Sashe 18
Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Wani basaraken murmushi ya yi ya nufi d'aki yace "Godiya na ke Nana Khadija."
Zasu shiga d'akin Kabir ya d'aga murya daga waje yace "Kai fa na ke jira, wallahi yah Fodio kar ka manta da ni anan waje ka shiga harkar gaban ka, kasan dai nima matar ce da ni ko."
Shima d'ago muryar ya yi yace "Naji me mata, amma aljihunka ba ka da kud'in da zaka saka mai a moto, to waye zai ciyar maka da matar kenan, ko dai hak'uri take ci?"
K'arasa shiga d'akin su ka yi, k'amshin da ya daki hancin shi ne yasa shi lumshe ido, a hankali ya bud'a ido ya sauke akan gadon da shi ma zanin da aka shinfid'a sama fari da maron ne, kallon ta ya yi yace "Khadija kin wahalar min da kan ki dayawa fa."
Murmushi kawai ta yi ba tace komai ba, zai fara cire kaya Khadija ta nufi wajen wata k'aramar jakar ta ta hannu ta d'auko ta fito, a tsakar gida ta samu Kabir ya na ta shawagi shi kad'ai, bud'a jakar ta yi ta ta ciro yan jikka jikka har guda biyar mik'akk'u ta mik'o mi shi tace "Gashi wai a baka."
Da mamaki ya kalli hannunta yace "Inji shi?"
"Eh." Ta fad'a da murmushi, jim ya d'anyi kafin ya karb'a, dan shi dai a iya saninshi Usman na k'ok'ari da su sosai wajen yi mu su buk'atunsu, amma kyauta irin haka dai ta shiga tsakanin shi da su gaskiya da wahala, saboda shi kan shi ma ai ba k'arfi bane da shi, da wannan mamaki yace "Ki masa godiya matar yaya, nagode sosai, ni na wuce."
"Amma ai da ka jira shi sai ku ci abinci ko."
Cike da zolaya yace "Me ki ka dafa ne? Kinsan ni fa ina son abu mai dad'i."
Dariya ta yi tace "To ka tafi tafi kawai, dan nasan abin da na dafa ba lallai ya birge ka ba."
"Da alama dai ba kya so na ci ne, to na hak'ura ma bana ci."
Jin motsin Usman ya sa ta dawo ciki, da sauri ta karb'i abun tsane ruwan hannun shi ta d'auki kwandon sabulu ta kai ban d'akin ta dawo ta cika bokiti da ruwa ta kai mi shi, kallonta ya yi yace "To na shiga na yi ne? Ko kuma madam ce ke da wannan alhakin?"
Dariya ta yi kawai ta kama hannun shi su ka nufi ban d'akin, shine ya fara shiga ita kuma ta tsaya baya tana tunanin ta mi shi wankan kamar yanda k'awar ta tace? Ko kuma dai ta bar shi ya yi da kan shi, wata zuciyar ce tace ma ta to ai mijin ki ne, ya sanki kin san shi, dan haka babu kunya a wannan fanni tsakanin ma'aurata, shiga kawai ta yi ta fara gurza shi soso da sabulu, haka su ka fito ta gama shirya shi cikin k'ananan kaya na kanti, sai dai la'asar ta matso ya sa shi yin alwala ya nufi masallaci ya fara sallah, ya na dawowa su ka ci abinci tare kamar yanda su ka saba, daga kan teburin ya kashe ta da wani kallo yace "Khadija."
"Na'am." Ta d'ago ta na kallon shi, cikin taushin murya da nuna buk'atar shi yace "Kinyi kewata kuwa?"
Da idon ta nan masu kama da na mai jin bacci ta kalle shi tace "Dan ba ka gan ka akan gado na bane ka fad'i haka?"
Sai da ya d'an lashe baki yace "Da gaske? Kenan kema yanzu haka ki na jin abin da na ke ji?"
Da gangan ta d'auki kofin (cup) lemun shinkafar da ta yi ta zuba a rigarta a tsakiyar maman ta tana kallon shi tace "Ya ma fi wanda ka ke ji."
Taso da ita ya yi tsaye ya d'aga kan shi ya na kallon ta ya soma cire mata mab'allan rigar ta har sai da ya rabata da ita, rigar nonon da ta kamata ya cire ita maya jefar kafin ya sa harshe ya na lashe jikinta in da lemun ya zuba... *gyara kimtsi*.
