Sashe 17
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da dare ma tare su ka ci abinci su ka ida su ka tab'a kallo, ko da dare ya k'ara yi Khadija ta fara tashi ta yi shirin kwanciya, ta na gamawa ta kwanta ta rufe ruf dan ta nuna ta yi bacci, sai da aka d'auki lokaci kafin ya shiga d'akin shi ma ya shirya, kashe wuta ya yi ya kwanta gefen ta, daga yanda Usman ya ji canzawar numfashinta ya tabbatar mi shi ba bacci ta ke ba, dan ya tsoratar da ita ya yaye zanin rufar daga fuskar ta cikin taushi murya yace "Allah yasa matsoraciyar nan ta yi bacci, sai na samu yanda na ke so."
Zunbur ta mik'e zaune ta kafe shi da ido duk da ba ganin shi takeda kyau ba, zaune ya yi ya janyo hannun ta ya na fad'in "Ashe ba bacci ki ke ba, to matso kusa da ni."
Girgiza kai ta yi alamar a'a, k'in matsawa ta yi sai da shi ya matsa daf da ita ya rumgumea jikin shi, shafata ya ke ya na fad'in "Khadija, kinsan me ye aure?"
D'an tureshi ta yi daga jikin ta tana so ya rabuda ita, matseta ya yi sosai yace "Ki nutsu mana, me ya sa ki ka cika tsoro ne? Ni fa mijin ki ne."
Kamar za ta fashe da kuka tace "Ni dai dan Allah ka sake ni, ba na jin dad'i."
Kallon fuskarta ya yi yace "Khadija ba na da tunanin tauye mi ki hakk'in ki, kar ki ga kamar ina takura ki, ina so ne kema ki shaida kinyi aure, sannan ki zama babbar mace, ba zan so ace kin wuce kwana uku a gidan nan ba tare da kinsan a wane matsayi ki ke ba, kumada safe na fad'a mi ki ni matafiyi ne, gobe ko jibi tafiya za ta iya taso min, kuma ba na dawowa k'asa da sati biyu, kinga kenan idan banyi abin da ya dace ba na zama kamar lusari kenan."
Khadija dai shiru ta yi ba tace komai ba sai sauraren shi, daga nan kuma sai ya samu dama ya kuma yi anfani da ita wajen mayar da Khadija babbar macen kamar yanda yace, dukansu sun san bak'on al'amari ne a gare su, shi farin ciki tare da jin wani sanyi a zuciyar shi, Khadija kuma kuka na rad'ad'i da zafin da take ji da ya zama sabon abu a wajen ta, da taimakon shi ya taimaka mata ta gyara kan ta ta tsarkake jikinta, har bacci ya fara d'aukar ta tajiya k'wak'ume ta kamar zai mayar da ita ciki, haka bacci ya rideta amma banda Usman da ya kwana ya na kallon fuskarta ya na shek'a mata sawar albarka da tunanin yanda rayuwarshi ta canza sanadiyarta cikin k'ank'anin lokaci, har aka kira sallah idon shi biyu, sai da ya yi alwala sannan ya zo ya tashe ta a hankali, masallaci ya nufa ita ta yi sallahnta a gida, tun akan sallaya ta kwanta saboda zafin da har yanzu take ji a k'asan ta da kuma bacci, ko da ya same ta bai tashe ta sai da ya tabbatar ya had'a mata ruwan shayi da soyayyen k'wai, tashin ta ya yi da kan shi ya mata wanka duk da ta cije akan bata so amma bai barta ba, haka ya saka mata kaya suka karya, yinin ranar babu inda ya je duk da yaran mak'wabta na shigowa, ya na zaune ya na kallon matar shi na kai da kawo ya na jin dad'i da sabon abu a game da ita.
