Sashe 2
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushin gefen labb'a ya yi yace "Na riga da na yanke hukunci, na san kin amince ne saboda kawai ki faranta min rai, ni kuma ba na son tursasaki a kan abin da ba kya so, dan haka ya wuce kawai."
Da sauri ta gyara zama ta na fuskantar shi tace "Haba aljanna ta, ni fa na ce na amince, wallahi babu takura a ciki, wani k'aramin rashin fahimta ne, kuma sai ga shi cikin ikon Allah fasihi kuma nagartattacen miji na ya fahimtar da ni, dan haka in ba so ka ke na maka kuka ba kawai ka amince."
Yanda ta k'arashe maganar cikin shagwab'a ya birge shi, dan haka ya rumgumo ta jikin shi ya na dariya, cikin so da k'auna ya ci gaba da rarrashin ta tare da saka mata albarka, tambayar ta ya yi "To yanzu ina so ki fad'a min duk abin da ki ke buk'ata, ni kuma insha Allah zanyi mi ki shi a matsayin tukuici da kuma fad'an kishiya."
Kasancewar ta mace mai yawan shagwab'a da son jiki ya sa ta turo baki gaba ta kwanta a kafad'ar shi tace "Kaji ka da wata magana, ai ni yanzu ba kai ne za ka min hidima ba, ni ce ma zan bayar da tawa gudunmuwar."
"Ban yarda ba, sai kin fad'a, in ba haka ba kuma zan kama ki ne."
Yanda ya yi maganar cikin sigar rausaya ya sa ta tashi ta nufi d'akin ta ta na fad'in "Na k'i wayon, ka kamani d'in."
Ya na jin haka ya tashi da gudu ya nufe ta, ita ma a guje ta k'arasa shiga d'akin, kasancewar Bilal na wajen kakannin shi (iyayen Khadija) ya sa su ka saki jiki sosai su ka more rayuwar su, dan dama kusan kullum haka su ke.
*Washe gari* kamar kullum misalin *09:30* su ka gama shirin fita, har farfajiyar gida su ka isa tare, ita ma kuma cikin shirin fita ta ke, sai da ya shafi lallausan kumatun ta tare da sumbatar ta kafin yace "Ni zan wuce, ki kula min da kan ki, sannan ki gaishe min da su Mama, tun da ba za ki bani damar da zan kai ki da kai na ba bare na gaishe su."
Masha Allah, duk da cikin gilashi ne ta waina idon ta, amma bai hana su d'aukar hankalin Usman ba, saboda girman idon da kuma farin su tamkar madara, cikin wasa da idon ta ne tace "Na shiga uku, da alama sai an shekara d'ari ka na min gorin wannan maganar."
"Ai dole ne, dan na lura kamar ba kya so na je na kwaso albarka wajen Mama, sannan na sake mata godiya da ta bani ke."
"Gashi kuma ba kya gajiya da godiya kullum."
"Ni kam ina zan gaji da godiya, duk wanda ya baka yar sa ka aura ai ya gama ma ka komai, bare kuma mata irin ki Khadija, ai har duniya ta nad'e ba zan daina mu su godiya ba wallahi, dan na san sun fini sanin ki, amma kuma hakan bai hana su ka rabu da ke ba su ka bani ke, duk da kuwa sun san ba zan tab'a rabuwa da ke ba in ba mutuwa ce ta raba mu ba."
Ajiyar zuciya ta sauke tace "Idan har na biye ma ka, to hak'ik'a zan tabbata anan ban tafi in da zan je ba, dan haka sai an jima, nima ka gaishe min da Mama na da Abba na, tun da ka k'i bani damar bin ka bare na gaishe su."
Ta na fad'a ta juya ta na dariya shi kuma ya na fad'in "Au! Ramawa ki ka yi? Shikenan ai zan kama ki."
Gwalo ta masa tace "Ka kamani d'in, kafin nan na san in da na kai."
Wata tsandareriyar mota ta shiga bla (bleue) shi ma haka, sai dai ta shi bak'a ce, kowa hanyar da za ta sada shi da na shi iyayen ya nufa, dan su dama a *zarya* su ke, bayan masallacin *sahaba*, Khadija gaba ta yi saboda gidan su na gaban sabon gidan mota na *Rimbo*, shi kuma Usman gidan iyayen shi ya na nan *sabon gari* a 'yan *banana* (🤸♂aradu unguwar mu).
