Sashe 69
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Hajia wai me ta ke yi a gidan su? Dan Allah ki fad'a min ko na ji sauk'i, wallahi ji na ke kamar na tashi a bacci."
Shiru Hajia ta yi ta na tunanin abin da za ta fad'a ma sa, kamar zaiyi kuka yace "Hajia ki taimaka ki fad'a min mana, dan Allah ki ce ba wani mugun abu na yi wa Khadija da har ya sa ta tafi gidan su, Hajia kinfi kowa sanin Nana ita ce rayuwa ta, dan Allah ki cire ni a duhun nan."
Cike da k'aguwa Hajia tace"Fodio, na ce ka je godan nasu ka same ta ko."
Ikon Allah sai kawai Usman ya ji hawaye a fuskar shi, cikin rawar murya yace "Hajia sakin ta na yi?"
Jin muryarshi ya sa Hajia jikinta yin sanyi, tabbas sunyi kuskure a baya da su ka nunawa Khadija k'iyayya, gashi alamu na nuna cewa Khadija dai ita ce rayuwar d'an su, jin shiru ya sa yace "Hajia na shiga uku idan sakin ta na yi, Hajia tun yaushe ta ke gida?"
Kashe wayar kawai Hajia ta yi ta aje gefe ta fito waje su ka ci gaba da harkokin gaban su, sai dai kuma hankalin ta ya koma kan Usman da abin da ke faruwa, Haseenah na d'aki zaune ba aikin fari bare na bak'i sai kallon mai bisa ruwa takewa kowa, Usman kam daga nan baiyi k'asa a gwiwa ba wajen wucewa gidan su Khadija ya na addu'a a zuciyar shi "Allah ka sa ba wani abu nayi wa Khadija ba, Allah na rok'e ka kasa ba fad'a mu ka yi ba." Wani lokacin kuma mamakin kasa tuna komai ne ke damunshi, da haka ya isa gidan ya paka mota a k'ofar gidan, zai sallama sai ga Bashir zai fito daga ciki, gaisawa su ka yi cikin mutumta juna kafin yace ya wuce ciki Hajia na nan shi zai fita ne, ba musu ya wuce dan dama ba tsayawa zaiyi ba, Hajia na zaune tsakiyar less da atampopi ya sallama tace ya shigo, zaune ya yi k'asa kamar yanda ya same ta a k'asa ita ma, gaisawa su ka yi kamar kullum kafin ya d'anyi shiru ya na tunanin ta'inda zai fara, shiru ne ya ratsa d'akin kamar ba kowa a ciki, a hankali Hajia ta kalle shi da murmushi tace "Komai lafiya dai ko?"
Saida ya rarraba ido kafin yace "Mama, wani abu ne ya ke faruwa da ni da na ke so na samu amsar tambayoyi na anan, dan Hajia ta ma k'i saurara ta bare ta fad'a min me ke faruwa, dan Allah Mama ki taimaka ki fad'a min ina Khadija take? Sannan meya faru tsakani na da ita da har ya sa take zaune gida?"
Jim Mama ta yi ta na tunanin to in har iyayen shi ba su fad'a mi shi ba me zaisa ita ta fad'a, murmushi kawai ta yi ta kalle shi tace "Ba komai Usman, ka wuce ta na ciki yanzu mu ke zaune tare da ita ta shiga ta yi sallah."
Damuwar kan fuskar shi ce ta k'aru yace "Mama, dan girman Allah ki fad'a min meya faru tsakanin mu, Mama idan ma sakin ta na yi wallahi tallahi bansan na yi ba, shi ya sa na ce mu ku wani abu ne ke faruwa, gaba d'aya na kasa tuna komai ji na ke kamar daga dogon bacci na tashi."
Ganin kamar zai mata kuka ya sa ta saki fuska tace "Kar ka damu Usman, ba wata babbar matsala ba ce, ka shiga ka same ta a ciki ku yi magana, idan har ka na so ma za ka iya tafiya da matar ka gida yanzun."
Sai lokacin murmushi ya bayyana a fuskar shi yace "Mama da gaske zan iya tafiya da ita? Kai Alhamdulillah Allah na gode ma ka."