*Misalin* 05:54, su na kwance akan gado ya kalleta yace "Khadija, kin mayar da ni babban mutum, ina godiya ga Allah da ya k'addara had'uwa ta da ke a lokacin da babu wanda ya yi tsammanin faruwar wani abu tsakani na da ke, sannan ina godiya a gare ki da ki ka zama yarinya mai hak'uri da zab'in iyayen ta da kuma tawwakali da hukuncin ubangiji, ina kuma godewa Ashir da ya yi tunanin had'a ni da ke har yanzu mu ke kwance akan gado d'aya a matsayin mata da miji, sannan ba zan manta da k'ok'arin iyaye na a kai na wanda su ka jajirce har sai da su ka ga kin zama mallaki na, tabbas duk wanda ya yi biyayya ga iyayen shi ba ya tab'ewa, ni shaida ne kuma na gani a zahiri, Khadija, zuwan nan da na yi na taho mi ki da tsaraba mai yawa, amma babbar tsarabar da na ke so na ga ta k'ayatar da ke ita ce *kyautar zuciya ta*."
Tashi ta yi daga kxance ta na kallon shi tace "Ka na nufin ka mallaka min zuciyar ka gaba d'aya?"
Sai da ya jinjina kai alamar tabbatarwa kafin yace "Hakane, kin cancanci fiye da wannan ma, dan da akwai abin da ya fi zuciya ta mahimmaci a gare ni, to da shi zan ba ki, dan a gaskiya ba zan iya ba ki rayuwa ta ba."
Da sauri ta kalle shi tace "Ka na nufin ba zaka iya sadaukar da kan ka ba wa ni?"
Da fuskar tausayi yace "A gaskiya ba zan iya ba."
Cikin rashin jin dad'i tace "Kenan akwai wata da ka ke so?"
"Akwai mana." Ya fadada murmushi, sai lokacin ta rarumo gilashin ta ta saka ta kalle shi da kyau, ganin idonta sun kawo ruwa ya sa ya saki dariya ya rumgume ta yace "Ina da wacce na ke so mana, ga ta a gaba na, Nana Khadija *baiwar Allah*, Khadija ke ce na ke so, ba zan iya sadaukar da rayuwa ta ba wa ke saboda da ke kad'ai na ke so na yi rayuwa, ina so na na k'are rayuwa ta tare da ke cikin farin ciki."
D'agowa ta yi daga jikinshi ta kai mi shi duka a k'irji ta na fad'in "Har ka tsorata ni."
Dariya ya yk yace "Hakan na nufin nima na samu shiga kenan a cikin wannan tattausar zuciyar?"
Sai da ta rumgume shi tace "Sosai ma, kai ne farko da ka fara shigar ta, kuma insha Allah kai ne za ka zama na k'arshe, saboda ka na shiga na rufe ta na kuma jefa makullin a cikin tekun maliya."
Sumbatar ta ya fara yi daga nan dai aka sake juyewa ni kuma na sake juyowa na fito😎,haka su ka dinga gudanar da rayuwar su abar sha'awa, sun manta da yanda ma aka yi su ka had'u, soyayyar su suke barjewa kawai, zan iya cewa daga cikin biyayyar da Usman ya wa iyayensa akan auren Khadija ce ta sa k'ofofin arzik'i su ka fara bud'e masa ta ko ina, ga kuma addu'a da kullum ya ke samu daga matar shi da iyaye da yan uwa akan k'ok'arin da ya ke da kowa, sosai ya ke samun ci gaba ta fannin kasuwancin da ya saka a gaba, duk da su na d'an samun k'arancin lokacin juna hakan bai hana Khadija taya shi murnar samun ci gaban ba, dan ta lura mutum ne mai son samun na kan shi ba ya kuma buk'atar taimakon kowa, dan ita kan ta yawan kyautar da take wa yan uwan shi da iyayen shi lokuta da dama ya na nuna rashin jin dad'in shi, musamman idan Kabir ko Mannir ko Nura da ke k'arami su ka zo ya ga ta d'auki kud'i masu yawa ta basu wasu lokuta ma har da sabulan wanka da turaruka, sai yai ta fad'a wai ta lalata su har Kabir da ke da aure, ita kam tausayin shi take ganin koyarwa ce ya ke sai wata a baka, duk da ya na fad'a ba ta daina ba saboda a ganinta ita ta na da halin da za ta yi mu su tun da yan uwan mijin ta ne, sannan duk wata ita ma yan uwan ta su kan turo mata kud'i daga cikin ribar da ake samu na kud'in ta da suke juya mata, haka dai har lokacin hutunta ya k'are ta ci gaba da zuwa makarantar ta cikin kwanciyar hankali, duk da mijinta ba mazauni bane, amma ta na gamsuwa da kulawar da ya ke nuna mata.
