Sashe 42
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani dogon tsaki ya yi ya sake kara wayar shi a kunne, ta na kururuwa wayar amma ta k'i d'auka, sake maida kiran ya yi hakan ya sa mahaifin Haseenahr d'auka, dama ko da ta je gida da kuka ta isa, ta na zuwa ta k'ara fashewa da kuka wai ita wallahi ta gama auren gidan Usman, anyi tabbaya amma ta k'i fad'a saida aka kira Baban ta ya zo sannan tace "Ni kawai ba zan koma gidan shi ba, wallahi ba na bacci a cikin dare sai a dinga bani tsoro, yanzu kuma kawai..." Kuma sai ta yi shiru, mahaifin ta ne yace "Kawai me?"
Kallon shi ta yi da ido tsakar kai tace "Ba komai, ni kawai ba zan koma ba."
Ta na ganin kiran Usman a waya sai ta ture wayar wai ko sunan ma ba ta son gani, hakan ya sa iyayen jikin su yin sanyi su ka fara tunanin shiga baga ne na kishiya kawai, shine yanzu da ya kira baban ta ya d'auka, saida su ka gaisa cikin mutumci kafin yace ya zo ya same shi gida ya na son ganin shi, ba musu yace ya na nan tafe yanzun, dan shima idan bai ganta ba ba zai iya salun nutsuwa ba, Khadija na kallo ya fita daga gidan da sauri.
Ya na zuwa kam suka tattauna sosai in da Haseenah ke cewa kawai ya sake ta ba za ta koma ba, shi kam yace ba zai iya rayuwa ba yanzun babu ita, dan haka dai aka sasanta mahaifin ta yace ta je gida zai samar mata magani, haka ya d'auko ta suka dawo gida bayan ya bawa Baban ta kud'i a fara mata magani, Khadija na kallo suka dawo suka nufi b'angaren ta, ya jima ya na bata magana da rarrashi kafin ya fita, a gida ma suna tafiya mahaifin ta ya fito ya hau moton shi, bai zame ko ina ba sai *pharmacie salfiya* cibiyar magunguna na addini, da ya fad'a mu su matsalar sun zo ya zo da mara lafiyar da suga yanayin jikin ta, amma tunda ya riga ya zo sai suka bashi wanda ya dace da abin da ya fad'a, amma sunce in har ba ta daina ba to su kawo ta wajen su dan su duba ta, ya na barin nan gidan Haseenah ya wuce kai tsaye, dan suna so su d'auki matakin tunda wuri, Khadija na ganin shigowar shi amma ba ta kawo komai a ran ta ba dan bata nufin kowa da sharri, har falon Haseenah ya ke zaune ya na fad'a mata yanda za ta yi anfani da su, saida ya gama kafin ya bar gidan, Haseenah na ganin fitar shi ta kai magungunan d'aki ta aje, d'ibar wasu ta yi daga cikin wanda za ta yi anfani da su yanzun ta zubar.
Usman kuma na barin nan gidan su ya nufa, Hajia ya fad'a ma halin da ake ciki, ta jinjina al'amarin tare da dogon nazari akai, sai dai zuciyar ta ta kasa yarda cewa Khadija za ta iya cutar da ita, dan da za ta hana ta zaman gidan ai da bata ma barta ta shigo ba, amma dai "Allahu a'alam." Cewar Hajiar, ya na fita Aziza ta taso maganar dan ta na waje ta ke jin wasu maganganun, cike da damuwa Hajia ta fad'a mata yanda aka yi, ke Aziza ki na fitowa sai ki ka kira Hassana ki ka fad'a mata, kafin ka ce kwabo maganar ta karad'e yan uwan mata ana ta caccakar Khadija da maganganun b'atanci.
Yamma na yi Haseenah ta shiga madafa ta d'ora girki, sai bayan magriba ta k'arasa ta yi wanka ta shirya, ko da ya shigo ya yi wanka ya sake kaya ya zauna wajen cin abinci, kallon shi ta yi tace "Bara na kira su aunty Khadija su zo mu ci abinci."