*Muje da sauri fan's*, sati biyu kad'ai da auren su, amma shak'uwa ce mai k'arfi ta shiga tsakanin su sosai, a cikin k'ank'anin lokaci suka saba da junan su, dan sosai Usman ke sakin jiki da Khadija ya na janta a jikinshi, *sabo tirken wawa*, sai gashi ita kanta Khadija ta saba da shi sosai ta yanda ba ta kl cin abinci in ba tare da shi ba, dan ji take kamar ya zamar mata yan uwan ta biyar, cikin wannan rayuwar farin ciki Usman ya shirya tafiya *zinder*, matuk'a Khadija taji ba dad'i, tunanin ta ya za ta yi rayuwa a gidan ita kad'ai babu shi, ya yi k'ok'ari sosai ya kwantar mata da hankali, amma hakan bai mata ba har sai da tace ya d'auko Aziza ya kawota nan, ya ji dad'in tunanin ta sosai, kuma haka akayi kam, a ranar da zai tafi a ranar aka kawo Aziza da kayan ta, haka ya tafi suka rabu cike da kewar juna.
Ta ji dad'in zaman ta tare da Aziza duk da yarinya ce, ita ke kula da duk d'awainiyar ta, haka ma yan uwan Usman d'in na yawon kawo mata ziyara, haka ma jefi jefi yan yan uwan ta su kan lek'o dan su ga halin da take ciki, a haka har aka kwashe *kwana goma sha biyu*, a kwana na sha uku Usman yace ya na nan tafe, duk da ba ta san ainahin abin da ta ke ji a ran ta ba a game da shi, amma haka ta ji farin ciki ya mamaye ta sosai, a ranar Kaltume ta zo gidan, kuma Kaltume yarinya ce da Allah ya bawa basirar sanin kan tsiyar maza😂, idan ta fad'i wata magana sai ka d'auka babbar mace ce, haka ta samu ta had'awa Khadija wani had'add'en lemun kayan marmari sannan ta zuba mata madara a ciki da *garin raihan*, wuni ta yi ta na shan shi bayan tasha lalle da kitso na tarban miji, bayan nan kuma da kan ta ta taimaka mata suka canza zaman duka kayan d'akin, kuma duk su na aikin ne ta na k'ara fad'a mata irin shiri da kwalliyar da za ta yi, duk Khadija na sauraren ta har ta gama, girki ta d'ora su ka ci kafin ta tafi gida.
Kasancewar shigowar rana zaiyi ya sa tun k'arfe *d'aya* na rana Khadija ta kammala girki ta aje in da ya dace, dama tun da safe Hajia ta aiko Mannir ya d'auki Aziza, hakan ya bata damar sakewa sosai ta yi aikin ta, wanka ta yi ta jima ta na shafawa ta na zanawa da dangwalawa, k'ananan kaya ta saka riga da siket na kanti masu kyau da suka dace da ita, turaren tsintsiya ta kunna sannan ta turara na wuta mai dad'in k'amshi, sai kuma na ruwa (airfreshner) shi ma mai k'amshin lemon tsami ta fesa, ko ina ya d'au harama mai gidan kawai ake jira, k'arfe *uku* cip-cip ta na zaune ta ji sallama, shaida muryar ya sa ta ja dogon numfashi lokacin da ta tuna hud'ubar Kaltume, mik'ewa ta yi ta fice da gudu ta yaye laluben, ba ta tsaya tunanin komai ba ta fad'a jikin shi ta rumgume shi k'yam, cikin farin ciki take fad'in "Sannu da zuwa miji na, sannu da dawowa, na yi farin ciki da dawowar ka gare ni."
Ajiyar zuciya Usman ya sauke ya d'an juya ya kalli *Kabir* k'annan shi da ya d'auko shi daga gidan mota, karb'ar jakar hannun shi ya yi yace "Nagode ko, ka gaishe da su Hajia sai na shigo."
Baki bud'e ta d'ago a hankali dan ganin waye, ta na ganin Kabir ta sake saurin sunne kan ta cikin k'irjin shi ta cakumo rigar shi ta rufe fuska da ita, dariya su ka mata Kabir yace "Matar yaya wai ba dai sati biyu da ya yi baya nan ne ya saki wannan farin cikin ba kamar ya yi shekara?"
Ita kam kunya ce ta sake rufeta ta kuma tusa kan ta cikin k'irjin shi dan ba za ta iya d'agowa su had'a ido ba, murmushi Usman ya yi ya na shafa bayanta yace "Dallah malam ka wuce ka yi abin da na saka ka, sai ka takura min yar..."
Shirun da ya yi ya sa Khadija d'agowa ta kalle shi, had'a goshinsu ya yi wuri d'aya yace "Yar yarinya ta na ke nufi."