Dariya Mama ta yi ta na kallo ya shiga ciki, dama k'ofar ba rufe ta ke ba kamar yanda tafi barinta mafi yawan lokuta, ya na tura k'ofar ya shiga ya yi daidai da Khadija ta idar da sallah ta mik'e tare da cire hijabin ta, riga ce jikinta ruwan madara mai k'ananan hannuwa wacce ta kama ta, sai bak'in siket da ya bud'e sosai bai kama jikin ta ba, saida gabanta ya fad'i ganin mutum kawai a d'akin, amma kuma saita kasa motsawa saboda tasan yau ta ta kam ta k'are dan idon shi na kan cikin ta, Usman da tunda ya d'ora idon shi akan cikin ta yaji k'wak'walwar shi ta fara tuna ma sa da wasu abubuwan, mamaki ne fal a fuskar shi har ya fara matsowa kusan ta, ta na ganin haka ta fara ja da baya a hankali shi ma ya na bin ta, daf da ban d'aki ta juya da sauri za ta shige ciki da azama ya rik'o hannun ta.
Janyo hannun ta ya yi har saida ya zaunar da ita bakin gadon ya tsaya gabanta sank'am kamar zai fad'a mata ya na kallo, kan ta k'asa ta kasa had'a ido da shi kafin yace "Ya mu ka yi da ke?"
D'agowa ta yi tace "Akan me fa?"
Had'e rai ya yi yace "Kar ki raina min wayo mana, Khadija me ye hujjar ki na b'oye min ki na da ciki? Akan me za ki min haka?"
Mik'ewa ta yi tace "Kaga malam dan Allah kar ka d'aga min hankali, ni babu wani ciki da na ke da, ko kai ka ga na yi ma ka kama da masu ciki ne?"
Wani bala'in haushi ne ya taso mi shi amma sai ya share yace "Tashi wuce muje gida sai mu yi maganar acan."
"Wane gidan kuma?" Ta fad'a ta na kallon shi, kai tsaye yace "Gidan ki mana."
Wani murmushi ta yi tace "Ni ai duk filaye ne gare ni har yanzu ban gina gida ko d'aya ba."
Cile da k'aguwa yace "Haba uwar yarima, gidan mu fa na ke nufi, ki tashi mu tafi mana."
Cikin nuna rashin damuwa tace "Au! Ai wannan gidan ka ne ba nawa ba, idan da nawa ne ma ai da ba ka yi abin da ka yi ba har na baro ma ka gidan."
A hankali ya durk'usa kan gwiwoyinshi ya rik'o hannayen ta yana murzawa yace "Khadija fad'a min me na mi ki in ba ki hak'uri? Ke kinsan ba zan iya cutar da ke ba, tunda mu ke da ke ba mu tab'a samun sab'anin da yasa mu ka raba shinfid'a ba bare gida, dan Allah ki fad'a min sai na baki hak'uri yanzu kuma mu koma gida tare, sanin kan ki ne ba zan iya bacci ba alhalin ke ki na nan."
Ajiyar zuciya ta sauke tace "Ka na nufin ka ce ba ka san ma me ka min ba?"
Kamar zaiyi kuka yace "Wallahi na manta Khadija, komai ya dawo min kamar sabo a rayuwa ta." Tab'e baki ta yi tace "To kaga ka tashi dai yanzu ka koma gidan ka kafin amaryar ka ta fara neman ka."
Tsaki yaja yace "Ina mi ki magana mai mahimmanci ke ki na magana akan wata, dallah malama ki tashi ki wuce mu tafi gida."
Waro ido ta yi irin mamakin nan tace "Eyee! Lallai ma mutumin nan, to ba zan je ba ina nan gidan mu."
Ba alamar wasa yace "Haka ki ka ce?" Ita ma ba tsoro tace "Eh, haka na fad'a."
Yatsunshi ya sa biyu ya kama agarar (jijiyar da ke bayan k'afa kusa da diga-digi) ya dinga murzawa da zafi, da sauri ta janye k'afar ta sai kuwa ya rik'e k'afar ya na fad'in "Ba dai kinfi son na mi ki hukunci a gidan ba? To ai sai mu zuba ni da ke, na ga wanda ya isa ya k'wace a hannu na yau."
K'ok'arin k'watar k'afar ta ta shiga yi amma ya hanata dama, idon ta ne suka cika fal da ruwa ta na so ta bashi hak'uri amma ta k'i magana, shi kam ko a jikin shi har cije leb'e yake ya na fad'in "Uhum! Da dad'i ko? To yaya yanzu za ki fad'a min dalilin ki na k'in fad'a min ki na da ciki?"