Da ido kawai ya bita har ta fita, jim kad'an su ka shigo tare da Bilal, Khadija ba wai ta shigo bane saboda ta na son cin abinci sai dan gudun matsala, akan cinyar sh ya zaunar da Bilal in da Haseenah ta fara zuba abincin, a faranti d'aya suka fara ci shi da Bilal, amma Bilal na kai lomar farko ya kalli Haseenah ba ko k'yabtawa, da k'yar ya samu ya aika lomar ta gangara cikin shi, Khadija da Usman ma na kai wa suka yi saurin furzo shi waje suna goge baki, haka ita ma Haseenah ta na sawa ta firzo ta na ta faman goge baki, Usman ne ya kalle ta yace "Haseenah me ye haka? Kin d'and'ana girkin nan kuwa kinji?"
A marairaice ta kalle shi tace "...
*Yasin na gaji.*
11/02/2020 à 18:31 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
_*H. UMAR*, mahaifin da ya fi na kowa, ina alfahari da kai Baba na, wannan sadaukarwa ce gare ka kai kad'ai, ka cancanci fiye da ita ma, ka huta ka ju dad'in ka, Allah ya k'ara girma da lafiya dattijon arzik'i, *kut.kut.kut.*😉 kaza._
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*22*
"Wallahi bansan ya akayi gishirin nan ya yi yawa haka ba, ni fa lafiya k'alau na kammala girki na, kuma babu yanda za ayi na yi girki ban d'and'ana na ji yanda ya ke ba, sannan idan ka duba ai haka ba ta tab'a faruwa ba."
Satar kallon Khadija ya yi wacce ta kafe Haseenah da ido ta na murmushi dan ita ta fahimci me take nufi da abin da ta fad'a, girgiza kai ya yi yace "Shikenan kar ki damu, komai ya wuce."
Mik'ewa ta yi duk ta yi kalar tausayi tace "Ku yi hak'uri dan Allah, bara na samo mu ku ko soyayyen k'wai ne ku ci."
Da sauri ya katse ta da "A'a ki barshi kawai, tunda hakane ake so mu zauna, ki kawo mana madara gari da sugar kawai sai mu had'a da farar shinkafar."
Haka kam akayi taje ta kawo ta zuba a kofofi ta had'a ma kowa, ta mik'owa Khadija ta mik'e tsaye tace "Gaskiya ba na cin wannan had'in da dare, zanje na samu wani abu na ci da zai d'auke ni a wannan daren."
Kai tsaye madafa ta nufa, ba ta ji wahalar d'aukar silallan naman dake cikin masuburbud'ar sanyi ba ta had'a sassauk'an miya mai kyau da dad'i, fitowa ta yi lokacin sai Bilal da Baban shi akan salon suna kallo ta zo gaban tebur d'in ta d'ibo sabuwar shinkafar ta zuba a faranti ta zuba miyar, Bilal ne ya juyo ya kalle ta yace "Mummy ni dai na k'oshi."
"Dama bance ka zo ka ci ba." Ta fad'a ta na kai lomar farko, hankali kwance ta kammala ta tashi tace wa su je su kwanta, kallon Usman ta yi tace "Saida safe."
"Saida safe." Ya amsa ya na shafa bayan Bilal, da ido ya bisu har suka b'acewa ganin shi, ya na ganin fitar su ya taso in da ta ci abinci, ya na bud'a k'aramin kwanon miyar ya lumshe ido, cokali ya sa ya d'auko tsokar nama ya jefa bakin shi, saida ya sake lumshe ido ya na taunawa ya na fad'in "Umm, umm."
Da sauri ya d'ebo shinkafar kad'an a wani faranti ya zuba miyar ya dinga turawa saboda gudun kar Haseenah ta riske shi, har ya gama bata fito ba dan haka ya same ta d'akin ta na ta shirin bacci, nan ya fara lulawa da ita wata duniyar, sunyi nisa sosai ya na neman gangara kawai ta raba kanta da shi ta sauko daga kan gadon, ya na kallon ta kamar wasa ta canza kayan jikin ta ta saka hijab, ba tare da ya taso ba yace "Lafiya dai? sallah za ki yi ne?"
