Sashe 60
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rumgume juna su ka yi cikin farin ciki, ba ta jima ba ta mata sallama ta bar asibitin, daga nan kuma gidan k'awar ta ta wuce Kaltume dan sanar da ita, da shigarta gidan ta ji sun k'ara birge ta abun sha'awa, dan farko *Madina* kishiyar Kaltume ta so ita ma ta yi kalar nata iskancin, sai dai ina tuni Kaltume ta nuna mata ruwa ba sa'an kwando bane, sannan shi kan shi mijin na su *Alhaji Ibrahim* yasan da ya fad'a tarkon Kaltume da babu mai k'watar shi idan ba ubangiji shi ba, a k'arshe dai Madina ta fahimci tazara mai tsayi ce tsakanin su da ita dole ta hak'ura, musamman da ya zama babu mai iya bata shawara ga yanda za ta mu'amulanci rayuwar gidan ta, cikin sauk'i sai suka zauna lafiya kamar ba kishiyoyi ba, yanzun ma saida suka gaisa sosai ita da Khadija har suka fara tab'a hira kafin Kaltume tace su je daga ciki, nan fa ta fad'a mata ta na da ciki kar kuso suji bud'ar da Kaltume ta rabka har k'ofar gida, tsabar nuna farin cikin ta ya sa nan take ta bawa yara kud'i tace su siyo alawa mai tsada su rabawa yara, anjima kuma da yamma za ta yi fanke na sadaka da godiya ga Allah, Khadija dai kallonta kawai tale ta na k'ara k'aunar Kaltume, tabbas a rayuwa bata da yar uwa mace amma Kaltume ta zame mata komai, har kusan yamma kafin ta bar gidan saboda kiran ta da Mama ta yi, haka ta koma gida nan ma Mama da aka k'ara tabbatar mata gaba d'aya gida ya d'auka Bilal zai samu k'ane ko k'anwa, in da Mama ke binshi da gwalo ta na fad'in "Tuzurun wofi, yanzu dai sai naga k'afafun uban wa za ka hawa ko kuma wanda zaka wa shagwab'a, dama can rashin ganin wani ne a gaban ka ya sa ka wannan iskancin."
Shi kam cewa ya ke to sai me, ai k'ane za'a mi shi dan haka bai damu ba, kuma idan ya na son hawan k'afafu ga nata nan zai hau, da haka har 'yan biyar su ka zo suma suka d'ora nasu farin cikin ana addu'ar Allah ya sauketa lafiya.
*Mu ma dai munce ameen.*
Kamar kullum Usman ya je gaishe da iyayen sa, kuma kamar yanda ya saba riska yau ma malam baya nan, sai dai ya bar sak'on wannan ruwan addu'ar a bashi ya sha, saida ya shanye Hajia ta fito daga ban d'aki tace "Tashi kaje ka yi wanka ruwa na nan na had'a ma ka."
Kasa magana ya yi saboda mamaki da kuma rashin sanin abin da zai fad'a, saida ta maimaita da "Ko ba ka ji ba ina magana?"
Saida ya gyara zama ya kalli jikin shi da kyau yace "Amma Hajia na yi wanka fa, wane irin wanka ne zanyi yanzu kuma?"
"Ka tashi ka shiga lokaci tafiya yake." Marairaicewa ya sake yi yace "Amma Hajia wai dan..." Katse shi ta yi da "In za ka tashi ka tashi kafin ka b'ata min rai."
