Sashe 29
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kai ma kasan dole zan damu da kai, sai dai ba na son shiga hurumin da ba nawa bane."
Mik'ewa ya yi ya nufi frije d'in ta ya bud'a, wani k'aton cake ya d'auko mai suffar zuciya tare da yagourt mai kauri da sanyi, komawa ya yi ya zauna ya fara ci ya na shan madarar, Khadija dai kallon shi take har ya sai da ya cinye duka kafin ya mik'e, ban d'akin ta ya shiga ya wanko bakin shi ya dawo, kallon ta ya yi yace "Umman Bilal ya yarinyar can ta fad'a min kinga lokacin da take tuwo ko?"
Gyara zama ta yi akan gadon tace "Eh, na gani."
"To amma me ya sa ba ki fad'a mata ba na cin tuwo ba? Tunda ke kin sani."
Da mamaki ta kalle shi tace "Au! Wai dama duk soyayyar da ku ka yi ba ka tab'a fad'a mata abin da ka ke so ba da wanda ba ka so? Dole sai ni ce zan dinga fad'a mata?"
Matsowa ya yi kusanta yace "A gani na ya zama dole tunda ke ce gaba da ita, me ya sa ba za ki d'ora ta a hanya ba a matsayinki na babba?"
Da k'arfi ta zaburo daga kan gadon ta sauko ta na fad'in "Oho, wato babba juji ko? Komai tunda ke ce babba ke ce babba, to daga yau na bar mata girman ta d'auka, kuma ka je ka tambaya ta idan ban fad'a mata ba ka cin tuwo ba, amma sai tace a dole ita ma sai ta d'ora ka a tsarin da ya mata, saboda ita ma matarka ce, haka kawai za ka zo ka d'ora min laifi ka cika ni da surutu."
Komawa ta yi kan gadon ta kwanta ta ja zani ta rufa, shi kam baki bud'e ya ke kallonta har ta kwanta, sunkuyawa ya yi ya sumbaci kumatun ta ya d'ago yace "Saida safe masifata."
Zunbur ta tashi tace "Masifar ka kuma? Abban Bilal ni ce ma masifar yanzu? Lallai ka kyauta."
Gimtse dariyar shi ya yi yace "To in ba tawa ba ta wacece? Ai Khadija sai Usman, Usman kuma sai Khadija, kinga dole na kiraki da masifa ta tunda na ga kin fara koyon masifar."
Cinno baki ta yi gaba ta bishi da kallo har ya kai k'ofa, sai da ya bud'e ya fita ya juyo yace "Allahya huci zuciyar Umman Bilal, ta Usman bada kanka a sare kaje gida ka ce ya fad'i, na Khadija ba ni shan furataba nono, hakan ya yi ko? Saida safe, ina son ki."
Dariya ce ta kubce mata, sumba ta aika masa tare da fad'in "Ina son ka ni ma, saida safe."
_Ni ma dai saida safen nan gaskiya._😉
*Washe gari* ta kama alhamis, hakan kuma ya sa duk yan islamiyya na hutu ba karatu, k'awayen Haseenah na su ka zo gidan tun misalin *11:00* bayan fitar Usman ba jimawa, in da Bilal ma ke gida ya na wasan shi, dan ya so ya je gidan su maman Khadija amma ta hana, a madafa suka tare su na ta hira abinsu, kasancewar *Zeinab* na da k'ok'arin aiki ya sa yau ita taja ragamar girkin gidan, abinci su ka had'a kala har uku da kuma abin sha, bayan sun gama su ka dawo falon Haseenah dan cin abinci, kiran Usman ta yi ya aiko a d'aukar mi shi abinci ta na da bak'i a gida, ba d'aukar lokaci ya aiko da yaron shi Bilyamin ya d'auka, su na ci su na kwamtsa hirarsu sai ga Mariya, sai da suka gama ta shiga da ita ciki inda ta kwashe komai ta fad'a mata, bud'ar bakin Mariya cewa ta yi "Lallai Haseenah ina tausaya miki, dan wallahi kishiyar nan ta ki ba k'aramar muguwa bace, kawai ki hak'ura ki bita sau da k'afa, domin kuwa ita da d'an ta ne da gidan nan wallahi."