Ko kallon shi ba ta yi ba ta nufi k'ofar fita, zaune ya tashi yace "Wai lafiya? Ina za ki je haka?"
"Gidan mu." Ta fad'a ta na fita daga d'akin, da sauri ya sauko shi ma ya zura doguwar riga ya fito, ko da ya fito har ta kai farfajiyar gidan, rik'o ta ya yi yace "Haba Haseenah, ina za ki je da daran nan haka?"
Kallon shi ta yi kamar za ta yi kuka tace "Ka yi hak'uri dan Allah ka barni na tafi gidan mu, wallahi ba zan iya kai safe gidan nan ba, ni kad'ai na san me na ke ji."
A tak'aice dai haka Usman ya yi juyin duniya Haseenah tace ba za ta kwana gidan nan ba, shi kuma a ganin shi abun kunya ne ya kai ta gidan su, a cikin daren nan ya kai ta gidan su wajen Hajia, sam abun bai wa iyayen dad'i ba haka su ka kwana suna jimami, shi ma da k'yar ya dawo gidan ya kwanta, sai dai ba wani bacci ya yi ba saboda Haseenah na nesa da shi, saida asuba da yaje ya tashi Bilal sun dawo daga masallaci ya ke ce ma Khadija "Kinsan yer uwar ki ba ta kwana gidan nan ba?"
Da mamaki ta kalle shi tace "Subhanallah, me ya faru da ita? Ta na ina to?"
Wani murmushin gefen labb'a ya yi yace "Kar ki damu, gari na k'arasa wayewa zanje na d'auko ta, Haseenah za ta zauna gidan nan kamar yanda ke ma ki ke zaune."
K'ala ba tace ba har ya fita, da kan ta ta had'a mu su abin kari suka karya kafin ya fita, daga nan gida ya yi lokacin magana ta gama kewaye dangi Haseenah ta kwana gidan surukanta saboda ba ta son kwana gidan mijin, wannan kuma ba komai bane sai sharrin Khadija da ke son korarta a gidan.
Kallon shi ta yi da ido tsakar kai tace "Ba komai, ni kawai ba zan koma ba."
Ta na ganin kiran Usman a waya sai ta ture wayar wai ko sunan ma ba ta son gani, hakan ya sa iyayen jikin su yin sanyi su ka fara tunanin shiga baga ne na kishiya kawai, shine yanzu da ya kira baban ta ya d'auka, saida su ka gaisa cikin mutumci kafin yace ya zo ya same shi gida ya na son ganin shi, ba musu yace ya na nan tafe yanzun, dan shima idan bai ganta ba ba zai iya salun nutsuwa ba, Khadija na kallo ya fita daga gidan da sauri.
Ya na zuwa kam suka tattauna sosai in da Haseenah ke cewa kawai ya sake ta ba za ta koma ba, shi kam yace ba zai iya rayuwa ba yanzun babu ita, dan haka dai aka sasanta mahaifin ta yace ta je gida zai samar mata magani, haka ya d'auko ta suka dawo gida bayan ya bawa Baban ta kud'i a fara mata magani, Khadija na kallo suka dawo suka nufi b'angaren ta, ya jima ya na bata magana da rarrashi kafin ya fita, a gida ma suna tafiya mahaifin ta ya fito ya hau moton shi, bai zame ko ina ba sai *pharmacie salfiya* cibiyar magunguna na addini, da ya fad'a mu su matsalar sun zo ya zo da mara lafiyar da suga yanayin jikin ta, amma tunda ya riga ya zo sai suka bashi wanda ya dace da abin da ya fad'a, amma sunce in har ba ta daina ba to su kawo ta wajen su dan su duba ta, ya na barin nan gidan Haseenah ya wuce kai tsaye, dan suna so su d'auki matakin tunda wuri, Khadija na ganin shigowar shi amma ba ta kawo komai a ran ta ba dan bata nufin kowa da sharri, har falon Haseenah ya ke zaune ya na fad'a mata yanda za ta yi anfani da su, saida ya gama kafin ya bar gidan, Haseenah na ganin fitar shi ta kai magungunan d'aki ta aje, d'ibar wasu ta yi daga cikin wanda za ta yi anfani da su yanzun ta zubar.