Tashi ya yi kamar zai k'urma ihu saboda haushi, ya rasa irin wannan sabon al'amari na iyayen shi, haka ya tub'e kayan da ya sanyo yanzun ya yi wanka da wannan hakukuwan na magani, haka ya sanyo kayan ya fito duk ruwan jikin shi sun tsaya a kayan, ya na fitowa Hajia kuma ta bashi damammiyar fura da maganin jiya a ciki, saida ta masa jan ido yasha dan cewa ya yi jiya baiyi bacci ba, hakan ya sa ta bud'e mi shi ido sosai sannan ya sha, wata 'yar kwalba ta d'auko bak'a mai d'auke da maganin *jibda* a ciki, da kan ta ta lak'ato a hannu ta shafa mi shi a wuya zuwa kai da hannuwan shi har zuwa damatsenshi, bashi ta yi tace ya d'iba ya shafa a cikin shi har zuwa k'irji, kamar zaiyi kuka ya kalle ta yace "Hajia wai duk wannan na miye haka? Wannan abun nan amai zai saka ni, sam warin shi babu dad'i."
Shiru kawai ta yi ba tace komai ba dole ya shafa yanda take so, mik'ewa ya yi yace "Hajia ko za ki bani magungunan sai ki nuna min yanda ake sha, ina ga kamar hakan zaifi ko?"
Kallon shi ta yi tace "Alhaji, kai ka haife ni ko ni na haife ka?"
Cike da ladabi ya rusuna yace "A'a Hajia ki yi hak'uri, ban fad'i haka dan b'ata ran ki ba."
"To ka wuce ka tafi in da za ka je kawai, sannan ba na so ka fad'a wa wani ko wata batun magungunan nan, ko da kuwa matan ka ne ban yarda ba, kaji ni ko?"
"Naji Hajia, amma wallahi da gaske na le idan ki ka bani zanyi aiki da su, Hajia ki duba kiga hakan zaifi a gani na, misali yanzu na wankan nan, idan da a waje na yake da haka ba za ta faru ba, amma idan ya na nan zai zamana kullum sai na yi wanka anan kenan, sannan idan na yi tafiya za'a dakatar da maganin kenan har sai na dawo, sannan Hajia..."
"Dakata dallah." Ta katse shi tare da d'aga hannu, shiru ta yi ta jima ta na tunanin abin da ya fad'a kafin ta gamsu ta d'auko duka magungunan ta bashi, saida ya karb'a ta nuna mi shi yanda zaiyi aiki da su kafin ta sake jadadda mi shi bata so ko matar shi ta sani, alk'awari ya mata babu wanda zaiji dan haka ta bashi ya tafi, aljihu ya saka su ya fita daga gidan ya shiga harkokin gaban shi, sai yamma ya dawo gida cin abinci, zai shiga wanka ne ya fito da komai na aljihun shi ya na ajewa akan gaban madubi, ya na aje ledar maganin Haseenah ta kalle shi tace "Oga wannan fa na miye haka?"
Ba tare da wani damuwa ba yace "Um, ba na fad'a mi ki zan karb'o wannan maganin ba a wajen Hajia? To ai sune na karb'o d'in, da k'yar ta bani su bayan na mata alk'awarin ba zan bari kowa ya sani ba."
Ya na fad'a ya shige wanka, zaune ta yi tana kallon magungunan har ya fito, cikin taushin murya tace "To yanzu ya za ka yi da su kenan? Za ka ci gaba da sha ne?"
Da k'arfi yace "Wa? Ni! Haba dai Hajia, kinga kawai d'auke su ma daga nan ki zuba su shara danni ko d'aya ba zanyi anfani da su ba."
Mik'ewa ta yi da wani mirmushin mugunta a fuskar ta ta kalle shi tace "Haka na ke son ji dama, dan ba na son namiji mai tsirfa kamar mace."
*Da dare* Usman da malam da kuma rakiyar Murtala da d'aya abokin nashi mijin Hajia Salamatu wato *Alhaji Salisu* suka je aka nemowa Nura auren sahibar shi *Choukra*, cikin girmamawa aka yi abin da za ayi aka gama kafin abin da zai biyo baya, ko da su ka dawo har gida suka fara aje malam in da ya umarci Usman da ya shigo su yi magana, suna shiga ya bashi ruwan addu'a yasha, ganin Nura a gidan ne ya sa yace ya je gida gobe da safe ya same shi kafin ya fita, da "To yah Fodio." Ya amsa kafin ya fito suka wuce.