Cike da damuwa Hassenah tace "Ni ma na fahimci hakan, kar ki tona raina ki ji me na ji ranar, ita ce da laifi amma ya rufe ido ya d'ora min laifin, wai shi ya san matan shi."
"Ai kad'an ma ki ka gani in dai ba ki tashi tsaye ba, yanzu dai ina magani da na baki? Kinyi aiki da shi?"
"Duka na yi, kuma ya ci abincin? Amma ni banga wani sabon abu ba."
Gyara zama ta d'anyi tace "Kinsan me zai faru, ki sake kawo kud'i a kaiwa malam ya sake mi ki wani maganin, ko da na bakali ne da kuma samun soyayyar shi."
"Kamar nawa?" Ta fad'a ta na kallonta, ita ma kallonta ta yi tace "Eh to, iya kud'in ki ai iya shagalinki."
Da alamar tambaya Haseenah tace "Ki na nufin idan na bayar da kud'i dayawa zaifi kyau aikin?"
"Sosai ma."
Mik'ewa ta yi ta bud'a jakarta da take zuba kud'in da yake bata tun da ta zo, yan biyar biyar ko karyawa babu guda hud'u ta bata, aifa baki har waje ta karb'a suka fito daga d'akin, sallama su ka yi ta tafi ta barta da k'awayen ta, yamma ta yi suka sake tashi kama mata aiki, sai dai suna buk'atar bredi dan soya shi da k'wai, babu yaron da za'a bawa ya siyo sai Bilal ta kira dake farfajiyar gida tare da mai gadi, kud'i ta bashi ya siyo mata bredi, cikin sanyin jiki yace "Aunty nan ba'a siyar da bredi sai can nesa tsallaken titi, kuma Abba ya hana ni fita har can wajen."
A gadarance tace "Kenan ba ka da wani anfani cikin gidan? Sai dai a dafa a baka ka ci? To k'arya ka ke, maza wuce ka d'auko wannan shegen moton na ka da baida anfani sai dai ka yi yawo da shi cikin gida ko k'ofar gida ka je ka siyo ka kawo min yanzun nan."
Cikin sanyi ya juyo ya nufo wajen uwatai, d'akin da ya ke aje moton ya fito da shi, Khadija na gani tace "To, to ina kuma zuwa da wannan tuk'a-tuk'ar?"
Sai da ya zo gabanta cikin turo baki yace "Ba aunty amarya ce ta aike ni siyan bredi ba."
Da mamaki ta kalle shi tace "Bredi fa? Amma ba ka fad'a mata ba ka tab'a zuwa ko bakin titi kai kad'ai ba bare gaban shi?"
"Na fad'a mata, amma tace wai ni ban da anfani a gidan sai dai na ci abinci, kuma wai dole na je na siyo."
Wata shegiyar dariya Khadija ta bushe da ita ta kalle shi ta kalli Uwani, mik'ewa ta yi tace "Ku biyo ni har da ke Uwani."
Fita su ka yi har madafar ta same su, sai shewa da hira su ke, suna ganin ta kowa ya yi shiru sai wani kallo ake mata, ko ta kan su bata bi ba ta kalli Haseenah tace "...
*Ku yi hak'uri da wannan.*
29/01/2020 à 13:36 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_INA K'ARA TAYA 'YAR UWARMU KUMA D'AYA DAGA CIKIN 'YAR GIDAN AMANA WATO MEMBER'S D'IN K'UNGIYAR *🇸🇦ZAMAN AMANA* MAI SUNA *MARYARHMAH UMMISIDDIQUE* MARUBUCIYAR *MINTI KARU'NYI YE* DA KUMA *NAGA TA KAINA* TA'AZIYYAR RASHIN UWA MAHAIFIYA DA TAYI, INA ADDU'A GA UWAR KIRKI HAR KULLUM ALLAH YAKAI RAHMA K'ABARINTA, ALLAH YA K'ARA MANA HAK'URIN RASHINTA, MUNYI RASHIN UWAR K'WARAI😰_
_Bismillahir rahamanir rahim_
*17*
"Haseenah, ga Uwani ki bata kud'in ta siyo mi ki bredin, amma Bilal mahaifin shi ya hana a aike shi ko kusa da titi."
