Sashe 82
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da k'yar tace "Na tabbata." Mik'ewa ya yi yace "Shikenan, amma dan Allah da kinji wani abu ki yi magana tun da wuri."
Komai ba tace ma sa ba har Hajia ta same su tare da malam da ya kawota, kamar dama jiran zuwan Hajia ake sai ko ga wata likita ta fito ta kalli Usman tace "Alhamdulillah ta haihu lafiya, an samu d'iya mace."
"Alhamdulillah." Suka fad'a kusan a tare, nan akayi duk abin da ya kamata wanda suke buk'ata, lokacin dare ya yi sosai Hajia tace Usman ya koma gida da Khadija ita za ta zauna wajen su, ba b'ata lokaci suka kama hanyar gida Khadija sai gyangyad'i take, kallon ta ya yi ya na murmushi yace "Hajia wane suna ki ka zab'a da za'a sawa 'yar ta ki?"
Cikin doguwar hamma tace "Ka tambayi maman ta mana, watak'ila ta na da sunan da take sha'awa ita ma."
Wani kallo ya mata yace "Ta na da wata uwa ce da ta wuce ki a duniyar nan?" Cike da kasala tace "To idan da hali a saka mata *Nana Aisha* kaga idan na haihu nan kusa nima munyi 'yan biyu kenan sai a saka mata *Humaira*."
Cikin murmushi yace "Idan kuma namiji ki ka sake sunkuto min fa." Cikin zolaya tace "Sai ka saka masa *Humair*."
"To amma..." Da sauri ta katse shi tace "Dan Allah ka rabu da ni bacci na ke ji." Dariya ya yi yace "To idan ki ka yi bacci a motar fa?"
Kai tsaye tace "Saika d'auke ni ka kwantar da ni akan gadon ka."
Wani kallo ya mata yace "Me ya sa sai a kan gado na?"
"Saboda ina so haihuwa ta same ni akan gadon." Marairaicewa ya yi yace "Yanzu ku saboda Allah haka za ku had'e min kai ku haihu lokaci d'aya, kenan dole nima sai na yi jego kamar ku."
Dariya Khadija ta dinga shek'awa har da rik'e ciki kafin tace "Ai daidai kenan, kaga kai ma sai ka nemi k'unzugu ka aje saboda tarban jinin bik'i."
Kamar zaiyi kuka yace "Allah ni dai ban yarda ba, babu wani jego da zanyi haka kawai da raina da lafiya ta, dole kisan dubarar da za ki dinga min saboda na gujewa abkawa jego."
Hararan shi ta yi tace "Saboda ni kad'ai ce ke da kai?"
Saida ya kashe mata ido yace "Amma ai ke dabance, ke kad'ai ce ki ka iyani yanda ya kamata, ke ki ka fi kowa sanin abin da na ke so da abin da na ke da buk'ata."
Ba tace komai ba har suka isa gida rabe ya bud'e mu su k'ofa suka shiga, sun samu Bilal na baccin shi kamar yanda suka bar shi, nan suka kwanta suma bacci cike da gajiya, sam Khadija ba ta yi tsammanin gari zai waye ba ta haihu ba saboda abin da take ji, amma sai gashi ta tashi cikin k'arfin jiki, tunda asuba ta had'a kyakyawan abin karin kumallo sannan ta shirya, haka Bilal ma ya shirya Usman ma kafin suka karya na su kumallo abin da basu saba ba kari tunda safiya, asibiti suka tafi sun samu iyayen Haseenah da kuma Mariya, bayan sun gaisa suke mata godiya akan kayan ta da ta bayar Haseenah ta yi aiki da su, nan Usman ya zauna kuda da Haseenah ya kalle ta yace "Mai jego wai wane suna ki ka zab'awa 'yar ta ki ne?"
Kunya ce ta kama Haseenah ta rufe fuska da hijabi, dariya ya yi yace "Ki fad'a mana, dan ni zan iya saka mi ki sunan tsofaffi kamar sunan su Hajia."
Hajia ce tace "Sunan na mu ne na tsofi kenan? To aiko in ka yi wasa sunan Hajiar (mahaifiyar Haseenah) za'a saka mata."
Dariya ya yi ya kalli Hajia a ran shi kuma yace "Asiya." Mahaifiyar Haseenahr ce tace "Ko kuma sunan ki ba, ai yafi nawa."
