka to fa akwai yiwuwar ya nuna mata ba'a mi shi wasa da gudan jini.