Sai lokacin ta juyo ta kalle ta tace "Yanzu kamar Bilal ne za ace ba'a aikin shi, shi kad'ai ne yaro cikin gidan nan, kuma ace ba'a aikin shi, to me ya sa? Me ye anfanin haihuwar shi kena..."
Ba ta sauka daga abin da za ta fad'a ba Khadija ta ji ba za ta iya d'auka ba, zuciya ce kawai ta d'ebe ta ta kife ta da mari, kafin ta ankara ta shak'o wuyan rigar ta cikin d'aga murya tace "In ke ba ki san zafin haihuwa ba ni na sani, in ba ki san darajar 'yaya' ba ni na sani tunda na haifa, idan ba ki san anfanin haihuwa ba, to ki bari har ki bari ki haifi na ki sai ki zuba cikin shara, dama ya fad'a min kin ce wai sai dai a dafa a bashi ya ci, to ki sani Bilal ba jinin matsiyata bane, ko gidan uban shi babu abinci ba zai rasa abincin da zai ci ba daga dangin uwar shi, ki kiyaye ni, sannan ki fita ido na."
Sakin ta tayi ta juya ta fice, Zeinab ce ta yi saurin kallon Haseenah tace "Wai k'yale ta za ki yi? Jar uban nan, ai wallahi babu macen da ta isa."
Wannan magana ce ta sa Haseenah d'aukar k'aramar tab'aryar da ke madafar ta fita, su na ganin haka su ka tashi da sauri su ka bi bayan ta, Khadija na daf da shiga falon ta Haseenah ta sauke mata tab'aryar nan a kai, dafe kai ta yi ta juyo ta na fad'in "Kai kai kai kai."
Mik'ewa ya yi ya nufi frije d'in ta ya bud'a, wani k'aton cake ya d'auko mai suffar zuciya tare da yagourt mai kauri da sanyi, komawa ya yi ya zauna ya fara ci ya na shan madarar, Khadija dai kallon shi take har ya sai da ya cinye duka kafin ya mik'e, ban d'akin ta ya shiga ya wanko bakin shi ya dawo, kallon ta ya yi yace "Umman Bilal ya yarinyar can ta fad'a min kinga lokacin da take tuwo ko?"
Gyara zama ta yi akan gadon tace "Eh, na gani."
"To amma me ya sa ba ki fad'a mata ba na cin tuwo ba? Tunda ke kin sani."
Da mamaki ta kalle shi tace "Au! Wai dama duk soyayyar da ku ka yi ba ka tab'a fad'a mata abin da ka ke so ba da wanda ba ka so? Dole sai ni ce zan dinga fad'a mata?"
Matsowa ya yi kusanta yace "A gani na ya zama dole tunda ke ce gaba da ita, me ya sa ba za ki d'ora ta a hanya ba a matsayinki na babba?"
Da k'arfi ta zaburo daga kan gadon ta sauko ta na fad'in "Oho, wato babba juji ko? Komai tunda ke ce babba ke ce babba, to daga yau na bar mata girman ta d'auka, kuma ka je ka tambaya ta idan ban fad'a mata ba ka cin tuwo ba, amma sai tace a dole ita ma sai ta d'ora ka a tsarin da ya mata, saboda ita ma matarka ce, haka kawai za ka zo ka d'ora min laifi ka cika ni da surutu."
Komawa ta yi kan gadon ta kwanta ta ja zani ta rufa, shi kam baki bud'e ya ke kallonta har ta kwanta, sunkuyawa ya yi ya sumbaci kumatun ta ya d'ago yace "Saida safe masifata."
Zunbur ta tashi tace "Masifar ka kuma? Abban Bilal ni ce ma masifar yanzu? Lallai ka kyauta."