Na kuma Haseenah ce ta kalli Hajia a ran ta ita ma tace "Allah ya sa kar ya sawa 'yata sunan mahaifiyar shi, *Hawa'u* ai sunan da ne."
Jin dai su na ta cecekuce ya sa tace "Kawai tambayi mahaifiyar ta wane suna ta ke so?" Ta fad'a da nuna Khadija, kallon ta Khadija ta yi tace "Ni kuma?"
"K'warai aunty Khadija, babu wanda ya dace ya saka mata suna bayan ke, a sanadiyar ki ta samu gatan da aka haifeta gidan mahaifin ta, dan haka kawai ki zab'a mata sunan da ya mi ki."
Murmushi Khadija ta yi tace "To shikenan a saka mata Aisha, sai ku tayani addu'a Allah ya sa na haifi mace sai a saka mata Humaira, kunga sun zama 'yan biyu kenan, Aisha da Humaira."
Kowa ya ji dad'in abin da ya faru, haka aka sawa yarinya Aisha tare da sa mata albarka, su kuma aka bisu da addu'a k'ara had'a kan su, nan Usman ya wuce da Bilal makaranta, zuwa k'arfe takwas ko da aka kama aiki aka sallame su, amma ba su bar asibitin ba har sai kusan k'arfe tara kafin Usman ya aiko Bilyamin ya d'auke su, tunda Bilal ya dawo ya ke b'angaren Haseenah ya na lagudar yarinyar, wani iko na ubangiji sai yarinyar ta yi kama da Bilal d'in kamar ciki d'aya suka fito, duk mutanen da ke zuwa wajen Bilal bai bar wajen ba, Khadija ta yi mamaki sosai yaron da ba ya son hayaniya da taron jama'a, amma sai gashi ya wuni zigidir wajen Haseenah har saida yamma lokacin islamiyya ya yi kad'ai ya bar wajen.
Sosai yan uwan Khadija da abokan ta suka mata kara wajen zuwa yi wa Haseenah barka, sai dai Hajia Turai ta rantse ta maya kan ba za ta zo ba sai in Khadija ta haihu, to fa ranar za ta zo gidan ko me zai faru sai dai ya faru, a lokacin kuma Khadija ta nemi da Usman ya mata izini taje ta dawo da Uwani ko dan aikin da ke tunkaro su ta na buk'atar mai taimako, ba musu ya mata izini ta tafi tare da Bilal, ba ta sha wahalar shawo kan su ba saboda dama ba laifin ta bane, nan suka dawo tare da su aka d'ora daga in da aka tsaya.
Sosai Khadija ke kama girmanta wajen ganin ta sauke nauyin da Usman ya d'ora mata, kowace safiya kafin Haseenah ta fito daga wanka za ta samu abin karyawarta yana jiran ta, da rana kuma idan su Mariya su ka zo tare suke aikin rana cikin raha da annashuwa, haka za su dinga cewa ta zauna ta huta za su yi amma sai tace a'a, haka suke girkin rana da na dare tare, kuma sosai suke k'aruwa wajen koyan girkin, dan kwana uku da akayi da haihuwar kullum akwai abin da ake girkawa, a haka aka shiga kwana na hud'u, a lokacin sosai Khadija take jin jikin ta fa ba dad'i amma ta na daurewa ne, yau dai ko da suka gama girkin rana ta shiga d'akin ta ba ta fito ba, saida Uwani taga abin ya fara tsananta ta fito ta nemi taimakon mutane dan su tafi asibiti, Hassana da su Rabi'a na gidan a lokacin su ka taho dan ganin lafiya, d'aki suka same ta kwance sai nishi take ta na ware k'afafun ta saboda tasan haihuwarta kusa take, nan suka duk'ufa aka taimaka mata, leda aka shinfid'a akan gadon suka fara karb'ar haihuwa, ai kuwa ba jimawa sai kan yarinya ya lek'o duniya, suna k'arasa jawo ta sai ta fashe da kukan da ya sa Usman da ya taho hankali tashe lokacin da Bilal ya kira shi ya tsaya cak, rufe fuska ya yi kafin ya bud'e ya na dariya mai kama da kuka, d'aukar Bilal ya yi ya na juyawa da shi cikin farin ciki.
