← Book details Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 76 OF 86

Sashe 76

Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da k'yar yace "Mummy, ciwo na, ki bani ruwa na sha." Ruwa ta d'auka ta bashi, komawa ya yi ya kwanta yanda ya ke har bacci ya sake d'aukar shi.

*B'angaren* Usman kuma tun a hanya yake tunani dama Haseenah ta shirya raba shi da yaron shi, in ba haka ba me ya sa ta hana shi ya fita da shi? Kawai makirci ne ta shirya mi shi dan ta raba shi da Bilal d'in shi, tunda ai tasan baya bari Bilal ya fita da moton shi, ko a k'afa bai cika son ana aikan shi ba wajen ti-ti, da wannan tunanin ya k'araso gida dan d'aukar mataki akan amarsu.

_Ita dama rayuwa haka take tafiya, ka shuka alkairi saika girbi alkairi, a baya mutane suna ganin laifin Khadija saboda makircin Haseenah, wanda ita Khadija a kan gaskiyarta take, yau kuma gashi Haseenah ita ma bata da niyyar cutar da Bilal, amma sakkayar Allah dama haka take, gashi ita ma yanzu za'a hukunta ta akan laifin da bata san hawa ba bata san sauka ba, Allah ka mana agaji da kan ka._

Haseenah da ke madafa a lokacin da waya a kunne ta kira Mariya ta na tambayar ko za ta zo? Cewar Mariya "Haseenah ba zan samu damar zuwa ba wallahi, saboda kwana biyun nan munyi hidimar biki, ko na tambayi Abban Fadila ma ba zai bar ni ba, amma ke ki zo ki kawo kud'in, idan na samu dama sai naje wajen malam d'in."

Cikin damuwa tace "Haba aunty Mariya, na fad'a mi ki fa halin da nake ciki, wallahi Usman ko magana ba ya son yi min, ina ga fa Khadija wani asiri ta masa ya juya min baya, kuma yace za ta dawo gidan, jiya ma kar ko so kiji maganar da ya fad'a min akan Bilal, to ina ga ta dawo gidan? Ai sai dai ya sake ni."

Mariya ce tace "To ya za ayi? Ni dai yanzu na fad'a mi ki uziri na ai, kinga kuwa dan na gyara aurenki ai bana b'algace nawa ba."

Ajiyar zuciya ta sauke tace "To shikenan, bara ya shigo saina tambaye shi naji idan zai bar ni, ko zuwa gobe sai naje na kai mi ki kud'in, amma fa aunty Mariya wannan karan so na ke gaba d'aya a zautar da shi ya zama ba komai a gabansa sai ni, sannan ba shi kad'ai ba har iyayen shi da yan uwan shi ina so a rufe bakin su, su zama babu ruwansu da harkar shi bare har wani ya yi tunanin taimaka masa da ko da addu'a ce."

Da matuk'ar mamaki Mariya tace "Ke Haseenah, a ina ki ka koyi mugunta haka? Yaushe zuciyar ki ta zama marar imani haka? To kinga gaskiya no ba zan iya wannan aikin ba, dan in na biye mi ki mu ka yi haka to kashin mu zai bushe wallahi."

Cikin rashin nuna damuwa tace "Me ki ke nufi? Kamar ya banda imani?"

Muryar Usman ce ta bata amsa da "To ki na da shine imanin?"

Bata san lokacin da ta saki wayar ba ta juyo da k'arfi, hannu tasa ta rufe bakinta matuk'ar tsoro a fuskarta, tabb', lallai yanda ta ga alamunshi ta san yau babu tsumi ba dabara, amma duk da haka bara ta jaraba lallab'a shi ko Allah zaisa a dace, a cewar ta fa, durk'ushewa ta yi ta had'e hannayenta ta kalle shi tana hawaye tace "Dan Allah dan girman Allah Abban Bilal ka yi hak'uri, wallahi tallahi sharrin shaid'an ne da zugar aunty Mariya, ka yi hak'uri ka yafe min dan Allah ko dan cikin nan dake jiki na, wallahi na ma ka alk'awarin haka ba za ta sake faruwa ba."

Takowa ya yi har kusanta ya sa hannu ya kashe wutar gas d'in, tsayawa ya yi ya na k'are mata kallo, wai yarinyar da ya aura saboda nutsuwarta da hankalinta, ita ce ta yi sanadiyar faruwar abubuwa marasa dad'i irin haka a rayuwar shi, ita kam kallon da yake mata ne ya sa ta sake cewa "Dan Allah babban mutum ka yi hak'uri, wallahi ba laifi na bane, wall..."

Marin da ya zuba mata ne ya sa ta kwamtsa wata k'ara ta fad'i kwance, duk'awa ya yi ya d'ago ta cikin zafin rai ido jawur yace "Haseenah me nai mi ki a rayuwa? Me ya sa ki ka cutar dani? Me ya sa Haseenah?"