Gimtse dariyar shi ya yi yace "To in ba tawa ba ta wacece? Ai Khadija sai Usman, Usman kuma sai Khadija, kinga dole na kiraki da masifa ta tunda na ga kin fara koyon masifar."
Cinno baki ta yi gaba ta bishi da kallo har ya kai k'ofa, sai da ya bud'e ya fita ya juyo yace "Allahya huci zuciyar Umman Bilal, ta Usman bada kanka a sare kaje gida ka ce ya fad'i, na Khadija ba ni shan furataba nono, hakan ya yi ko? Saida safe, ina son ki."
Dariya ce ta kubce mata, sumba ta aika masa tare da fad'in "Ina son ka ni ma, saida safe."
_Ni ma dai saida safen nan gaskiya._😉
*Washe gari* ta kama alhamis, hakan kuma ya sa duk yan islamiyya na hutu ba karatu, k'awayen Haseenah na su ka zo gidan tun misalin *11:00* bayan fitar Usman ba jimawa, in da Bilal ma ke gida ya na wasan shi, dan ya so ya je gidan su maman Khadija amma ta hana, a madafa suka tare su na ta hira abinsu, kasancewar *Zeinab* na da k'ok'arin aiki ya sa yau ita taja ragamar girkin gidan, abinci su ka had'a kala har uku da kuma abin sha, bayan sun gama su ka dawo falon Haseenah dan cin abinci, kiran Usman ta yi ya aiko a d'aukar mi shi abinci ta na da bak'i a gida, ba d'aukar lokaci ya aiko da yaron shi Bilyamin ya d'auka, su na ci su na kwamtsa hirarsu sai ga Mariya, sai da suka gama ta shiga da ita ciki inda ta kwashe komai ta fad'a mata, bud'ar bakin Mariya cewa ta yi "Lallai Haseenah ina tausaya miki, dan wallahi kishiyar nan ta ki ba k'aramar muguwa bace, kawai ki hak'ura ki bita sau da k'afa, domin kuwa ita da d'an ta ne da gidan nan wallahi."
Cike da damuwa Hassenah tace "Ni ma na fahimci hakan, kar ki tona raina ki ji me na ji ranar, ita ce da laifi amma ya rufe ido ya d'ora min laifin, wai shi ya san matan shi."
"Ai kad'an ma ki ka gani in dai ba ki tashi tsaye ba, yanzu dai ina magani da na baki? Kinyi aiki da shi?"
"Duka na yi, kuma ya ci abincin? Amma ni banga wani sabon abu ba."
Gyara zama ta d'anyi tace "Kinsan me zai faru, ki sake kawo kud'i a kaiwa malam ya sake mi ki wani maganin, ko da na bakali ne da kuma samun soyayyar shi."
"Kamar nawa?" Ta fad'a ta na kallonta, ita ma kallonta ta yi tace "Eh to, iya kud'in ki ai iya shagalinki."
Da alamar tambaya Haseenah tace "Ki na nufin idan na bayar da kud'i dayawa zaifi kyau aikin?"
"Sosai ma."
Mik'ewa ta yi ta bud'a jakarta da take zuba kud'in da yake bata tun da ta zo, yan biyar biyar ko karyawa babu guda hud'u ta bata, aifa baki har waje ta karb'a suka fito daga d'akin, sallama su ka yi ta tafi ta barta da k'awayen ta, yamma ta yi suka sake tashi kama mata aiki, sai dai suna buk'atar bredi dan soya shi da k'wai, babu yaron da za'a bawa ya siyo sai Bilal ta kira dake farfajiyar gida tare da mai gadi, kud'i ta bashi ya siyo mata bredi, cikin sanyin jiki yace "Aunty nan ba'a siyar da bredi sai can nesa tsallaken titi, kuma Abba ya hana ni fita har can wajen."