Ko da ya isa mahaifiyar shi kad'ai ya samu a gidan, dan haka su na gaisawa ya d'auko maganar auren shi, tambayar da ta fara mi shi ita ce "Khadija ta sani?"
"Eh Mama, ta sani, kuma ta bada goyon bayan ta d'ari bisa d'ari, yanzu amincewar ku na ke buk'ata."
Cike da kamala tsohuwar tace "Ba ka da matsala da amincewar mu *Fodio* (sunan mahaifin ta ne, dan haka ta ke ma sa inkiya da Fodio), tun da dai har ka shirya, kuma ka na ganin ba wata matsala, sannan matar ka ma ta amince ba tare da tashin hankali ba, ai ka ga Alhamdulillah, sai dai kawai mu bika da addu'a da kuma fatan alkairi."
"Nagode sosai Mama, Allah ya k'ara lafiya da girma, yanzu kenan idan Abba ya shigo za ku iya magana da su, duk yanda ku ka yi zuwa dare idan na dawo na ji insha Allah."
Kasantuwar shi d'an fari ya sa ko ido ba ta son had'awa da shi kamar ta na jin kunyar shi, ba tare da ta kalle shi ba tace "Shikenan ba damuwa, insha Allah zan fad'a ma sa."
D'an gyara zama ya yi alamar zai tashi yace "Mama babu wata matsala ko wani abun da ku ke buk'ata?"
"Ah, Fodio kai ne za ka bar gidan nan da wata matsala? Ai sai dai in ba ka raye, Alhamdulillah wallahi babu komai, Allah dai ya yi albarka, Allah ya sa ka gama da duniya lafiya."
Sai da ya durk'usa k'asa ya amsa da "Ameen Ameen Mama, nagode sosai da addu'ar ki gare ni, ni zan wuce sai anjima idan na dawo."
"To Allah ya yarda, Allah ya tsare, ka gaishe min da waccen mutumin."
Dariya ya yi yace "Watak'ila fa gobe ku gan shi gidan nan, dan mahaifiyar shi ta tafi d'auko shi."
Cikin wasa irin ta kaka da jika tace "Ka ce mi shi ma kar ya kuskura ya zo in har ya san ba zai taho da k'atuwar bak'ar leda ba."
"Zai zo da ita Mama, ai kin san shi da k'ok'arin cefanai."
"Ko dai k'ok'arin jefawa a ciki ba."
Da wannan wasan ya bar gidan zuciyar shi sakayau da ita kamar kullum, dan har abada babu abin da ke dagula mi shi lissafi, b'angaren mace, Allah ya wadata shi da mata kamar Khadija, babu abin da ya nema a gurin ta ya rasa, haka ma iyaye, Allah ya bashi iyayen da su ke son abin da ya ke so, sannan su ke nusar da shi tare da kora shi da addu'a a kullum, hakan na sa shi farin ciki , kuma shima ya na k'ok'ari sosai wajen sauke hakk'ok'in duka b'angarorin, haka ne m'a sanadiyar da ta sa kullum ci gaba ya ke gani babu komawa baya ko rashin nasara, dan Allah ba ya kunyatar ko tab'ar da wanda ya kiyaye hakk'ok'in wannan mutanen a duniya.
Khadija ma a gidan su farin ciki ta ke kamar ba ta farin ciki a gidan ta, hakan kuma ya samo asali ne sakamakon samun kan ta da ta yi a tsakiyar mahaifiyar ta da kuma d'an ta, sai sauran matan yayyun ta da kuma 'ya'yan su, bayan sun ci abincin rana yan uwan ta maza su uku su ka shigo gidan, anan ta tara su kuma ta fad'a mu su auren da mijin ta zaiyi, ta gaggauta fad'a mu su hakane saboda ta san sune za su iya bata shawara mai kyau wacce ta dace, kuma kamar yanda ta yi tsammani hakane ya faru, sosai su ka kwantar mata da hankali tare ja mata kunne da nasihohi ma su shiga rai, tare da kafa mata misali da matar babban yayan ta wanda da zai k'ara aure ta tashi hankalin kowa, a k'arshe dai sai da ta bar gidan, yanzu gashi nan sai amaryar ke rayuwar ta a b'angaren na su, abin da ba ta son ganin shi ke faruwa a bayan idon ta kuma ba yanda za ta yi, ga yayan ta ma su na hannun uban su sai yaga dama ya ke barin su su je wajen uwar, saboda hure mu su kunne da ta ke, hakan ya k'ara saka jikin Khadija yin sanyi, kuma ta yi niyyar yin aiki da shawarwarin da su ka bata, a haka ita ma ta yi yammacin ta tare da maman ta abar k'aunar ta, zuwa *5:30* na yamma kuma Bilal ya d'auki kayan shi su ka wuce tare da maman shi a motar ta.