Cikin duburburcewa tace "Wallahi ba ni bace, ka yi hak'uri dan Allah, ba zan.." Shak'e mata wuyan da ya yi ne yasa komai nata tsayawa idon ta fitowa waje, cikin fitar hayyaci Usman ke fad'in "Haseenah ke annoba ce, jaraba ce kuma masifa ce ke da bala'i, barin irin ki a doron duniya wallahi japa'i ne, wallahi da zan kashe ki amma ba zan iya ba saboda cikin da ke jikin ki, Haseenah banga anfanin zama da ke ba a rayuwa ta, kin raba ni da hankali na da ubangiji na, kin raba ni da iyaye na da 'yan uwa na, kin raba ni da matar da nafi so a rayuwa ta, sannan kin raba ni da d'ana da ya fito daga ciki na, Haseenah ni kam ya zanyi dake? Wane irin hukuncin ma zan mi ki ne da zai sa na huce abin da ki ka min."

Haseenah dake ta fafutukar neman rayuwa ya na sakin ta ta samu ta sauke wasu numfarfashi, mik'ewa ya yi tsaye ya juya baya ya cire hular kan shi yana shafa sumar shi kamar zai cire kan, sake juyowa ya yi ya nuna ta da hannu yace "A dalilin ki yanzu haka Bilal na kwance asibiti, bansan ko zai rayu ba saboda yanda jikin shi yake, dan haka Haseenah ba zan iya ci gaba da zama dake ba, kije gidanku kawai na sake ki saki biyu."

Wata k'ara Haseenah ta yi ta d'ora hannu akai tace "Ahhhhhhh, na shiga uku na lalace, dan Allah Usman ka rufa min asiri ka yi hak'uri ka yafe min, wallahi ba zan sake ba na rantse ma ka, ka taimaka min mana ka dubi cikin nan dake jikina, kar ka mayar dani bazawara tun yanzu Usman ko haihuwar fari banyi ba."

Girgiza kai yayi ya tab'e baki yace "Hum, ai ko meya faru ke kika jawa kan ki, dan haka ki tattara naki ya naki ki bar min gida na, idan ki ka bari na dawo gidan nan na same ki wallahi saina lahira ya fiki jin dad'i."

Yana fad'a ya fice daga madafar ya shiga b'angaren shi, rage kayan jikinshi ya yi ya shiga ya watsa ruwa saboda yaji sanyi, yana fitowa maganin ciwon kai yasha kafin ya canza kaya ya bar gidan ko kallon b'angaren Haseenah baiyi ba, a tunanin shi ma tana barin gidan zai ruguza wannan b'angaren dan ya zauna lafiya, dan ba zaisake bari zuciyarshi ta raya mi shi sake k'ara wani aure nan gaba, lokacin har an fara kiran sallah la'asar sai kawai ya tsaya ya yi sallah kafin ya isa asibiti.

*Ana tare*🤝
11/03/2020 à 19:36 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑

_SAMIRA HAROUNA_

*Litattafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._

*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_ 🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

```Fatan alkairi masoya```

_Bismillahir rahamanir rahim_

*38*

Bai samu ganin Khadija ba saboda a lokacin suna sallah, kuma an rufe d'akin da Bilal ke kwance saboda hayaniyar da tayi yawa aka barshi shi kad'ai kafin wani lokaci, fita Usman d'in ya yi yace zai dawo anjima.

A wajen Haseenah ba yanda ta iya dole ta d'an d'auki abin da ta d'auka ta fito ta na kuka ta bar gidan, amma da taje gida kasa fad'an komai ta yi sai tace kawai ta na girki ya same ta yace ta taho gida ya sake ta saki biyu, su kam iyayen take su ka d'ora laifin kan Khadija cewa ita ta shiga ta fita aka sake ta, Haseenah dai komai ba tace ba sai sauraren su, mahaifin ta ne yace zai je ya samu mahaifin Usman d'in dan ba zai d'auki wannan wulak'ancin ba a sako masa 'ya da tsohon ciki, ba ta yi yunk'urin hanawa ba tunda ita kan ta za ta so ta koma d'in, haka ko akayi bayan sallah magriba anyi katari malam ya na gidan mahaifin Haseenah ya sallama ya fito, da ganin shi malam ya tarbe shi yanda ya kamata ya shinfid'a mu su tabarma a waje su ka zauna, nan fa malam *Mussa* ya fad'awa malam abin da ke faruwa, sosai malam ya jinjina ya kuma fad'a mi shi baisan me ke faruwa ba sai yanzu, amma ya yi alk'awarin tuntub'ar Fodio yaji dalilin yin hakan, nan dai ya kwantar masa da hankali suka rabu lafiya, malam kam baiyi k'asa a gwiwa ba wajen kiran Usman yace ya same shi gida, ana idar da sallah isha'i ya k'araso ya samu malam, a cikin gida suka samu waje tare da Hajia suka tattauna sosai sosai, anan ya fad'a mu su cewa "A gaskiya Baba ba zan iya zama da yarinyar nan ba, domin kuwa duk ita ce silar abubuwan da suka dinga faruwa da ni, kawai ku rabu da ita can ta haihu, idan ta haihu zanje na d'auko abinda ta haifa bayan ta shayar da shi dan ba zan iya barin abin da ta haifa a hannunta ba saboda mugun halin ta."

Malam ne yace "Amma duk abin da tayi Fodio bai kamata ka sake ta a wannan halin ba."

Shirun da ya yi yasa Hajia cewa "Koma dai menene ita taja, a gaskiya Hassenah ta bamu mamaki, yarinya sumi-sumi ashe lunbu-lunbu ce macijin k'yaik'ayi, muna ta wa Khadija kallon mai laifi ashe ita ce muguwar."
Chapter 76 · 0% Book details