Jin zafi ya kai mata ya sa ta bud'a baki da k'arfi tace "Mamaaaaa, ki zo ki taimake ni."
Bushewa ya yi da dariya yace "Kuma a zaton ki za ta zo? Kar ki wahalar dani a banza ki fad'a min abin da na ke son sani."
Jin bala'in na k'aruwa ya sa Khadija fashewa da kuka irin na sangartattun yaran nan ta na fad'in "Dan Allah ka yi hak'uri zan fad'a ma ka, wallahi zafi ke akwai, dan Allah ka daina zan fad'a."
D'an tsagaitawa ya yi yace "To ina jinki." Saida ta fara goge hawaye tace "To d'anyi baya mana ka matse ni sosai."
Kallon da ya mata ya sa ta d'an matsa baya amma sai ya sake binta ba tare da ya mik'e tsaye ba, shiru ta yi shi kuma ya sake kamo k'afar ta yace "Ke fa na ke saurare, muguwa kawai, da meye nufin ki to? Ban cancanci zama uban d'an ba ko kuma ke kad'ai ke da shi? Allah sai kin fad'a min dalilin ki ko na rabu da ke."
Tangale kanta ta yi da hannayen ta ta rufe fuska ta na tunani, a hankali taji ya d'an d'ago ya zauna bakin gadon ya rumgumota jikin shi, cikin taushin murya yace "Nana, ki fad'a min komai da ya faru mana, meye ake b'oye min haka da ba'a so na sani? Kowa na tambaya sai ya yi shiru ba ya son fad'a min komai."
D'agowa ta yi daga jikinshi tace "Kaje ka tambayi Hajia ko Baba su za su fad'a ma ka komai."
"Ban damu da sanin komai ba Khadija, na fi damuwa da sanin abin da ya sa ki ke zaune gida."
Tallabo fuskarta ya yi yasa idonta cikin na shi yace "Khadija me nai mi ki da zafi haka?"
Kamar za ta fashe da kuka tace "Mun samu sab'ani ne da kai akan amaryar ka, sab'anin da ya sa ka yi abin da ba ka tab'a yi ba a rayuwar ka, shine ni kuma na dawo gida gaba d'aya a lokacin ba ka buk'ata ta a gidan ka."
Shiru Hajia ta yi ta na tunanin abin da za ta fad'a ma sa, kamar zaiyi kuka yace "Hajia ki taimaka ki fad'a min mana, dan Allah ki ce ba wani mugun abu na yi wa Khadija da har ya sa ta tafi gidan su, Hajia kinfi kowa sanin Nana ita ce rayuwa ta, dan Allah ki cire ni a duhun nan."
Cike da k'aguwa Hajia tace"Fodio, na ce ka je godan nasu ka same ta ko."
Ikon Allah sai kawai Usman ya ji hawaye a fuskar shi, cikin rawar murya yace "Hajia sakin ta na yi?"
Jin muryarshi ya sa Hajia jikinta yin sanyi, tabbas sunyi kuskure a baya da su ka nunawa Khadija k'iyayya, gashi alamu na nuna cewa Khadija dai ita ce rayuwar d'an su, jin shiru ya sa yace "Hajia na shiga uku idan sakin ta na yi, Hajia tun yaushe ta ke gida?"
Kashe wayar kawai Hajia ta yi ta aje gefe ta fito waje su ka ci gaba da harkokin gaban su, sai dai kuma hankalin ta ya koma kan Usman da abin da ke faruwa, Haseenah na d'aki zaune ba aikin fari bare na bak'i sai kallon mai bisa ruwa takewa kowa, Usman kam daga nan baiyi k'asa a gwiwa ba wajen wucewa gidan su Khadija ya na addu'a a zuciyar shi "Allah ka sa ba wani abu nayi wa Khadija ba, Allah na rok'e ka kasa ba fad'a mu ka yi ba." Wani lokacin kuma mamakin kasa tuna komai ne ke damunshi, da haka ya isa gidan ya paka mota a k'ofar gidan, zai sallama sai ga Bashir zai fito daga ciki, gaisawa su ka yi cikin mutumta juna kafin yace ya wuce ciki Hajia na nan shi zai fita ne, ba musu ya wuce dan dama ba tsayawa zaiyi ba, Hajia na zaune tsakiyar less da atampopi ya sallama tace ya shigo, zaune ya yi k'asa kamar yanda ya same ta a k'asa ita ma, gaisawa su ka yi kamar kullum kafin ya d'anyi shiru ya na tunanin ta'inda zai fara, shiru ne ya ratsa d'akin kamar ba kowa a ciki, a hankali Hajia ta kalle shi da murmushi tace "Komai lafiya dai ko?"