Usman kuma na barin nan gidan su ya nufa, Hajia ya fad'a ma halin da ake ciki, ta jinjina al'amarin tare da dogon nazari akai, sai dai zuciyar ta ta kasa yarda cewa Khadija za ta iya cutar da ita, dan da za ta hana ta zaman gidan ai da bata ma barta ta shigo ba, amma dai "Allahu a'alam." Cewar Hajiar, ya na fita Aziza ta taso maganar dan ta na waje ta ke jin wasu maganganun, cike da damuwa Hajia ta fad'a mata yanda aka yi, ke Aziza ki na fitowa sai ki ka kira Hassana ki ka fad'a mata, kafin ka ce kwabo maganar ta karad'e yan uwan mata ana ta caccakar Khadija da maganganun b'atanci.
Yamma na yi Haseenah ta shiga madafa ta d'ora girki, sai bayan magriba ta k'arasa ta yi wanka ta shirya, ko da ya shigo ya yi wanka ya sake kaya ya zauna wajen cin abinci, kallon shi ta yi tace "Bara na kira su aunty Khadija su zo mu ci abinci."
Da ido kawai ya bita har ta fita, jim kad'an su ka shigo tare da Bilal, Khadija ba wai ta shigo bane saboda ta na son cin abinci sai dan gudun matsala, akan cinyar sh ya zaunar da Bilal in da Haseenah ta fara zuba abincin, a faranti d'aya suka fara ci shi da Bilal, amma Bilal na kai lomar farko ya kalli Haseenah ba ko k'yabtawa, da k'yar ya samu ya aika lomar ta gangara cikin shi, Khadija da Usman ma na kai wa suka yi saurin furzo shi waje suna goge baki, haka ita ma Haseenah ta na sawa ta firzo ta na ta faman goge baki, Usman ne ya kalle ta yace "Haseenah me ye haka? Kin d'and'ana girkin nan kuwa kinji?"
A marairaice ta kalle shi tace "...
*Yasin na gaji.*
11/02/2020 à 18:31 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
_SAMIRA HAROUNA_
*Litattafan marubuciyar*
*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._
*SADAUKARWA GA*
_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*
🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛
_*H. UMAR*, mahaifin da ya fi na kowa, ina alfahari da kai Baba na, wannan sadaukarwa ce gare ka kai kad'ai, ka cancanci fiye da ita ma, ka huta ka ju dad'in ka, Allah ya k'ara girma da lafiya dattijon arzik'i, *kut.kut.kut.*😉 kaza._
```Fatan alkairi masoya```
_Bismillahir rahamanir rahim_
*22*
"Wallahi bansan ya akayi gishirin nan ya yi yawa haka ba, ni fa lafiya k'alau na kammala girki na, kuma babu yanda za ayi na yi girki ban d'and'ana na ji yanda ya ke ba, sannan idan ka duba ai haka ba ta tab'a faruwa ba."
Satar kallon Khadija ya yi wacce ta kafe Haseenah da ido ta na murmushi dan ita ta fahimci me take nufi da abin da ta fad'a, girgiza kai ya yi yace "Shikenan kar ki damu, komai ya wuce."
Mik'ewa ta yi duk ta yi kalar tausayi tace "Ku yi hak'uri dan Allah, bara na samo mu ku ko soyayyen k'wai ne ku ci."
Da sauri ya katse ta da "A'a ki barshi kawai, tunda hakane ake so mu zauna, ki kawo mana madara gari da sugar kawai sai mu had'a da farar shinkafar."