*Washe gari* da safe Hajia Sadija ce ta yi sallama gidan surukan Khadija in da Mansur ke binta a baya, tarba ta musamman suka samun daga wajen Hajia da malam d'in kafin su ka nutsu, cikin dattako Mama tace "Nasan za ku yi mamakin gani na da sanyin safiyar nan, to ba wani abu bane dama face wani alkairi da ya tunkaro mu, shine na ce ba za mu yi farin cikin mu kad'ai ba, kuma da kuma Usman d'in ku na da hakk'in ku san me ke faruwa."
Malam ne yace "To gaskiya dai ba mu yi mamaki ba, abu d'aya da na ji shine fargaba, kuma bai wuce fargaban tunanin makomar auren yaran mu ba."
Murmushi ta yi tace "Malam kenan, kamar yanda na fad'a ne a farko alkairi ne ke tafe damu, kuma insha Allahu babu abin da zai shafi makomar auren yaran nan, yanzun ma k'addara ce kawai ta gifta a tsakanin su, amma komai zai daidaita da yardar Allah."
"Allah yasa haka Hajia." Cewar malam yayin da Hajia kuma tace "Allah ya yarda, ya kuma kawo mana k'arshen matsalar."
"Ameen ya Rabbi." Mama ce ta d'ora da "Dama dai ba wani abu bane Bilal ne za'a wa k'ane ko k'anwa idan Allah ya amince."
Da sauri duka suka kafe ta da ido kowa da mamaki, Mansur ma da kallo ya bita da mamaki, dan sam bai d'auka abin da zai kawosu ba kenan, amma ya zaiyi shiru ya yi ya na sauraren ikon Allah, Hajia ce tace "Wai Hajia ki na nufin Khadija juna biyu ne da ita?"
Dariya mama ta yi tace "K'warai kuwa."
Da tsantsar farin ciki tace "Kai Alhamdulillah, Allah abin godiya, Allah mun gode ma ka, gashi bayan shekaru goma sha uku za ka k'ara azurta baiwar ka da ni'imar ka wacce babu wanda ya isa ya bawa wani sai kai, baiwar da kud'i basa sayanta kuma alfarma bata bayar da ita."
Malam da hak'oran shi ke waje ya na faffad'an murmushi ne yace "Tabbas hakane, arzik'i ne da imanin ka ko kafircin ka bai isa ya baka shi ba, sai mai bayarwa ya ga damar baka."
"To wannan dai shine dama na ce bara mu zo mu fad'a mu ku, dan bai kamata ku kasa sani ba."
Malam ne yace "Gaskiya ne Hajia, kuma mun gode da wannan girmama mu da ku ke yi, Allah ya saka da alkairi."
"Ba komai wallahi." Mama ta fad'a ta na mik'ewa ta na gyara mayafin ta tana ci gaba da fad'in "Mu zamu wuce, dama zanje 'yar kasuwa ne na ce mu fara biyowa ta nan d'in."
Shi kam cewa ya ke to sai me, ai k'ane za'a mi shi dan haka bai damu ba, kuma idan ya na son hawan k'afafu ga nata nan zai hau, da haka har 'yan biyar su ka zo suma suka d'ora nasu farin cikin ana addu'ar Allah ya sauketa lafiya.
*Mu ma dai munce ameen.*
Kamar kullum Usman ya je gaishe da iyayen sa, kuma kamar yanda ya saba riska yau ma malam baya nan, sai dai ya bar sak'on wannan ruwan addu'ar a bashi ya sha, saida ya shanye Hajia ta fito daga ban d'aki tace "Tashi kaje ka yi wanka ruwa na nan na had'a ma ka."
Kasa magana ya yi saboda mamaki da kuma rashin sanin abin da zai fad'a, saida ta maimaita da "Ko ba ka ji ba ina magana?"