Saida ya rarraba ido kafin yace "Mama, wani abu ne ya ke faruwa da ni da na ke so na samu amsar tambayoyi na anan, dan Hajia ta ma k'i saurara ta bare ta fad'a min me ke faruwa, dan Allah Mama ki taimaka ki fad'a min ina Khadija take? Sannan meya faru tsakani na da ita da har ya sa take zaune gida?"
Jim Mama ta yi ta na tunanin to in har iyayen shi ba su fad'a mi shi ba me zaisa ita ta fad'a, murmushi kawai ta yi ta kalle shi tace "Ba komai Usman, ka wuce ta na ciki yanzu mu ke zaune tare da ita ta shiga ta yi sallah."
Damuwar kan fuskar shi ce ta k'aru yace "Mama, dan girman Allah ki fad'a min meya faru tsakanin mu, Mama idan ma sakin ta na yi wallahi tallahi bansan na yi ba, shi ya sa na ce mu ku wani abu ne ke faruwa, gaba d'aya na kasa tuna komai ji na ke kamar daga dogon bacci na tashi."
Ganin kamar zai mata kuka ya sa ta saki fuska tace "Kar ka damu Usman, ba wata babbar matsala ba ce, ka shiga ka same ta a ciki ku yi magana, idan har ka na so ma za ka iya tafiya da matar ka gida yanzun."
Sai lokacin murmushi ya bayyana a fuskar shi yace "Mama da gaske zan iya tafiya da ita? Kai Alhamdulillah Allah na gode ma ka."
Dariya Mama ta yi ta na kallo ya shiga ciki, dama k'ofar ba rufe ta ke ba kamar yanda tafi barinta mafi yawan lokuta, ya na tura k'ofar ya shiga ya yi daidai da Khadija ta idar da sallah ta mik'e tare da cire hijabin ta, riga ce jikinta ruwan madara mai k'ananan hannuwa wacce ta kama ta, sai bak'in siket da ya bud'e sosai bai kama jikin ta ba, saida gabanta ya fad'i ganin mutum kawai a d'akin, amma kuma saita kasa motsawa saboda tasan yau ta ta kam ta k'are dan idon shi na kan cikin ta, Usman da tunda ya d'ora idon shi akan cikin ta yaji k'wak'walwar shi ta fara tuna ma sa da wasu abubuwan, mamaki ne fal a fuskar shi har ya fara matsowa kusan ta, ta na ganin haka ta fara ja da baya a hankali shi ma ya na bin ta, daf da ban d'aki ta juya da sauri za ta shige ciki da azama ya rik'o hannun ta.
Janyo hannun ta ya yi har saida ya zaunar da ita bakin gadon ya tsaya gabanta sank'am kamar zai fad'a mata ya na kallo, kan ta k'asa ta kasa had'a ido da shi kafin yace "Ya mu ka yi da ke?"
D'agowa ta yi tace "Akan me fa?"
Had'e rai ya yi yace "Kar ki raina min wayo mana, Khadija me ye hujjar ki na b'oye min ki na da ciki? Akan me za ki min haka?"
Mik'ewa ta yi tace "Kaga malam dan Allah kar ka d'aga min hankali, ni babu wani ciki da na ke da, ko kai ka ga na yi ma ka kama da masu ciki ne?"
Wani bala'in haushi ne ya taso mi shi amma sai ya share yace "Tashi wuce muje gida sai mu yi maganar acan."
"Wane gidan kuma?" Ta fad'a ta na kallon shi, kai tsaye yace "Gidan ki mana."
Wani murmushi ta yi tace "Ni ai duk filaye ne gare ni har yanzu ban gina gida ko d'aya ba."
Cile da k'aguwa yace "Haba uwar yarima, gidan mu fa na ke nufi, ki tashi mu tafi mana."
Cikin nuna rashin damuwa tace "Au! Ai wannan gidan ka ne ba nawa ba, idan da nawa ne ma ai da ba ka yi abin da ka yi ba har na baro ma ka gidan."