Zasu shiga d'akin Kabir ya d'aga murya daga waje yace "Kai fa na ke jira, wallahi yah Fodio kar ka manta da ni anan waje ka shiga harkar gaban ka, kasan dai nima matar ce da ni ko."
Shima d'ago muryar ya yi yace "Naji me mata, amma aljihunka ba ka da kud'in da zaka saka mai a moto, to waye zai ciyar maka da matar kenan, ko dai hak'uri take ci?"
K'arasa shiga d'akin su ka yi, k'amshin da ya daki hancin shi ne yasa shi lumshe ido, a hankali ya bud'a ido ya sauke akan gadon da shi ma zanin da aka shinfid'a sama fari da maron ne, kallon ta ya yi yace "Khadija kin wahalar min da kan ki dayawa fa."
Murmushi kawai ta yi ba tace komai ba, zai fara cire kaya Khadija ta nufi wajen wata k'aramar jakar ta ta hannu ta d'auko ta fito, a tsakar gida ta samu Kabir ya na ta shawagi shi kad'ai, bud'a jakar ta yi ta ta ciro yan jikka jikka har guda biyar mik'akk'u ta mik'o mi shi tace "Gashi wai a baka."
Da mamaki ya kalli hannunta yace "Inji shi?"
"Eh." Ta fad'a da murmushi, jim ya d'anyi kafin ya karb'a, dan shi dai a iya saninshi Usman na k'ok'ari da su sosai wajen yi mu su buk'atunsu, amma kyauta irin haka dai ta shiga tsakanin shi da su gaskiya da wahala, saboda shi kan shi ma ai ba k'arfi bane da shi, da wannan mamaki yace "Ki masa godiya matar yaya, nagode sosai, ni na wuce."
"Amma ai da ka jira shi sai ku ci abinci ko."
Cike da zolaya yace "Me ki ka dafa ne? Kinsan ni fa ina son abu mai dad'i."
Dariya ta yi tace "To ka tafi tafi kawai, dan nasan abin da na dafa ba lallai ya birge ka ba."
"Da alama dai ba kya so na ci ne, to na hak'ura ma bana ci."
Jin motsin Usman ya sa ta dawo ciki, da sauri ta karb'i abun tsane ruwan hannun shi ta d'auki kwandon sabulu ta kai ban d'akin ta dawo ta cika bokiti da ruwa ta kai mi shi, kallonta ya yi yace "To na shiga na yi ne? Ko kuma madam ce ke da wannan alhakin?"
Dariya ta yi kawai ta kama hannun shi su ka nufi ban d'akin, shine ya fara shiga ita kuma ta tsaya baya tana tunanin ta mi shi wankan kamar yanda k'awar ta tace? Ko kuma dai ta bar shi ya yi da kan shi, wata zuciyar ce tace ma ta to ai mijin ki ne, ya sanki kin san shi, dan haka babu kunya a wannan fanni tsakanin ma'aurata, shiga kawai ta yi ta fara gurza shi soso da sabulu, haka su ka fito ta gama shirya shi cikin k'ananan kaya na kanti, sai dai la'asar ta matso ya sa shi yin alwala ya nufi masallaci ya fara sallah, ya na dawowa su ka ci abinci tare kamar yanda su ka saba, daga kan teburin ya kashe ta da wani kallo yace "Khadija."
"Na'am." Ta d'ago ta na kallon shi, cikin taushin murya da nuna buk'atar shi yace "Kinyi kewata kuwa?"
Da idon ta nan masu kama da na mai jin bacci ta kalle shi tace "Dan ba ka gan ka akan gado na bane ka fad'i haka?"
Sai da ya d'an lashe baki yace "Da gaske? Kenan kema yanzu haka ki na jin abin da na ke ji?"
Da gangan ta d'auki kofin (cup) lemun shinkafar da ta yi ta zuba a rigarta a tsakiyar maman ta tana kallon shi tace "Ya ma fi wanda ka ke ji."
Taso da ita ya yi tsaye ya d'aga kan shi ya na kallon ta ya soma cire mata mab'allan rigar ta har sai da ya rabata da ita, rigar nonon da ta kamata ya cire ita maya jefar kafin ya sa harshe ya na lashe jikinta in da lemun ya zuba... *gyara kimtsi*.