Cikin dariya Kabir yace "To sai anjiman ku amare, sai ka shigo d'in, amma ni banga alamar za ta barka ka fito ba."
"Saboda me?" Cewar Usman ya na kallonshi, shafa kan shi ya yi yace "Ai na ga ta yi kewarka ne sosai."
Wannan maganar ce ta sa Khadija juyawa da k'arfi za ta koma d'aki Usman ya fizgota ta fad'a kan shi, dariya su ka saka Usman ya juyo ya kalli Kabir yace "Kai wai za ka fice min ko sai na raka ka ne?"
Sosa k'eya ya yi yace "To ai ba ka ban tsaraba ta bane, ko ka manta yanda mu ka yi da kai kafin ka tafi?"
Sakin Khadija ya yi ya aje jakunkunan hannun shi ya tunkari Kabir ya na fad'in "Ina zuwa, bara ka gani d'an hancin uwa kai."
Maimakon ya fita daga gidan sai ya daka da gudu ya yi hanyar ban d'aki ya na dariya ya na fad'in "Amma fa sai da na fad'a maka banda mai a moto na, kace idan mu ka zo za ka ban kud'i na saka, ka bani kawai sai na tafiya ta na barku ku soyewar ku."
Dawowa ya yi ya kama hannun Khadija ya sunkuya zai d'auki jakunkunan ta tu saurin karb'a ta na fad'in "Bara na shigar ma ka da su."
Kabir ne ya sake fad'in "Dan Allah ka fito ka sallame ni kafin ka shiga d'akin nan, dan bansan me zai faru ba idan ka shiga."
Juyowa ya yi ya kanne shi Khadija kuma k'arasa shiga ta yi saboda kunya, suna shiga Usman ya tsaya ya na k'arewa d'akin kallo, komai a d'akin kalar kayan d'akin ta ne ma'ana fari da maron, sai telebijin da k'aramin teburin tsakar d'aki ne kad'ai bak'ak'e, ajiyar zuciya ya sauke ya kalle ta yace "Duk wannan shirin na zuwa na ne?"
Cike da kunya tace "Eh mana, sati biyu ba ka gidan ka, ya na da kyau ka tarar da sabon abu dama."
Hannunshi ta kama tace "Muje ka cire wannan kayan ka yi wanka, idan ka fito sai ka zo ka ci abinci."
"Na ci abinci ko ki ba ni abinci?" Ya fad'a ya na tsare ta da ido, murmushi ta yi ta kalle shi tace "Duk yanda ka ke so ai girman ka ne, ka cancanci fiye da haka ma."
Zunbur ta mik'e zaune ta kafe shi da ido duk da ba ganin shi takeda kyau ba, zaune ya yi ya janyo hannun ta ya na fad'in "Ashe ba bacci ki ke ba, to matso kusa da ni."
Girgiza kai ta yi alamar a'a, k'in matsawa ta yi sai da shi ya matsa daf da ita ya rumgumea jikin shi, shafata ya ke ya na fad'in "Khadija, kinsan me ye aure?"
D'an tureshi ta yi daga jikin ta tana so ya rabuda ita, matseta ya yi sosai yace "Ki nutsu mana, me ya sa ki ka cika tsoro ne? Ni fa mijin ki ne."
Kamar za ta fashe da kuka tace "Ni dai dan Allah ka sake ni, ba na jin dad'i."
Kallon fuskarta ya yi yace "Khadija ba na da tunanin tauye mi ki hakk'in ki, kar ki ga kamar ina takura ki, ina so ne kema ki shaida kinyi aure, sannan ki zama babbar mace, ba zan so ace kin wuce kwana uku a gidan nan ba tare da kinsan a wane matsayi ki ke ba, kumada safe na fad'a mi ki ni matafiyi ne, gobe ko jibi tafiya za ta iya taso min, kuma ba na dawowa k'asa da sati biyu, kinga kenan idan banyi abin da ya dace ba na zama kamar lusari kenan."