A gadarance tace "Kenan ba ka da wani anfani cikin gidan? Sai dai a dafa a baka ka ci? To k'arya ka ke, maza wuce ka d'auko wannan shegen moton na ka da baida anfani sai dai ka yi yawo da shi cikin gida ko k'ofar gida ka je ka siyo ka kawo min yanzun nan."
Cikin sanyi ya juyo ya nufo wajen uwatai, d'akin da ya ke aje moton ya fito da shi, Khadija na gani tace "To, to ina kuma zuwa da wannan tuk'a-tuk'ar?"
Sai da ya zo gabanta cikin turo baki yace "Ba aunty amarya ce ta aike ni siyan bredi ba."
Da mamaki ta kalle shi tace "Bredi fa? Amma ba ka fad'a mata ba ka tab'a zuwa ko bakin titi kai kad'ai ba bare gaban shi?"
"Na fad'a mata, amma tace wai ni ban da anfani a gidan sai dai na ci abinci, kuma wai dole na je na siyo."
Wata shegiyar dariya Khadija ta bushe da ita ta kalle shi ta kalli Uwani, mik'ewa ta yi tace "Ku biyo ni har da ke Uwani."
Fita su ka yi har madafar ta same su, sai shewa da hira su ke, suna ganin ta kowa ya yi shiru sai wani kallo ake mata, ko ta kan su bata bi ba ta kalli Haseenah tace "...
*Ku yi hak'uri da wannan.*
29/01/2020 à 13:36 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Littatafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
```Fatan alkairi masoya```
_INA K'ARA TAYA 'YAR UWARMU KUMA D'AYA DAGA CIKIN 'YAR GIDAN AMANA WATO MEMBER'S D'IN K'UNGIYAR *🇸🇦ZAMAN AMANA* MAI SUNA *MARYARHMAH UMMISIDDIQUE* MARUBUCIYAR *MINTI KARU'NYI YE* DA KUMA *NAGA TA KAINA* TA'AZIYYAR RASHIN UWA MAHAIFIYA DA TAYI, INA ADDU'A GA UWAR KIRKI HAR KULLUM ALLAH YAKAI RAHMA K'ABARINTA, ALLAH YA K'ARA MANA HAK'URIN RASHINTA, MUNYI RASHIN UWAR K'WARAI😰_
_Bismillahir rahamanir rahim_
*17*
"Haseenah, ga Uwani ki bata kud'in ta siyo mi ki bredin, amma Bilal mahaifin shi ya hana a aike shi ko kusa da titi."
Sai lokacin ta juyo ta kalle ta tace "Yanzu kamar Bilal ne za ace ba'a aikin shi, shi kad'ai ne yaro cikin gidan nan, kuma ace ba'a aikin shi, to me ya sa? Me ye anfanin haihuwar shi kena..."
Ba ta sauka daga abin da za ta fad'a ba Khadija ta ji ba za ta iya d'auka ba, zuciya ce kawai ta d'ebe ta ta kife ta da mari, kafin ta ankara ta shak'o wuyan rigar ta cikin d'aga murya tace "In ke ba ki san zafin haihuwa ba ni na sani, in ba ki san darajar 'yaya' ba ni na sani tunda na haifa, idan ba ki san anfanin haihuwa ba, to ki bari har ki bari ki haifi na ki sai ki zuba cikin shara, dama ya fad'a min kin ce wai sai dai a dafa a bashi ya ci, to ki sani Bilal ba jinin matsiyata bane, ko gidan uban shi babu abinci ba zai rasa abincin da zai ci ba daga dangin uwar shi, ki kiyaye ni, sannan ki fita ido na."
Sakin ta tayi ta juya ta fice, Zeinab ce ta yi saurin kallon Haseenah tace "Wai k'yale ta za ki yi? Jar uban nan, ai wallahi babu macen da ta isa."
Wannan magana ce ta sa Haseenah d'aukar k'aramar tab'aryar da ke madafar ta fita, su na ganin haka su ka tashi da sauri su ka bi bayan ta, Khadija na daf da shiga falon ta Haseenah ta sauke mata tab'aryar nan a kai, dafe kai ta yi ta juyo ta na fad'in "Kai kai kai kai."