Nan su Hassana su ka fito da yarinyar suka bashi ya karb'a, ya na kallon ta ya ji wata muguwar k'aunar yarinyar saboda sak Khadija ya ke ganin fuskarta, yan uwa fad'an irin bidirin da ake ma b'ata lokaci ne, Khadija dai ga farin jinin mutane gashi haihuwar ta zama biyu, hakan ya sa kullum gidan kamar ranar ake biki, kuma an mayar da bikin rana d'aya ma'ana ranar da Khadija ta haihu, a k'alla mutanen da ke zuwa gidan basa irguwa kuma mafi aksari mutanen Khadija ne, shirye shirye ake sosai in da k'awayen Khadija su ka yi anko har kala biyar saboda farin ciki, kuma babu wanda Usman baiwa Khadija da Haseenah ba, dan ma Khadija ta yi wa kan ta dayawa da bai sani ba, a lokacin kuma Khadija ta tuna da ranar bikin ya yi daidai da zagayowar ranar haihuwar Usman, wanda shekarun su ka kama *arba'in da biyar*, dan haka ta fad'awa k'awayen ta su kaltume cewa ta na so ta mi shi bazata, nan aka fara wani sabon shirin dan bashi mamaki, in da ba kowa ya sani ba daga yan uwan Usman maza da mata, sai yan uwan Khadija da na Haseenah, sai kuma abokan Usman d'in wanda aka gayyata.
*Rana bata k'arya* sai dai uwar d'iya ta ji kunya, yau akayi suna kuma yara sun ci sunan da uwarsu ta zab'a musu wato *Aisha* da *Humaira*, duk girman gidan Usman sai gashi ya kasa d'aukar mutanen da ke wajen har saida aka had'a da wasu runfa har biyu a k'ofar gida, duk wanda ya zo sai yace masha Allah saboda taron jama'ar, kuma kashi uku a cikin hud'u duk na Khadija ne, ita ma kuma hakan ya faru ne sakamakon jimawa da tayi ba ta haihu ba, Usman yayi iya k'ok'arin shi wajen samarwa mutanen abinci da abin sha, inda aka yanka manyan shanu har guda biyu, a b'angaren Khadija kuma shiga kawai take ta na sakewa, duk da Usman ya musu d'inki iri d'aya kuma yawa d'aya amma saida kaltume da Hajia Turai suka sake mata wani d'inki, ita kanta ba ta sani ba sai ana gobe bikin kad'ai suka kawo mata su, yawan taron jama'a ya sa muryar Khadija dishewa ta shak'e ba'a ji saidai ta d'aga hannu kawai.
Komai ba tace ma sa ba har Hajia ta same su tare da malam da ya kawota, kamar dama jiran zuwan Hajia ake sai ko ga wata likita ta fito ta kalli Usman tace "Alhamdulillah ta haihu lafiya, an samu d'iya mace."
"Alhamdulillah." Suka fad'a kusan a tare, nan akayi duk abin da ya kamata wanda suke buk'ata, lokacin dare ya yi sosai Hajia tace Usman ya koma gida da Khadija ita za ta zauna wajen su, ba b'ata lokaci suka kama hanyar gida Khadija sai gyangyad'i take, kallon ta ya yi ya na murmushi yace "Hajia wane suna ki ka zab'a da za'a sawa 'yar ta ki?"
Cikin doguwar hamma tace "Ka tambayi maman ta mana, watak'ila ta na da sunan da take sha'awa ita ma."
Wani kallo ya mata yace "Ta na da wata uwa ce da ta wuce ki a duniyar nan?" Cike da kasala tace "To idan da hali a saka mata *Nana Aisha* kaga idan na haihu nan kusa nima munyi 'yan biyu kenan sai a saka mata *Humaira*."
Cikin murmushi yace "Idan kuma namiji ki ka sake sunkuto min fa." Cikin zolaya tace "Sai ka saka masa *Humair*."
"To amma..." Da sauri ta katse shi tace "Dan Allah ka rabu da ni bacci na ke ji." Dariya ya yi yace "To idan ki ka yi bacci a motar fa?"
Kai tsaye tace "Saika d'auke ni ka kwantar da ni akan gadon ka."
Wani kallo ya mata yace "Me ya sa sai a kan gado na?"
"Saboda ina so haihuwa ta same ni akan gadon." Marairaicewa ya yi yace "Yanzu ku saboda Allah haka za ku had'e min kai ku haihu lokaci d'aya, kenan dole nima sai na yi jego kamar ku."
Dariya Khadija ta dinga shek'awa har da rik'e ciki kafin tace "Ai daidai kenan, kaga kai ma sai ka nemi k'unzugu ka aje saboda tarban jinin bik'i."