Su na isa gida Bilal ya wuce da yan kayan shi d'akin shi tare da canza na jikin shi, ita ma kaya ta sauya ta wuce madafa dan sarrafa abin da za su ci da dare, tare da Bilal su ka shiga ya na kama mata duk aikin da ta ke yi, sai da aka gama sallah magrib ta gama lokacin Bilal ya wuce masallacin da ke had'e da gidan su, ta na gama ajewa a mazaunin cin abinci ta yi wanka ta shirya cikin riga da zane wanda su ka d'auke jikin ta sosai, kasancewar babu wata tazara mai tsayi tsakanin sallah magrib da isha'i ya sa ta yi sallahn ta, ta na kammalawa ta fito falon ya yi daidai da shigowar Bilal daga masallaci tare da baban shi.
Ta na ganin shi ta tashi tsaye ta turo baki tace "Sai yanzu za ka dawo min gida? Ina ka shige haka?"
Kallon Bilal ya yi yace "Yau salon gaisuwar maman ka kenan? To ka fad'a mata ba zan amsa ba."
Ita ma Bilal ta kalla tace "To ka fad'awa Abban ka ya juya ya koma in da ya fito, dan ba ya da muhalli a gidan nan yau."
Dariya ya yi ya kalli Bilal yace "Ka tambayar min ita kaji, wai dama ana korar mutum da gidan sa?"
Da shu'umin murmushi a fuskar ta tace "Ka fad'a ma sa sau nawa aka yi, idan kuma bai tab'a gani ba to yau zai faru a kan shi."
Da sauri ta gyara zama ta na fuskantar shi tace "Haba aljanna ta, ni fa na ce na amince, wallahi babu takura a ciki, wani k'aramin rashin fahimta ne, kuma sai ga shi cikin ikon Allah fasihi kuma nagartattacen miji na ya fahimtar da ni, dan haka in ba so ka ke na maka kuka ba kawai ka amince."
Yanda ta k'arashe maganar cikin shagwab'a ya birge shi, dan haka ya rumgumo ta jikin shi ya na dariya, cikin so da k'auna ya ci gaba da rarrashin ta tare da saka mata albarka, tambayar ta ya yi "To yanzu ina so ki fad'a min duk abin da ki ke buk'ata, ni kuma insha Allah zanyi mi ki shi a matsayin tukuici da kuma fad'an kishiya."
Kasancewar ta mace mai yawan shagwab'a da son jiki ya sa ta turo baki gaba ta kwanta a kafad'ar shi tace "Kaji ka da wata magana, ai ni yanzu ba kai ne za ka min hidima ba, ni ce ma zan bayar da tawa gudunmuwar."
"Ban yarda ba, sai kin fad'a, in ba haka ba kuma zan kama ki ne."
Yanda ya yi maganar cikin sigar rausaya ya sa ta tashi ta nufi d'akin ta ta na fad'in "Na k'i wayon, ka kamani d'in."
Ya na jin haka ya tashi da gudu ya nufe ta, ita ma a guje ta k'arasa shiga d'akin, kasancewar Bilal na wajen kakannin shi (iyayen Khadija) ya sa su ka saki jiki sosai su ka more rayuwar su, dan dama kusan kullum haka su ke.
*Washe gari* kamar kullum misalin *09:30* su ka gama shirin fita, har farfajiyar gida su ka isa tare, ita ma kuma cikin shirin fita ta ke, sai da ya shafi lallausan kumatun ta tare da sumbatar ta kafin yace "Ni zan wuce, ki kula min da kan ki, sannan ki gaishe min da su Mama, tun da ba za ki bani damar da zan kai ki da kai na ba bare na gaishe su."