*Misalin* 05:54, su na kwance akan gado ya kalleta yace "Khadija, kin mayar da ni babban mutum, ina godiya ga Allah da ya k'addara had'uwa ta da ke a lokacin da babu wanda ya yi tsammanin faruwar wani abu tsakani na da ke, sannan ina godiya a gare ki da ki ka zama yarinya mai hak'uri da zab'in iyayen ta da kuma tawwakali da hukuncin ubangiji, ina kuma godewa Ashir da ya yi tunanin had'a ni da ke har yanzu mu ke kwance akan gado d'aya a matsayin mata da miji, sannan ba zan manta da k'ok'arin iyaye na a kai na wanda su ka jajirce har sai da su ka ga kin zama mallaki na, tabbas duk wanda ya yi biyayya ga iyayen shi ba ya tab'ewa, ni shaida ne kuma na gani a zahiri, Khadija, zuwan nan da na yi na taho mi ki da tsaraba mai yawa, amma babbar tsarabar da na ke so na ga ta k'ayatar da ke ita ce *kyautar zuciya ta*."
Tashi ta yi daga kxance ta na kallon shi tace "Ka na nufin ka mallaka min zuciyar ka gaba d'aya?"
Sai da ya jinjina kai alamar tabbatarwa kafin yace "Hakane, kin cancanci fiye da wannan ma, dan da akwai abin da ya fi zuciya ta mahimmaci a gare ni, to da shi zan ba ki, dan a gaskiya ba zan iya ba ki rayuwa ta ba."
Da sauri ta kalle shi tace "Ka na nufin ba zaka iya sadaukar da kan ka ba wa ni?"
Da fuskar tausayi yace "A gaskiya ba zan iya ba."
Cikin rashin jin dad'i tace "Kenan akwai wata da ka ke so?"
"Akwai mana." Ya fadada murmushi, sai lokacin ta rarumo gilashin ta ta saka ta kalle shi da kyau, ganin idonta sun kawo ruwa ya sa ya saki dariya ya rumgume ta yace "Ina da wacce na ke so mana, ga ta a gaba na, Nana Khadija *baiwar Allah*, Khadija ke ce na ke so, ba zan iya sadaukar da rayuwa ta ba wa ke saboda da ke kad'ai na ke so na yi rayuwa, ina so na na k'are rayuwa ta tare da ke cikin farin ciki."
D'agowa ta yi daga jikinshi ta kai mi shi duka a k'irji ta na fad'in "Har ka tsorata ni."
Dariya ya yk yace "Hakan na nufin nima na samu shiga kenan a cikin wannan tattausar zuciyar?"
Sai da ta rumgume shi tace "Sosai ma, kai ne farko da ka fara shigar ta, kuma insha Allah kai ne za ka zama na k'arshe, saboda ka na shiga na rufe ta na kuma jefa makullin a cikin tekun maliya."
Sumbatar ta ya fara yi daga nan dai aka sake juyewa ni kuma na sake juyowa na fito😎,haka su ka dinga gudanar da rayuwar su abar sha'awa, sun manta da yanda ma aka yi su ka had'u, soyayyar su suke barjewa kawai, zan iya cewa daga cikin biyayyar da Usman ya wa iyayensa akan auren Khadija ce ta sa k'ofofin arzik'i su ka fara bud'e masa ta ko ina, ga kuma addu'a da kullum ya ke samu daga matar shi da iyaye da yan uwa akan k'ok'arin da ya ke da kowa, sosai ya ke samun ci gaba ta fannin kasuwancin da ya saka a gaba, duk da su na d'an samun k'arancin lokacin juna hakan bai hana Khadija taya shi murnar samun ci gaban ba, dan ta lura mutum ne mai son samun na kan shi ba ya kuma buk'atar taimakon kowa, dan ita kan ta yawan kyautar da take wa yan uwan shi da iyayen shi lokuta da dama ya na nuna rashin jin dad'in shi, musamman idan Kabir ko Mannir ko Nura da ke k'arami su ka zo ya ga ta d'auki kud'i masu yawa ta basu wasu lokuta ma har da sabulan wanka da turaruka, sai yai ta fad'a wai ta lalata su har Kabir da ke da aure, ita kam tausayin shi take ganin koyarwa ce ya ke sai wata a baka, duk da ya na fad'a ba ta daina ba saboda a ganinta ita ta na da halin da za ta yi mu su tun da yan uwan mijin ta ne, sannan duk wata ita ma yan uwan ta su kan turo mata kud'i daga cikin ribar da ake samu na kud'in ta da suke juya mata, haka dai har lokacin hutunta ya k'are ta ci gaba da zuwa makarantar ta cikin kwanciyar hankali, duk da mijinta ba mazauni bane, amma ta na gamsuwa da kulawar da ya ke nuna mata.