Kamar zaiyi kuka yace "Allah ni dai ban yarda ba, babu wani jego da zanyi haka kawai da raina da lafiya ta, dole kisan dubarar da za ki dinga min saboda na gujewa abkawa jego."
Hararan shi ta yi tace "Saboda ni kad'ai ce ke da kai?"
Saida ya kashe mata ido yace "Amma ai ke dabance, ke kad'ai ce ki ka iyani yanda ya kamata, ke ki ka fi kowa sanin abin da na ke so da abin da na ke da buk'ata."
Ba tace komai ba har suka isa gida rabe ya bud'e mu su k'ofa suka shiga, sun samu Bilal na baccin shi kamar yanda suka bar shi, nan suka kwanta suma bacci cike da gajiya, sam Khadija ba ta yi tsammanin gari zai waye ba ta haihu ba saboda abin da take ji, amma sai gashi ta tashi cikin k'arfin jiki, tunda asuba ta had'a kyakyawan abin karin kumallo sannan ta shirya, haka Bilal ma ya shirya Usman ma kafin suka karya na su kumallo abin da basu saba ba kari tunda safiya, asibiti suka tafi sun samu iyayen Haseenah da kuma Mariya, bayan sun gaisa suke mata godiya akan kayan ta da ta bayar Haseenah ta yi aiki da su, nan Usman ya zauna kuda da Haseenah ya kalle ta yace "Mai jego wai wane suna ki ka zab'awa 'yar ta ki ne?"
Kunya ce ta kama Haseenah ta rufe fuska da hijabi, dariya ya yi yace "Ki fad'a mana, dan ni zan iya saka mi ki sunan tsofaffi kamar sunan su Hajia."
Hajia ce tace "Sunan na mu ne na tsofi kenan? To aiko in ka yi wasa sunan Hajiar (mahaifiyar Haseenah) za'a saka mata."
Dariya ya yi ya kalli Hajia a ran shi kuma yace "Asiya." Mahaifiyar Haseenahr ce tace "Ko kuma sunan ki ba, ai yafi nawa."
Na kuma Haseenah ce ta kalli Hajia a ran ta ita ma tace "Allah ya sa kar ya sawa 'yata sunan mahaifiyar shi, *Hawa'u* ai sunan da ne."
Jin dai su na ta cecekuce ya sa tace "Kawai tambayi mahaifiyar ta wane suna ta ke so?" Ta fad'a da nuna Khadija, kallon ta Khadija ta yi tace "Ni kuma?"
"K'warai aunty Khadija, babu wanda ya dace ya saka mata suna bayan ke, a sanadiyar ki ta samu gatan da aka haifeta gidan mahaifin ta, dan haka kawai ki zab'a mata sunan da ya mi ki."
Murmushi Khadija ta yi tace "To shikenan a saka mata Aisha, sai ku tayani addu'a Allah ya sa na haifi mace sai a saka mata Humaira, kunga sun zama 'yan biyu kenan, Aisha da Humaira."
Kowa ya ji dad'in abin da ya faru, haka aka sawa yarinya Aisha tare da sa mata albarka, su kuma aka bisu da addu'a k'ara had'a kan su, nan Usman ya wuce da Bilal makaranta, zuwa k'arfe takwas ko da aka kama aiki aka sallame su, amma ba su bar asibitin ba har sai kusan k'arfe tara kafin Usman ya aiko Bilyamin ya d'auke su, tunda Bilal ya dawo ya ke b'angaren Haseenah ya na lagudar yarinyar, wani iko na ubangiji sai yarinyar ta yi kama da Bilal d'in kamar ciki d'aya suka fito, duk mutanen da ke zuwa wajen Bilal bai bar wajen ba, Khadija ta yi mamaki sosai yaron da ba ya son hayaniya da taron jama'a, amma sai gashi ya wuni zigidir wajen Haseenah har saida yamma lokacin islamiyya ya yi kad'ai ya bar wajen.
Sosai yan uwan Khadija da abokan ta suka mata kara wajen zuwa yi wa Haseenah barka, sai dai Hajia Turai ta rantse ta maya kan ba za ta zo ba sai in Khadija ta haihu, to fa ranar za ta zo gidan ko me zai faru sai dai ya faru, a lokacin kuma Khadija ta nemi da Usman ya mata izini taje ta dawo da Uwani ko dan aikin da ke tunkaro su ta na buk'atar mai taimako, ba musu ya mata izini ta tafi tare da Bilal, ba ta sha wahalar shawo kan su ba saboda dama ba laifin ta bane, nan suka dawo tare da su aka d'ora daga in da aka tsaya.
