← Book details Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 59 OF 86

Sashe 59

Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cewar malam, kallon malam ya yi ya kalli kofin hannun shi, ruwa ne dai fari k'al da su, kallon malam ya yi yace "Baba wannan fa? Na miye?"

"Karb'i kasha, na tsari ne." Ya fad'a ba alamar wasa, hannu ya sa ya karb'a ya yi bismillah ya kifa kai ya shanye, aje kofin ya yi ya musu sallama ya fita, bayan shi Hajia ta biyo saida ya zi gaf da d'akin ta tace "Bismillah nan." Saboda ba za ta kira sunan shi ba, bayan ta kawai ya bi suka shiga, ya na shiga ta mik'o mi shi roba da nono a ciki da abun magani tace "Shanye ka bani roban, kuma ka hi bismillah, sannan kasha zuciyar ka d'aya ba tare da tunanin cutar da wani ba ko wata."

A raunane ya kalle ta yace "Hajia shi kuma wannan na miye?"

Wani kallo ta watso masa amma ba tace komai ba, sanin ma'anar kallon ya sa ya kifa kai nan ma saida ya shanye kad'ai ya mik'a mata robar ya mata saida safe ya fito, haka ya d'auki hanya ya na tunanin abin da iyayen shi ke nufi da shi, da haka ya isa gida ya samu Haseenah yau dai ta yi girki kam, amma badan ranshi na so ba ya ci abin da ta dafa d'in har suka kwanta.

Bayan tafiyar shine Hajia ta ji kamar ta yi kuskuren rashin sanar da shi wani abu, amma ta yi niyyar fad'a mi shi gobe da safe idan ya zo, sai dai kuma ta makara kam, dan Usman ya jima baiyi bacci ba ya na dafe da cikin shi, da Haseenah ta tambaye shi kuma bud'ar bakin shi cewa ya yi "...

_Mu tara a shafi na gaba insha Allah._

*Ku yi hak'uri da ni mutane na abisa jinkira na, hakan na faruwa ne saboda sauyawar yanayi na.*

~*LUVE U ALL*~🥰😘
23/02/2020 à 13:03 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._