Masha Allah, duk da cikin gilashi ne ta waina idon ta, amma bai hana su d'aukar hankalin Usman ba, saboda girman idon da kuma farin su tamkar madara, cikin wasa da idon ta ne tace "Na shiga uku, da alama sai an shekara d'ari ka na min gorin wannan maganar."
"Ai dole ne, dan na lura kamar ba kya so na je na kwaso albarka wajen Mama, sannan na sake mata godiya da ta bani ke."
"Gashi kuma ba kya gajiya da godiya kullum."
"Ni kam ina zan gaji da godiya, duk wanda ya baka yar sa ka aura ai ya gama ma ka komai, bare kuma mata irin ki Khadija, ai har duniya ta nad'e ba zan daina mu su godiya ba wallahi, dan na san sun fini sanin ki, amma kuma hakan bai hana su ka rabu da ke ba su ka bani ke, duk da kuwa sun san ba zan tab'a rabuwa da ke ba in ba mutuwa ce ta raba mu ba."
Ajiyar zuciya ta sauke tace "Idan har na biye ma ka, to hak'ik'a zan tabbata anan ban tafi in da zan je ba, dan haka sai an jima, nima ka gaishe min da Mama na da Abba na, tun da ka k'i bani damar bin ka bare na gaishe su."
Ta na fad'a ta juya ta na dariya shi kuma ya na fad'in "Au! Ramawa ki ka yi? Shikenan ai zan kama ki."
Gwalo ta masa tace "Ka kamani d'in, kafin nan na san in da na kai."
Wata tsandareriyar mota ta shiga bla (bleue) shi ma haka, sai dai ta shi bak'a ce, kowa hanyar da za ta sada shi da na shi iyayen ya nufa, dan su dama a *zarya* su ke, bayan masallacin *sahaba*, Khadija gaba ta yi saboda gidan su na gaban sabon gidan mota na *Rimbo*, shi kuma Usman gidan iyayen shi ya na nan *sabon gari* a 'yan *banana* (🤸♂aradu unguwar mu).
Ko da ya isa mahaifiyar shi kad'ai ya samu a gidan, dan haka su na gaisawa ya d'auko maganar auren shi, tambayar da ta fara mi shi ita ce "Khadija ta sani?"
"Eh Mama, ta sani, kuma ta bada goyon bayan ta d'ari bisa d'ari, yanzu amincewar ku na ke buk'ata."
Cike da kamala tsohuwar tace "Ba ka da matsala da amincewar mu *Fodio* (sunan mahaifin ta ne, dan haka ta ke ma sa inkiya da Fodio), tun da dai har ka shirya, kuma ka na ganin ba wata matsala, sannan matar ka ma ta amince ba tare da tashin hankali ba, ai ka ga Alhamdulillah, sai dai kawai mu bika da addu'a da kuma fatan alkairi."
"Nagode sosai Mama, Allah ya k'ara lafiya da girma, yanzu kenan idan Abba ya shigo za ku iya magana da su, duk yanda ku ka yi zuwa dare idan na dawo na ji insha Allah."
Kasantuwar shi d'an fari ya sa ko ido ba ta son had'awa da shi kamar ta na jin kunyar shi, ba tare da ta kalle shi ba tace "Shikenan ba damuwa, insha Allah zan fad'a ma sa."
D'an gyara zama ya yi alamar zai tashi yace "Mama babu wata matsala ko wani abun da ku ke buk'ata?"
"Ah, Fodio kai ne za ka bar gidan nan da wata matsala? Ai sai dai in ba ka raye, Alhamdulillah wallahi babu komai, Allah dai ya yi albarka, Allah ya sa ka gama da duniya lafiya."
Sai da ya durk'usa k'asa ya amsa da "Ameen Ameen Mama, nagode sosai da addu'ar ki gare ni, ni zan wuce sai anjima idan na dawo."
"To Allah ya yarda, Allah ya tsare, ka gaishe min da waccen mutumin."
Dariya ya yi yace "Watak'ila fa gobe ku gan shi gidan nan, dan mahaifiyar shi ta tafi d'auko shi."