Sosai Khadija ke kama girmanta wajen ganin ta sauke nauyin da Usman ya d'ora mata, kowace safiya kafin Haseenah ta fito daga wanka za ta samu abin karyawarta yana jiran ta, da rana kuma idan su Mariya su ka zo tare suke aikin rana cikin raha da annashuwa, haka za su dinga cewa ta zauna ta huta za su yi amma sai tace a'a, haka suke girkin rana da na dare tare, kuma sosai suke k'aruwa wajen koyan girkin, dan kwana uku da akayi da haihuwar kullum akwai abin da ake girkawa, a haka aka shiga kwana na hud'u, a lokacin sosai Khadija take jin jikin ta fa ba dad'i amma ta na daurewa ne, yau dai ko da suka gama girkin rana ta shiga d'akin ta ba ta fito ba, saida Uwani taga abin ya fara tsananta ta fito ta nemi taimakon mutane dan su tafi asibiti, Hassana da su Rabi'a na gidan a lokacin su ka taho dan ganin lafiya, d'aki suka same ta kwance sai nishi take ta na ware k'afafun ta saboda tasan haihuwarta kusa take, nan suka duk'ufa aka taimaka mata, leda aka shinfid'a akan gadon suka fara karb'ar haihuwa, ai kuwa ba jimawa sai kan yarinya ya lek'o duniya, suna k'arasa jawo ta sai ta fashe da kukan da ya sa Usman da ya taho hankali tashe lokacin da Bilal ya kira shi ya tsaya cak, rufe fuska ya yi kafin ya bud'e ya na dariya mai kama da kuka, d'aukar Bilal ya yi ya na juyawa da shi cikin farin ciki.
Nan su Hassana su ka fito da yarinyar suka bashi ya karb'a, ya na kallon ta ya ji wata muguwar k'aunar yarinyar saboda sak Khadija ya ke ganin fuskarta, yan uwa fad'an irin bidirin da ake ma b'ata lokaci ne, Khadija dai ga farin jinin mutane gashi haihuwar ta zama biyu, hakan ya sa kullum gidan kamar ranar ake biki, kuma an mayar da bikin rana d'aya ma'ana ranar da Khadija ta haihu, a k'alla mutanen da ke zuwa gidan basa irguwa kuma mafi aksari mutanen Khadija ne, shirye shirye ake sosai in da k'awayen Khadija su ka yi anko har kala biyar saboda farin ciki, kuma babu wanda Usman baiwa Khadija da Haseenah ba, dan ma Khadija ta yi wa kan ta dayawa da bai sani ba, a lokacin kuma Khadija ta tuna da ranar bikin ya yi daidai da zagayowar ranar haihuwar Usman, wanda shekarun su ka kama *arba'in da biyar*, dan haka ta fad'awa k'awayen ta su kaltume cewa ta na so ta mi shi bazata, nan aka fara wani sabon shirin dan bashi mamaki, in da ba kowa ya sani ba daga yan uwan Usman maza da mata, sai yan uwan Khadija da na Haseenah, sai kuma abokan Usman d'in wanda aka gayyata.
*Rana bata k'arya* sai dai uwar d'iya ta ji kunya, yau akayi suna kuma yara sun ci sunan da uwarsu ta zab'a musu wato *Aisha* da *Humaira*, duk girman gidan Usman sai gashi ya kasa d'aukar mutanen da ke wajen har saida aka had'a da wasu runfa har biyu a k'ofar gida, duk wanda ya zo sai yace masha Allah saboda taron jama'ar, kuma kashi uku a cikin hud'u duk na Khadija ne, ita ma kuma hakan ya faru ne sakamakon jimawa da tayi ba ta haihu ba, Usman yayi iya k'ok'arin shi wajen samarwa mutanen abinci da abin sha, inda aka yanka manyan shanu har guda biyu, a b'angaren Khadija kuma shiga kawai take ta na sakewa, duk da Usman ya musu d'inki iri d'aya kuma yawa d'aya amma saida kaltume da Hajia Turai suka sake mata wani d'inki, ita kanta ba ta sani ba sai ana gobe bikin kad'ai suka kawo mata su, yawan taron jama'a ya sa muryar Khadija dishewa ta shak'e ba'a ji saidai ta d'aga hannu kawai.