Haka kam akayi taje ta kawo ta zuba a kofofi ta had'a ma kowa, ta mik'owa Khadija ta mik'e tsaye tace "Gaskiya ba na cin wannan had'in da dare, zanje na samu wani abu na ci da zai d'auke ni a wannan daren."
Kai tsaye madafa ta nufa, ba ta ji wahalar d'aukar silallan naman dake cikin masuburbud'ar sanyi ba ta had'a sassauk'an miya mai kyau da dad'i, fitowa ta yi lokacin sai Bilal da Baban shi akan salon suna kallo ta zo gaban tebur d'in ta d'ibo sabuwar shinkafar ta zuba a faranti ta zuba miyar, Bilal ne ya juyo ya kalle ta yace "Mummy ni dai na k'oshi."
"Dama bance ka zo ka ci ba." Ta fad'a ta na kai lomar farko, hankali kwance ta kammala ta tashi tace wa su je su kwanta, kallon Usman ta yi tace "Saida safe."
"Saida safe." Ya amsa ya na shafa bayan Bilal, da ido ya bisu har suka b'acewa ganin shi, ya na ganin fitar su ya taso in da ta ci abinci, ya na bud'a k'aramin kwanon miyar ya lumshe ido, cokali ya sa ya d'auko tsokar nama ya jefa bakin shi, saida ya sake lumshe ido ya na taunawa ya na fad'in "Umm, umm."
Da sauri ya d'ebo shinkafar kad'an a wani faranti ya zuba miyar ya dinga turawa saboda gudun kar Haseenah ta riske shi, har ya gama bata fito ba dan haka ya same ta d'akin ta na ta shirin bacci, nan ya fara lulawa da ita wata duniyar, sunyi nisa sosai ya na neman gangara kawai ta raba kanta da shi ta sauko daga kan gadon, ya na kallon ta kamar wasa ta canza kayan jikin ta ta saka hijab, ba tare da ya taso ba yace "Lafiya dai? sallah za ki yi ne?"
Ko kallon shi ba ta yi ba ta nufi k'ofar fita, zaune ya tashi yace "Wai lafiya? Ina za ki je haka?"
"Gidan mu." Ta fad'a ta na fita daga d'akin, da sauri ya sauko shi ma ya zura doguwar riga ya fito, ko da ya fito har ta kai farfajiyar gidan, rik'o ta ya yi yace "Haba Haseenah, ina za ki je da daran nan haka?"
Kallon shi ta yi kamar za ta yi kuka tace "Ka yi hak'uri dan Allah ka barni na tafi gidan mu, wallahi ba zan iya kai safe gidan nan ba, ni kad'ai na san me na ke ji."
A tak'aice dai haka Usman ya yi juyin duniya Haseenah tace ba za ta kwana gidan nan ba, shi kuma a ganin shi abun kunya ne ya kai ta gidan su, a cikin daren nan ya kai ta gidan su wajen Hajia, sam abun bai wa iyayen dad'i ba haka su ka kwana suna jimami, shi ma da k'yar ya dawo gidan ya kwanta, sai dai ba wani bacci ya yi ba saboda Haseenah na nesa da shi, saida asuba da yaje ya tashi Bilal sun dawo daga masallaci ya ke ce ma Khadija "Kinsan yer uwar ki ba ta kwana gidan nan ba?"
Da mamaki ta kalle shi tace "Subhanallah, me ya faru da ita? Ta na ina to?"
Wani murmushin gefen labb'a ya yi yace "Kar ki damu, gari na k'arasa wayewa zanje na d'auko ta, Haseenah za ta zauna gidan nan kamar yanda ke ma ki ke zaune."
K'ala ba tace ba har ya fita, da kan ta ta had'a mu su abin kari suka karya kafin ya fita, daga nan gida ya yi lokacin magana ta gama kewaye dangi Haseenah ta kwana gidan surukanta saboda ba ta son kwana gidan mijin, wannan kuma ba komai bane sai sharrin Khadija da ke son korarta a gidan.