← Book details Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 86

Sashe 41

Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ba wani shiri ta yi ba kuma tare da Bilal suka ci abinci, sai kusan goma ya shigo gidan, kasancewar Bilal baiyi bacci ba ya sa suka zauna falon shi suna kallo, abinci ya ci kafin ya shiga yi wa Haseenah saida safe, da k'yar ya baro d'akin ta dan baya son rabuwa da ita, Khadija ma d'aki ta raka Bilal ya kwanta kafin ta saka kayan bacci ta nufi d'akin shi, ta na kwance ya shigo ya wuce ban d'aki, ya d'an jima kafin ya fito ta na kallo har ya canza kaya, kashe wuta ya yi kafin ya kwanta gefen ta kuma nesa da ita ya juya mata baya, ta na ganin haka ta d'auki gilashin ta gefen ta saka ta janyo wata ma'ajiya ta d'auki Qur'ani ta fara karatu, Usman na so ya yi bacci amma fitinar sha'awar da ta taso mi shi saboda wasan da su ka yi da Haseenah ya sa ya kasa baccin, a k'alla awa d'aya su na haka ita ta na karatu shi ya na juye juye da matsar mara, a zabure ya juyo gefen Khadija ya rarumota ya danna bakin shi cikin nata, cikin dubara ta samu ta aje Qur'anin hannun ta...

Tabbas sihiri gaskiya ne kuma ya na iya kama kowa, Usman da ke bala'in jin dad'in kasancewa da Khadija a kowane lokaci, matar da take gamsar da shi fiye da tunanin mai tunani, amma yau ya kusanceta ba dan ya na so ba sai dan sauke abin da ke damun shi, da kuma *tsananin rabo*, da k'yar ya iya hak'ura ya kai bakin gab'a saboda ji ya ke kamar a cikin yaji ne ya ke link'aya da kayan shi, ta wani b'angaren kuma kamar a cikin tab'o ne ya jefa ta haka ya ke ji, babu wani dad'i da ya ji bare ayi maganar gamsuwa, gaba d'aya jin ta ya yi a k'afe babu ruwa kamar tabkin da ya tsotse, wanka ya shiga ya fito ya sake kwantawa ya juya mata baya, tsakin da ya yi ne ya sa Khadija juyawa ta kalle shi, tashi ta yi ita ma ta yi wanka ta dawo ta ci gaba da karatun ta.

Ana kiran sallah farko ya fita, ko Bilal bai waiwaya ba yau ya tafi masallaci, ya na dawowa kuma wajen Haseenah ya wuce, ko tashi ba ta yi ba ita kam ta na bacci, rufe d'akin ya yi ya zame kayan jikin shi a hankali ya shiga cikin zanin rufar, kamar a mafarki Haseenah ta ji wata wawar cakuma da ya wa k'irjin ta d'aya da hannu d'aya a baki, ta so raba kan ta da shi amma bai bata damar hakan ba saboda rik'on gaske ya mata ba kad'an ba, ya na jefa k'wallon sa a raga ya sauke wata arniyar ajiyar zuciya, kwance ya yi akan k'irjin ta ya yi shiru dan abin da ya ke ji ma kamar zai tafi da numfashin shi, saida ya d'auki kusan minti biyu a haka kafin ya fara aiki da gaske, irin sambatu da surutan da ya ke da ihu kamar wani zararre...Hum yau fa suruki na kad'an b'ata min rai gaskiya,😎 ka kiyaye ba na son haka.

Kusan awa d'aya ya d'auka kafin ya rabu da ita ya shiga ya yi wanka ya fito, kayan shi ya mayar a jikin kafin ya kalli Haseenah da ta had'a kai da gwiwa ta na kallon tace "Yanzu abin da ka yi ka kyauta? Yau fa ba kwana ne bane, me ka ke so a kalle mu dan Allah?"

Cike da nuna rashin damuwa yace "Ke ni dallah rabu dani, to zaunawa zanyi na kashe kai na bayan ina da maganin a cikin gida na, can babu abin da ke akwai sai kayan haushi da k'yama, to ya ki ke so na yi?"

Wani kallo ta masa tace "Ka na so ka ce babu abin da ka ke ji acan sai anan?"

Da sauri ya matso kusan ta ya rik'e hannun ta yace "Dan Allah kar ki fad'awa kowa maganar nan, amma wallahi matar can ba ta da dad'i, yanda ki ka san mutum ya fad'a a kwata haka take, ita fa ko miya marar kayan d'and'ano ta fita armashi."

Ba ta san lokacin da ta fashe da dariya ba saboda mugunta, shi kam rufe mata baki ya yi yace "Yanzu fad'a min me ki ke so na baki a matsayin tukuici? Wallahi na ji dad'in kasancewar mu yanzun nan." Ya k'arashe da sumbatar wuyan ta.

Cikin rik'e dariya tace "Ba na son komai miji na, tunda ma ka yi farin ciki hakan ya ishe ni."

Mik'ewa ya yi yace "Nagode matata, ni zan koma can na canza kaya, amma ki tashi ki yi wanka yanzu sai ki fito mu ci abinci."

Cike da makirci tace "Toh."