Saida ya gyara zama ya kalli jikin shi da kyau yace "Amma Hajia na yi wanka fa, wane irin wanka ne zanyi yanzu kuma?"
"Ka tashi ka shiga lokaci tafiya yake." Marairaicewa ya sake yi yace "Amma Hajia wai dan..." Katse shi ta yi da "In za ka tashi ka tashi kafin ka b'ata min rai."
Tashi ya yi kamar zai k'urma ihu saboda haushi, ya rasa irin wannan sabon al'amari na iyayen shi, haka ya tub'e kayan da ya sanyo yanzun ya yi wanka da wannan hakukuwan na magani, haka ya sanyo kayan ya fito duk ruwan jikin shi sun tsaya a kayan, ya na fitowa Hajia kuma ta bashi damammiyar fura da maganin jiya a ciki, saida ta masa jan ido yasha dan cewa ya yi jiya baiyi bacci ba, hakan ya sa ta bud'e mi shi ido sosai sannan ya sha, wata 'yar kwalba ta d'auko bak'a mai d'auke da maganin *jibda* a ciki, da kan ta ta lak'ato a hannu ta shafa mi shi a wuya zuwa kai da hannuwan shi har zuwa damatsenshi, bashi ta yi tace ya d'iba ya shafa a cikin shi har zuwa k'irji, kamar zaiyi kuka ya kalle ta yace "Hajia wai duk wannan na miye haka? Wannan abun nan amai zai saka ni, sam warin shi babu dad'i."
Shiru kawai ta yi ba tace komai ba dole ya shafa yanda take so, mik'ewa ya yi yace "Hajia ko za ki bani magungunan sai ki nuna min yanda ake sha, ina ga kamar hakan zaifi ko?"
Kallon shi ta yi tace "Alhaji, kai ka haife ni ko ni na haife ka?"
Cike da ladabi ya rusuna yace "A'a Hajia ki yi hak'uri, ban fad'i haka dan b'ata ran ki ba."
"To ka wuce ka tafi in da za ka je kawai, sannan ba na so ka fad'a wa wani ko wata batun magungunan nan, ko da kuwa matan ka ne ban yarda ba, kaji ni ko?"
"Naji Hajia, amma wallahi da gaske na le idan ki ka bani zanyi aiki da su, Hajia ki duba kiga hakan zaifi a gani na, misali yanzu na wankan nan, idan da a waje na yake da haka ba za ta faru ba, amma idan ya na nan zai zamana kullum sai na yi wanka anan kenan, sannan idan na yi tafiya za'a dakatar da maganin kenan har sai na dawo, sannan Hajia..."
"Dakata dallah." Ta katse shi tare da d'aga hannu, shiru ta yi ta jima ta na tunanin abin da ya fad'a kafin ta gamsu ta d'auko duka magungunan ta bashi, saida ya karb'a ta nuna mi shi yanda zaiyi aiki da su kafin ta sake jadadda mi shi bata so ko matar shi ta sani, alk'awari ya mata babu wanda zaiji dan haka ta bashi ya tafi, aljihu ya saka su ya fita daga gidan ya shiga harkokin gaban shi, sai yamma ya dawo gida cin abinci, zai shiga wanka ne ya fito da komai na aljihun shi ya na ajewa akan gaban madubi, ya na aje ledar maganin Haseenah ta kalle shi tace "Oga wannan fa na miye haka?"
Ba tare da wani damuwa ba yace "Um, ba na fad'a mi ki zan karb'o wannan maganin ba a wajen Hajia? To ai sune na karb'o d'in, da k'yar ta bani su bayan na mata alk'awarin ba zan bari kowa ya sani ba."
Ya na fad'a ya shige wanka, zaune ta yi tana kallon magungunan har ya fito, cikin taushin murya tace "To yanzu ya za ka yi da su kenan? Za ka ci gaba da sha ne?"