Khadija dai shiru ta yi ba tace komai ba sai sauraren shi, daga nan kuma sai ya samu dama ya kuma yi anfani da ita wajen mayar da Khadija babbar macen kamar yanda yace, dukansu sun san bak'on al'amari ne a gare su, shi farin ciki tare da jin wani sanyi a zuciyar shi, Khadija kuma kuka na rad'ad'i da zafin da take ji da ya zama sabon abu a wajen ta, da taimakon shi ya taimaka mata ta gyara kan ta ta tsarkake jikinta, har bacci ya fara d'aukar ta tajiya k'wak'ume ta kamar zai mayar da ita ciki, haka bacci ya rideta amma banda Usman da ya kwana ya na kallon fuskarta ya na shek'a mata sawar albarka da tunanin yanda rayuwarshi ta canza sanadiyarta cikin k'ank'anin lokaci, har aka kira sallah idon shi biyu, sai da ya yi alwala sannan ya zo ya tashe ta a hankali, masallaci ya nufa ita ta yi sallahnta a gida, tun akan sallaya ta kwanta saboda zafin da har yanzu take ji a k'asan ta da kuma bacci, ko da ya same ta bai tashe ta sai da ya tabbatar ya had'a mata ruwan shayi da soyayyen k'wai, tashin ta ya yi da kan shi ya mata wanka duk da ta cije akan bata so amma bai barta ba, haka ya saka mata kaya suka karya, yinin ranar babu inda ya je duk da yaran mak'wabta na shigowa, ya na zaune ya na kallon matar shi na kai da kawo ya na jin dad'i da sabon abu a game da ita.
*Muje da sauri fan's*, sati biyu kad'ai da auren su, amma shak'uwa ce mai k'arfi ta shiga tsakanin su sosai, a cikin k'ank'anin lokaci suka saba da junan su, dan sosai Usman ke sakin jiki da Khadija ya na janta a jikinshi, *sabo tirken wawa*, sai gashi ita kanta Khadija ta saba da shi sosai ta yanda ba ta kl cin abinci in ba tare da shi ba, dan ji take kamar ya zamar mata yan uwan ta biyar, cikin wannan rayuwar farin ciki Usman ya shirya tafiya *zinder*, matuk'a Khadija taji ba dad'i, tunanin ta ya za ta yi rayuwa a gidan ita kad'ai babu shi, ya yi k'ok'ari sosai ya kwantar mata da hankali, amma hakan bai mata ba har sai da tace ya d'auko Aziza ya kawota nan, ya ji dad'in tunanin ta sosai, kuma haka akayi kam, a ranar da zai tafi a ranar aka kawo Aziza da kayan ta, haka ya tafi suka rabu cike da kewar juna.
Ta ji dad'in zaman ta tare da Aziza duk da yarinya ce, ita ke kula da duk d'awainiyar ta, haka ma yan uwan Usman d'in na yawon kawo mata ziyara, haka ma jefi jefi yan yan uwan ta su kan lek'o dan su ga halin da take ciki, a haka har aka kwashe *kwana goma sha biyu*, a kwana na sha uku Usman yace ya na nan tafe, duk da ba ta san ainahin abin da ta ke ji a ran ta ba a game da shi, amma haka ta ji farin ciki ya mamaye ta sosai, a ranar Kaltume ta zo gidan, kuma Kaltume yarinya ce da Allah ya bawa basirar sanin kan tsiyar maza😂, idan ta fad'i wata magana sai ka d'auka babbar mace ce, haka ta samu ta had'awa Khadija wani had'add'en lemun kayan marmari sannan ta zuba mata madara a ciki da *garin raihan*, wuni ta yi ta na shan shi bayan tasha lalle da kitso na tarban miji, bayan nan kuma da kan ta ta taimaka mata suka canza zaman duka kayan d'akin, kuma duk su na aikin ne ta na k'ara fad'a mata irin shiri da kwalliyar da za ta yi, duk Khadija na sauraren ta har ta gama, girki ta d'ora su ka ci kafin ta tafi gida.
Kasancewar shigowar rana zaiyi ya sa tun k'arfe *d'aya* na rana Khadija ta kammala girki ta aje in da ya dace, dama tun da safe Hajia ta aiko Mannir ya d'auki Aziza, hakan ya bata damar sakewa sosai ta yi aikin ta, wanka ta yi ta jima ta na shafawa ta na zanawa da dangwalawa, k'ananan kaya ta saka riga da siket na kanti masu kyau da suka dace da ita, turaren tsintsiya ta kunna sannan ta turara na wuta mai dad'in k'amshi, sai kuma na ruwa (airfreshner) shi ma mai k'amshin lemon tsami ta fesa, ko ina ya d'au harama mai gidan kawai ake jira, k'arfe *uku* cip-cip ta na zaune ta ji sallama, shaida muryar ya sa ta ja dogon numfashi lokacin da ta tuna hud'ubar Kaltume, mik'ewa ta yi ta fice da gudu ta yaye laluben, ba ta tsaya tunanin komai ba ta fad'a jikin shi ta rumgume shi k'yam, cikin farin ciki take fad'in "Sannu da zuwa miji na, sannu da dawowa, na yi farin ciki da dawowar ka gare ni."