Ya na fita ta sauka da gaggawa ta shiga ta yi wanka ta fito ta yi sallah, riga ta saka iya gwiwa yar kanti ta fito da ita kai babu d'an kwali, lokacin Bilal har ya shirya Bilyamin ya d'auke shi sun tafi, Usman na zaune akan kujera Khadija na zuba masa abinci, yanda ya d'aure fuska babu annuri ne ya sa ta share shi ita ma, mayar da kallon shi ya yi ga Haseenah da ta fito ta na karkad'e gashin ta cikin takon jan hankali, kallon ta Khadija ta yi har ta zauna akan kujera, da wani shegen murmushi Usman yace mata "Sannu da fitowa."

Turo baki ta yi cikin shagwab'a tace "Ba zan sake ma ka magana ba sai nan da wata d'aya."

"Me?" Ya fad'a da zaro ido, d'orawa ya yi da "Haba amarya rufa min asiri mana, ina zan saka kai na to idan ki ka daina min magana, kinsan fa ke ce haske kuma fitilar zuciya ta dama gidan nan ba ki d'aya."

Sake turo baki ta yi ta kawar da kai tace "Ni ka k'yale ni kawai."

"To wai me na yi ma da za'a min wannan hukuncin?"

Kallon Khadija ya yi saboda aje farantin abinci da ta yi gaban shi, ita ma zubawa ta yi ta zauna ta fara tsakura ta na satar kallon su, amma zuciyar ta ta kai k'arshe wajen k'una, cike da shagwab'a tace "Ka ma manta kenan? Haka kawai ina bacci na za ka zo ka tara min gajiya, yanzu gashi duk jiki na ciwo ya ke, kuma saida na fad'a ma ka kar ka yi amma ka k'i saurara ta."

Hannu ya sa ya na shafa wuyan shi cikin alamun rashin gaskiya, satar kallon Khadija ya yi wacce ta k'i d'ago kai saboda hawayen da ke son taho mata, dan ya kawar da zancen ya sa ya kalle ta yace "Ba ki zuba mata abincin ba ita."

Wani jan kallo ta mi shi tace "Au! Wai ni ce ma zan zuba mata? To ai na ga duka yau kwanan mu ne ni da ita, me zai hana ta zuba da kan ta ko kuma ka zuba mata."

Had'e rai ya yi yace "Ke me ki ke nufi ne? Ba na son maganar banza fa kinji ko, daga k'aramar magana za ki wani tasowa mutane, zuciyar ki ta raya mi ki k'arya da gaskiya kawai sai ki zauna akai."

Zunbur ta mik'e tace "Au! Wai zuciya ta ma ce ta raya min kenan? To kamar yanda ba ka son maganar banza haka nima, wallahi Abban Bilal ka ji tsoron Allah kasan cewa za ka mutu."

Maida kallon ga tayi ga Haseenah tace "Ke kuma ki sani duk rayuwar da aka ginata babu Allah a ciki wallahi k'arshen ta munin ta ya na bayar da mamaki, Allah ma shaida ne ban rik'e ki a zuciya ta ba ko kad'an, na so na zauna lafiya da ke mu taru mu farantawa mijin mu, amma na fahimci kin biyo abun ta bayan gida saboda cimma burin ki a kai na, ki sani Haseenah wallahi tallahi da ace zan yi dan na raba ki da Usman, to ina da bokan da idan har ya shiga tsakanin ki da shi wallahi tallahi ba ke ba duk wanda ya zauna tare da ke ma sai ya tsane shi, amma tuna akwai Allah kuma zan mutu ya sa na d'aga mi ki k'afa, amma muje zuwa."

Ta na fad'a ta juya ta koma falon ta, janyo Haseenah ya yi ya d'ora a cinyar shi ya fara bata abincin ya na fad'in "Ki shirya kayan ki, ina tunanin tafiya da ke Dubai a satin nan, dan ba zan yarda na barki tare da matar nan ba a gidan nan."

Duk da a zuciyar ta akwai abin da taji shed'an na raya mata, amma sai ta nuna ta yi murna ta hanyar cewa "Dubai? Ni? Wayyo Allah yaushe? Da gaske ka ke?"

"Um, ki shirya kawai, ina tunanin tafiya nan da kwana biyu zuwa uku."

Haka suka gama cin abincin ya fita ita kuma ta koma d'aki, ta jima ta na waya da Mariya ta na fad'a mata canjin da aka samu, amma ba ta fad'a mata abin da ta ke shirin aikatawa ba har suka yi sallama, su na gamawa Haseenah ta shirya tsaf ta fito, kai tsayz k'ofar fita ta nufa mai gadi ya bud'e mata k'ofa, a lokacin Khadija na madafa ta tsinkaye ta ta fice, aikin gaban ta ta ci gaba da yi ba tare da tunanin komai ba, har ta gama aiki da duk abin da ta ke yi, ta na zaune falo tare da Bilal Usman ya shigo, ta yi mamakin ganin shi a lokacin sosai, shi ma kuma ya na ta kiran Haseenah ne ta k'i d'aga wayar shi duk abin duniya ya dame shi, hakan ya sa ya zo gidan kuma ya na nufa b'angaren ta ya ga k'ofar rufe alamar ba ta nan, shi ya sa ya shigo wajen Khadija, tsaye ya yi a kan ta yace "Na ga yarinyar nan ba ta nan ko kinsan in da ta tafi?"

Wani murmushin ta yi tace "Ni kuma ina zan san in da ta tafi? Ko gaishe ni ka ga ta na yi bare na samu kimar da za ta fad'a min za ta fita."
Chapter 41 · 0% Book details