Da k'arfi yace "Wa? Ni! Haba dai Hajia, kinga kawai d'auke su ma daga nan ki zuba su shara danni ko d'aya ba zanyi anfani da su ba."
Mik'ewa ta yi da wani mirmushin mugunta a fuskar ta ta kalle shi tace "Haka na ke son ji dama, dan ba na son namiji mai tsirfa kamar mace."
*Da dare* Usman da malam da kuma rakiyar Murtala da d'aya abokin nashi mijin Hajia Salamatu wato *Alhaji Salisu* suka je aka nemowa Nura auren sahibar shi *Choukra*, cikin girmamawa aka yi abin da za ayi aka gama kafin abin da zai biyo baya, ko da su ka dawo har gida suka fara aje malam in da ya umarci Usman da ya shigo su yi magana, suna shiga ya bashi ruwan addu'a yasha, ganin Nura a gidan ne ya sa yace ya je gida gobe da safe ya same shi kafin ya fita, da "To yah Fodio." Ya amsa kafin ya fito suka wuce.
*Washe gari* da safe Hajia Sadija ce ta yi sallama gidan surukan Khadija in da Mansur ke binta a baya, tarba ta musamman suka samun daga wajen Hajia da malam d'in kafin su ka nutsu, cikin dattako Mama tace "Nasan za ku yi mamakin gani na da sanyin safiyar nan, to ba wani abu bane dama face wani alkairi da ya tunkaro mu, shine na ce ba za mu yi farin cikin mu kad'ai ba, kuma da kuma Usman d'in ku na da hakk'in ku san me ke faruwa."
Malam ne yace "To gaskiya dai ba mu yi mamaki ba, abu d'aya da na ji shine fargaba, kuma bai wuce fargaban tunanin makomar auren yaran mu ba."
Murmushi ta yi tace "Malam kenan, kamar yanda na fad'a ne a farko alkairi ne ke tafe damu, kuma insha Allahu babu abin da zai shafi makomar auren yaran nan, yanzun ma k'addara ce kawai ta gifta a tsakanin su, amma komai zai daidaita da yardar Allah."
"Allah yasa haka Hajia." Cewar malam yayin da Hajia kuma tace "Allah ya yarda, ya kuma kawo mana k'arshen matsalar."
"Ameen ya Rabbi." Mama ce ta d'ora da "Dama dai ba wani abu bane Bilal ne za'a wa k'ane ko k'anwa idan Allah ya amince."
Da sauri duka suka kafe ta da ido kowa da mamaki, Mansur ma da kallo ya bita da mamaki, dan sam bai d'auka abin da zai kawosu ba kenan, amma ya zaiyi shiru ya yi ya na sauraren ikon Allah, Hajia ce tace "Wai Hajia ki na nufin Khadija juna biyu ne da ita?"
Dariya mama ta yi tace "K'warai kuwa."
Da tsantsar farin ciki tace "Kai Alhamdulillah, Allah abin godiya, Allah mun gode ma ka, gashi bayan shekaru goma sha uku za ka k'ara azurta baiwar ka da ni'imar ka wacce babu wanda ya isa ya bawa wani sai kai, baiwar da kud'i basa sayanta kuma alfarma bata bayar da ita."
Malam da hak'oran shi ke waje ya na faffad'an murmushi ne yace "Tabbas hakane, arzik'i ne da imanin ka ko kafircin ka bai isa ya baka shi ba, sai mai bayarwa ya ga damar baka."
"To wannan dai shine dama na ce bara mu zo mu fad'a mu ku, dan bai kamata ku kasa sani ba."
Malam ne yace "Gaskiya ne Hajia, kuma mun gode da wannan girmama mu da ku ke yi, Allah ya saka da alkairi."
"Ba komai wallahi." Mama ta fad'a ta na mik'ewa ta na gyara mayafin ta tana ci gaba da fad'in "Mu zamu wuce, dama zanje 'yar kasuwa ne na ce mu fara biyowa ta nan d'in."