Cikin wasa irin ta kaka da jika tace "Ka ce mi shi ma kar ya kuskura ya zo in har ya san ba zai taho da k'atuwar bak'ar leda ba."
"Zai zo da ita Mama, ai kin san shi da k'ok'arin cefanai."
"Ko dai k'ok'arin jefawa a ciki ba."
Da wannan wasan ya bar gidan zuciyar shi sakayau da ita kamar kullum, dan har abada babu abin da ke dagula mi shi lissafi, b'angaren mace, Allah ya wadata shi da mata kamar Khadija, babu abin da ya nema a gurin ta ya rasa, haka ma iyaye, Allah ya bashi iyayen da su ke son abin da ya ke so, sannan su ke nusar da shi tare da kora shi da addu'a a kullum, hakan na sa shi farin ciki , kuma shima ya na k'ok'ari sosai wajen sauke hakk'ok'in duka b'angarorin, haka ne m'a sanadiyar da ta sa kullum ci gaba ya ke gani babu komawa baya ko rashin nasara, dan Allah ba ya kunyatar ko tab'ar da wanda ya kiyaye hakk'ok'in wannan mutanen a duniya.
Khadija ma a gidan su farin ciki ta ke kamar ba ta farin ciki a gidan ta, hakan kuma ya samo asali ne sakamakon samun kan ta da ta yi a tsakiyar mahaifiyar ta da kuma d'an ta, sai sauran matan yayyun ta da kuma 'ya'yan su, bayan sun ci abincin rana yan uwan ta maza su uku su ka shigo gidan, anan ta tara su kuma ta fad'a mu su auren da mijin ta zaiyi, ta gaggauta fad'a mu su hakane saboda ta san sune za su iya bata shawara mai kyau wacce ta dace, kuma kamar yanda ta yi tsammani hakane ya faru, sosai su ka kwantar mata da hankali tare ja mata kunne da nasihohi ma su shiga rai, tare da kafa mata misali da matar babban yayan ta wanda da zai k'ara aure ta tashi hankalin kowa, a k'arshe dai sai da ta bar gidan, yanzu gashi nan sai amaryar ke rayuwar ta a b'angaren na su, abin da ba ta son ganin shi ke faruwa a bayan idon ta kuma ba yanda za ta yi, ga yayan ta ma su na hannun uban su sai yaga dama ya ke barin su su je wajen uwar, saboda hure mu su kunne da ta ke, hakan ya k'ara saka jikin Khadija yin sanyi, kuma ta yi niyyar yin aiki da shawarwarin da su ka bata, a haka ita ma ta yi yammacin ta tare da maman ta abar k'aunar ta, zuwa *5:30* na yamma kuma Bilal ya d'auki kayan shi su ka wuce tare da maman shi a motar ta.
Su na isa gida Bilal ya wuce da yan kayan shi d'akin shi tare da canza na jikin shi, ita ma kaya ta sauya ta wuce madafa dan sarrafa abin da za su ci da dare, tare da Bilal su ka shiga ya na kama mata duk aikin da ta ke yi, sai da aka gama sallah magrib ta gama lokacin Bilal ya wuce masallacin da ke had'e da gidan su, ta na gama ajewa a mazaunin cin abinci ta yi wanka ta shirya cikin riga da zane wanda su ka d'auke jikin ta sosai, kasancewar babu wata tazara mai tsayi tsakanin sallah magrib da isha'i ya sa ta yi sallahn ta, ta na kammalawa ta fito falon ya yi daidai da shigowar Bilal daga masallaci tare da baban shi.
Ta na ganin shi ta tashi tsaye ta turo baki tace "Sai yanzu za ka dawo min gida? Ina ka shige haka?"
Kallon Bilal ya yi yace "Yau salon gaisuwar maman ka kenan? To ka fad'a mata ba zan amsa ba."
Ita ma Bilal ta kalla tace "To ka fad'awa Abban ka ya juya ya koma in da ya fito, dan ba ya da muhalli a gidan nan yau."
Dariya ya yi ya kalli Bilal yace "Ka tambayar min ita kaji, wai dama ana korar mutum da gidan sa?"
Da shu'umin murmushi a fuskar ta tace "Ka fad'a ma sa sau nawa aka yi, idan kuma bai tab'a gani ba to yau zai faru a kan shi."