*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

```Fatan alkairi masoya```

_*Lubabatu Shehu shayi*, ina ganin sak'onninki sosai, lallai ke masoyiya ce ta hak'ik'a, tun a gidan Raheenat muke tare, kuma gashi har yanzu kina tare dani a gida na na kallon kitse, Allah ya bar k'auna._

*KALLON KITSE FAN'S 1&2*

💑 _Wannan sadaukarwar taku ce, kuyi yanda kuke so da ita._💑

_Bismillahir rahamanir rahim_

*30*

"Wallahi kawai wani kindirmu ne Hajia ta bani nasha, gaba d'aya ya na neman lalata min ciki ma." K'aramin tsaki ya yi, ita kam da mamaki tace "Kindirmu kuma? Haka kawai?"

Kamar wanda aka takura dole yace "Ina jin ko magani aka saka a ciki kome, ban dai sani ba ni dai kawai ya lalata min ciki sai tayar min da zuciya yake."

Cike da kissa ta shafo shi tace "To in hakane kar ka sake sha mana, tunda ya na tayar maka da zuciya, zai iya saka ka amai ma fa."

"Ina tunanin haka nima." Ya fad'a ido rufe, kallon shi ta yi tace "To wai ma maganin meye aka baka? Ba ka da lafiya ne dama ban sani ba."

Bud'e ido ya yi ya kalle ta yace "Ke kar ki tsora ta, lafiya ta k'alau mana ke shaida ce, tace dai ko maganin tsarin jiki ne da kuma...mtss na manta dai, kawai share."

Tashi tayi zaune ta na kallon shi idon shi rufe, tabbas in dai har hakane to iyayen shi sun fara hango wani abu kenan, d'aukar mataki shine abin da ya kamace ta kawai, dan haka tace "To beby in hakane me zai hana ka karb'o maganin, kaga sai ka rik'a sha anan zaifi da sai kaje can, koya ka gani."

Cike da damuwa yace "Kar ki damu kan ki, ni fa ba wani shan shi zan dinga yi ba, ina addu'a na tsarin jiki hakan ma ya isa, kawai ki rabu da su, kinsan tsofaffin nan da tame-tame."

Murmushi ta yi tace "Duk daha beby, idan ma ba za ka sha ba ai sai ka karb'o shi, dan in har ya na wajen su to ba fashi sai ka sha shi ko da za ka mutu ne."

Shiru ya yi ya na tuna lokacin da ya tambayi Hajia amma ta yi banza da shi, hakan na nufin dole dai ya sha ba makawa, dan haka yace "Ba tabbacin za su k'ara bani, amma in har sun bani na sha to zan karb'o shi daga wajen su na taho da shi."

"Gaskiya kam, da ba zan so wani abu ya samar min miji ba uban 'ya'ya." Ta fad'a ta na gyara kwanciyar ta, daga haka babu wanda ya sake magana har bacci ya d'auki dukan su.

*Yau kam* Alhamdulillah Khadija ta tashi jiki da sauk'i sosai, da kan ta ta gyara d'akin ta da na Bilal da ma na Mama, zuwa k'arfe goma kuma ta fita madafar da matan gidan ke aiki, da kan ta ta fara girkin rana kafin matan yan uwan ta suka fito su ka kama aka k'arasa, *12:10* yaran su ka fara shigowa da sallama wasu kuma da gudu, kowa wajen tashi uwa ya nufa kafin suka wuce d'aki dan cire kaya, lokacin ne Khadija ita ma ta shiga d'aki dan ta yi wanka ta yi alwala, ta na d'aure da k'irji za ta shiga ban d'aki wayar ta tayi k'ara, dawowa ta yi dan d'auka amma har ta tsinke, d'aukar wayar ta yi ta duba mai kiran, sunan k'awar ta ne Kaltume, aje wayar ta yi da niyyar idan ta fito ta kammala za ta kira ta, har ta aje ta yi sauri ta sake d'auka saboda idon ta da ya sauka kan kwanan (date) wata, dubawa ta yi da kyau taga tabbas yau wata na da kwana *21*, kai da kawowa ta fara yi tsakiyar d'akin ta na tunanin yanda ta kasa ankara da lokacin al'adarta har wata ya ja haka, sai lokacin kuma ta iya tunawa fa tunda Usman ya yi aure ma bata sake ganin jinin ta ba, to me hakan ke nufi? Ta tambayi kan ta.

"Kenan ciki gare ki kamar yanda Mama ta tambaya?" Da sauri ta zo gaban madubi ta janye d'aurin k'irjin ta tana shafa marar ta, tabbas sai lokacin kad'ai ta iya fahimtar tudun da mararta ta yi, a hankali ya fad'a kan gado ta yi zaune ta rufe ido, wasu hawayen farin ciki ne suka zubo mata ba tare da sanin ta ba, hannu ta sa ta share ta d'aga hannu sama ta furta "Alhamdulillah Allah, Allah kaine Allah, kuma kai ka ce mu rok'e ka za ka amsa mana, Allah nagode ma ka abisa wannan baiwar da ka min, Allah ka tabbatar min da alkairi."

Saukowa ta yi daga kan gadon ta shiga wanka, da sauri ta k'arasa ta fito ta saka kaya ta yi sallah, gyalen ta ta saka ta d'auki jaka tasa takalma ta fito, da kallo Mama ta biyota tace "Ke kuma ina zuwa haka da rana patsal-patsal haka?"

Kasancewar duk matan gidan na d'akin ya sa ta matsa kusan amaryar Ashir tace "Duk cikin nan ke ce babba, dan haka ke ce zan iya fad'awa dan ba na jin kunyar ki."

Rad'a ta mata a kunne kafin ta fice daga d'akin da sauri, dariya amaryar Ashir ta yi ta kalli Mama tace "Mama wai kinsan me?"

"Sai kin fad'a mana zan sani." Cewar Mama, saida ta jinjina kai tace "Ai Mama sai kin bani goron albishir kafin na fad'a."

"Ita goron ki ka bata kafin ta fad'a mi ki? Ai naga kyauta ta fad'a mi ki."

Dariya matar Bashir ta yi tace "To ai Mama shugaban k'asa ya hana aikin banza."

Tab'e baki Mama ta yi tace "To can ku k'arata ku da shugaban k'asar na ku, ku rik'e sirrin ku ba na son ji."

Dariya amaryar Ashir ta yi tace "Mama Khadija fa cewa ta yi ta na zargin ta na da juna biyu, yanzu ma za ta je asibiti ne a tabbatar mata da gaskiya."

Waro ido Mama ta yi tace "Ke *Safiya* ba na son k'arya, da gaske ki ke?"

"Wallahi kuwa Mama haka ta fad'a."

Wani murmushin farin ciki Mama ta yi kafin tace "Allah ya tabbatar da alkairi, *wani hanin ga Allah baiwa ne*."

"Hakane Mama." Suka amsa da shi.

Khadija na fita cikin sauk'i ta samu adaidaita sahu ta kai ta *Clinique tattali*, kamar yanda ta yi tunanin kam hakane ta faru, dan kuwa ta samu k'awar ta ce akan aiki mai sunan *Maryama*, kasancewar babu mutane a asibitin ya sa suka fara tab'a hira kafin ta fad'a mata abin da ya kawo ta, nan ma saida aka sha wata hirar kafin ta mata gwajin fitsari, ko da ta duba dan ta ga sakamakon Khadija tace"Dakata."

Kallon ta ta yi ita kuma tace "Kawai ki min murmushi idan har gaskiya ne tunani na, in kuma babu to ki had'e rai."

Dariya Maryama ta yi tace"Kaga wani sabon gwajin ciki kuma, to bara na gani." Ta na dubawa kam ta ga ciki dai ya tabbata, haba wa ai sai ta washe mata hak'ora tace "Ke kiyi farin ciki, wallahi ciki ya tabbata, kai Khadija na miki murna wallahi."
Chapter 59 · 0% Book details