A hankali ya durk'usa kan gwiwoyinshi ya rik'o hannayen ta yana murzawa yace "Khadija fad'a min me na mi ki in ba ki hak'uri? Ke kinsan ba zan iya cutar da ke ba, tunda mu ke da ke ba mu tab'a samun sab'anin da yasa mu ka raba shinfid'a ba bare gida, dan Allah ki fad'a min sai na baki hak'uri yanzu kuma mu koma gida tare, sanin kan ki ne ba zan iya bacci ba alhalin ke ki na nan."
Ajiyar zuciya ta sauke tace "Ka na nufin ka ce ba ka san ma me ka min ba?"
Kamar zaiyi kuka yace "Wallahi na manta Khadija, komai ya dawo min kamar sabo a rayuwa ta." Tab'e baki ta yi tace "To kaga ka tashi dai yanzu ka koma gidan ka kafin amaryar ka ta fara neman ka."
Tsaki yaja yace "Ina mi ki magana mai mahimmanci ke ki na magana akan wata, dallah malama ki tashi ki wuce mu tafi gida."
Waro ido ta yi irin mamakin nan tace "Eyee! Lallai ma mutumin nan, to ba zan je ba ina nan gidan mu."
Ba alamar wasa yace "Haka ki ka ce?" Ita ma ba tsoro tace "Eh, haka na fad'a."
Yatsunshi ya sa biyu ya kama agarar (jijiyar da ke bayan k'afa kusa da diga-digi) ya dinga murzawa da zafi, da sauri ta janye k'afar ta sai kuwa ya rik'e k'afar ya na fad'in "Ba dai kinfi son na mi ki hukunci a gidan ba? To ai sai mu zuba ni da ke, na ga wanda ya isa ya k'wace a hannu na yau."
K'ok'arin k'watar k'afar ta ta shiga yi amma ya hanata dama, idon ta ne suka cika fal da ruwa ta na so ta bashi hak'uri amma ta k'i magana, shi kam ko a jikin shi har cije leb'e yake ya na fad'in "Uhum! Da dad'i ko? To yaya yanzu za ki fad'a min dalilin ki na k'in fad'a min ki na da ciki?"
Jin zafi ya kai mata ya sa ta bud'a baki da k'arfi tace "Mamaaaaa, ki zo ki taimake ni."
Bushewa ya yi da dariya yace "Kuma a zaton ki za ta zo? Kar ki wahalar dani a banza ki fad'a min abin da na ke son sani."
Jin bala'in na k'aruwa ya sa Khadija fashewa da kuka irin na sangartattun yaran nan ta na fad'in "Dan Allah ka yi hak'uri zan fad'a ma ka, wallahi zafi ke akwai, dan Allah ka daina zan fad'a."
D'an tsagaitawa ya yi yace "To ina jinki." Saida ta fara goge hawaye tace "To d'anyi baya mana ka matse ni sosai."
Kallon da ya mata ya sa ta d'an matsa baya amma sai ya sake binta ba tare da ya mik'e tsaye ba, shiru ta yi shi kuma ya sake kamo k'afar ta yace "Ke fa na ke saurare, muguwa kawai, da meye nufin ki to? Ban cancanci zama uban d'an ba ko kuma ke kad'ai ke da shi? Allah sai kin fad'a min dalilin ki ko na rabu da ke."
Tangale kanta ta yi da hannayen ta ta rufe fuska ta na tunani, a hankali taji ya d'an d'ago ya zauna bakin gadon ya rumgumota jikin shi, cikin taushin murya yace "Nana, ki fad'a min komai da ya faru mana, meye ake b'oye min haka da ba'a so na sani? Kowa na tambaya sai ya yi shiru ba ya son fad'a min komai."
D'agowa ta yi daga jikinshi tace "Kaje ka tambayi Hajia ko Baba su za su fad'a ma ka komai."
"Ban damu da sanin komai ba Khadija, na fi damuwa da sanin abin da ya sa ki ke zaune gida."
Tallabo fuskarta ya yi yasa idonta cikin na shi yace "Khadija me nai mi ki da zafi haka?"
Kamar za ta fashe da kuka tace "Mun samu sab'ani ne da kai akan amaryar ka, sab'anin da ya sa ka yi abin da ba ka tab'a yi ba a rayuwar ka, shine ni kuma na dawo gida gaba d'aya a lokacin ba ka buk'ata ta a gidan ka."