Ajiyar zuciya Usman ya sauke ya d'an juya ya kalli *Kabir* k'annan shi da ya d'auko shi daga gidan mota, karb'ar jakar hannun shi ya yi yace "Nagode ko, ka gaishe da su Hajia sai na shigo."
Baki bud'e ta d'ago a hankali dan ganin waye, ta na ganin Kabir ta sake saurin sunne kan ta cikin k'irjin shi ta cakumo rigar shi ta rufe fuska da ita, dariya su ka mata Kabir yace "Matar yaya wai ba dai sati biyu da ya yi baya nan ne ya saki wannan farin cikin ba kamar ya yi shekara?"
Ita kam kunya ce ta sake rufeta ta kuma tusa kan ta cikin k'irjin shi dan ba za ta iya d'agowa su had'a ido ba, murmushi Usman ya yi ya na shafa bayanta yace "Dallah malam ka wuce ka yi abin da na saka ka, sai ka takura min yar..."
Shirun da ya yi ya sa Khadija d'agowa ta kalle shi, had'a goshinsu ya yi wuri d'aya yace "Yar yarinya ta na ke nufi."
Cikin dariya Kabir yace "To sai anjiman ku amare, sai ka shigo d'in, amma ni banga alamar za ta barka ka fito ba."
"Saboda me?" Cewar Usman ya na kallonshi, shafa kan shi ya yi yace "Ai na ga ta yi kewarka ne sosai."
Wannan maganar ce ta sa Khadija juyawa da k'arfi za ta koma d'aki Usman ya fizgota ta fad'a kan shi, dariya su ka saka Usman ya juyo ya kalli Kabir yace "Kai wai za ka fice min ko sai na raka ka ne?"
Sosa k'eya ya yi yace "To ai ba ka ban tsaraba ta bane, ko ka manta yanda mu ka yi da kai kafin ka tafi?"
Sakin Khadija ya yi ya aje jakunkunan hannun shi ya tunkari Kabir ya na fad'in "Ina zuwa, bara ka gani d'an hancin uwa kai."
Maimakon ya fita daga gidan sai ya daka da gudu ya yi hanyar ban d'aki ya na dariya ya na fad'in "Amma fa sai da na fad'a maka banda mai a moto na, kace idan mu ka zo za ka ban kud'i na saka, ka bani kawai sai na tafiya ta na barku ku soyewar ku."
Dawowa ya yi ya kama hannun Khadija ya sunkuya zai d'auki jakunkunan ta tu saurin karb'a ta na fad'in "Bara na shigar ma ka da su."
Kabir ne ya sake fad'in "Dan Allah ka fito ka sallame ni kafin ka shiga d'akin nan, dan bansan me zai faru ba idan ka shiga."
Juyowa ya yi ya kanne shi Khadija kuma k'arasa shiga ta yi saboda kunya, suna shiga Usman ya tsaya ya na k'arewa d'akin kallo, komai a d'akin kalar kayan d'akin ta ne ma'ana fari da maron, sai telebijin da k'aramin teburin tsakar d'aki ne kad'ai bak'ak'e, ajiyar zuciya ya sauke ya kalle ta yace "Duk wannan shirin na zuwa na ne?"
Cike da kunya tace "Eh mana, sati biyu ba ka gidan ka, ya na da kyau ka tarar da sabon abu dama."
Hannunshi ta kama tace "Muje ka cire wannan kayan ka yi wanka, idan ka fito sai ka zo ka ci abinci."
"Na ci abinci ko ki ba ni abinci?" Ya fad'a ya na tsare ta da ido, murmushi ta yi ta kalle shi tace "Duk yanda ka ke so ai girman ka ne, ka cancanci fiye da haka ma."