← Book details Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 86

Sashe 12

Kallon Kitse Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ta na shan majina ta wuce zuciyar ta ba dad'i ko kad'an, tun da suka je gida daf da magrib sun samu duk yan uwan ta sun dawo daga uzurirrikansu ban da Naseer dake karatu a *France*, yanda ta shigo tana kumboro baki ta na murzar ido ta cire gilashi ne ya sa Ashir zaburowa ya kamo hannun ta yana fad'in "Auta lafiya? Me ya same ki kike kuka?"

Zaunar da ita ya yi ya karb'i gilashin ya maida mata ya kalli Kaltume yace "Umma waya tab'a ta?"

Cikin taushin murya Kaltume tace "Wani tsoho ta bige, ita ma kuma ta fad'i, amma duk ta damu."

Bashir da Mansur a zabure suka matso Bashir na fad'in "Subhanallah, auta ba ki ji ciwo ba?"

Dukansu duba jikin ta suke ko sunga ciwo amma shiru, Mama na gefe tana kallonsu ta yi shiru, a hankali Khadija ta janye siket d'in ta ta nuna musu in da take jin zafi, wajen har ya yi bak'i ai sai suka zabura da ganin wannan d'an ciwo, da gudu Habeeb ya wuce d'akin shi ya d'auko maclean dan a shafa mata, tuni kuma Bashir da Ashir sun umarci matansu da su d'auko musu suma, sai ga abun wanke hak'ora har hud'u a gaban su, nan dai suka shafa mata akayita lallab'a ta har zuwa dare.

Kwance take a d'akin ta cikin bargo yayin da suk yan uwan ke kewaye da ita sai kanta dake kan k'afafun mama, d'aya hannunta na sak'ale cikin hannun Habeeb ya na shafawa, sai mama dake shafar kanta Ashir kuma na karanta mata wani littafi mai sunan *magana jari*, lumshe ido take sosai ta na so tayi bacci, janyo hannun ta tayi daga hannun Habeeb ta tusa shi ta k'asan gilashinta ta murza idon ta tana turo baki gaba, ganin ta rufe ido ya sa Ashir matsowa kusan fuskarta yace "Auta."

Bud'a ido ta yi ta kalle shi, cikin murya k'asa k'asa yace "Albishirinki."

"Goro." Ta fad'a ta lumshe ido, d'orawa ya yi da "Na biya mi ki kujerar hajj, tare da Mama za ku tafi wannan karan insha Allah."

Zunbur ta tashi zaune tace "Da gaske yah Ashir? Kai amma naji dad'i sosai, nagode."

Da k'arfi mama ta maida kanta akan cinyar ta tace "Dan Allah ki kwanta ki yi bacci ko muma mun samu mu rintsa."

Daddab'a ta ta ci gaba da yi har bacci ya d'auke ta, addu'a mama ta shafa mata Mansur ya cire mata gilashin ya aje mata gefenta kafin suka kashe mata wutar d'akin suka fita, har ga Allah wannan kulawar da suke nuna mata Mama tasan ta yi yawa, haka kuma matar Bashir da Ashir suna jin haushin hakan, saboda kai tsaye suna nuna musu farin cikinta yafi nasu, kulawar da suke nuna mata basa nuna musu kwatankwacin ta, shi ya sa mama ke fatan su rage ko dan kasancewar ta ya mace, dan ma ita d'in yarinya ce mai son aiki da kazar-kazar.

*Allah ka k'ara mana k'oshin lafiya, sis Alawiyya Allah ya baki lafiya.*
12/01/2020 à 22:18 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑
*KALLON KITSE*
_(Ake wa rogo)_
💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑

_SAMIRA HAROUNA_

*Littatafan marubuciyar*

*1* _KAUSSAR_
*2* _D'AUKAR FANSA_
*3* _BA SO BANE_
*4* _AUREN HAD'I_
*5* _SANIN MASOYI_
*6* _JIHADI_
*7* _K'ANGIN RAYUWA_
*8* _ITACE K'ADDARARMU_
*9* _KAWU NA NE_
*10* _MAATA_
*11* _KALLON KITSE..._

*SADAUKARWA GA*

_MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)*

🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S*
_(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛

```Fatan alkairi masoya```

_Bismillahir rahamanir rahim_

*10*

Washe gari da safe Khadija ta shirya su ka tafi tare da Habeeb ya kai ta gidan tsohon da ta bige, sai da aka mu su kwatance su ka isa gidan, a k'ofar gidan Habeeb ya tsaya ita ta wuce ciki ta na rabka sallama tun daga soro, kasancewar safiya ce kusan matasan gidan ba su riga sun tafi harkokinsu ba, dan wasu ma su na cin d'umamen tuwo ta same su, izini aka mata ta shiga ciki, gaba d'aya ta had'e tace "Ina kwanan ku."

"Lafiya k'alau." Aka amsa mata, d'orawa ta yi da "Antashi lafiya."

"Lafiya lau mu ka tashi."

"Ya mai jiki?" Ta fad'a ta na d'an kallon tsohuwar, da fara'a tsohuwar tace "Mai jiki da dama."

Da mamaki tsohuwar ta kalleta a nutse tace "Sannu ko yan mata?"

"Sannu Mama." Ta fad'a da murmushin ta, tsohuwar ce tace " Sai dai kuma ban shaida ki, gashi na ji har ki na tambayar jikin malam ko?"

Da k'ayataccen murmushi tace "Eh mama, na zo duba jikin su ne, ba za ku shaida ni ba dama, ni ce hatsarin nan ya faru tare da ita."

"Ayyah! Sannu ko, mai jiki ai da sauk'i, yanzu ma haka fitowa ya yi zai fita shago, babban yaron na shi ne ya hana shi yace ya koma ya kwanta, ya na ciki, muje na rakaki ki gan shi."

Ledar hannunta ta sake mayar da ita d'aya hannun saboda nauyin ta kafin ta wuce, ta cire takalmi za ta shiga kenan Usman shi kuma ya fito, saida jikinsu ya had'e da sauri ta ja baya, sai dai kuma ta na ja da baya ta kai wa tsohuwar karo, da azama ta sake matsawa ta na fad'in "Yi hak'uri, yi hak'uri dan Allah."

Wani banzan kallo Usman ya mata ya rab'ata ya wuce ya saka takalmin shi, Khadija kam ajiyar zuciya ta saune ta k'arasa shiga ciki, zaune ta yi kusan katifar da tsohon ke zaune ta aje ledar hannun ta, da murmushi tace "Baba ya jiki?"

Shima da murmushin yace "Jiki da sauk'i 'yata, ya na ki jikin? Ince dai ba ki ji ciwo ba ko?"

"A'a Baba, ban ji ciwo ba."

"To Allah ya k'ara kiyayewa, Allah ya kare mu daga sharrin k'arfe."

"Amee Baba, kuma dan Allah ka yi hak'uri, laifi na ne abin da ya faru."

"Ah haba haba, 'yata ba laifin ki bane, Allah ne ya aiko ai, sai dai Allah ya k'ara kiyayewa, kuma ku dinga kula ku na tafiya a hankali."

"Insha Allah Baba, nagode, ni zan wuce."

Tsohuwar ce tace "Sai tafiya y'ar nan, ko ruwa baki sha ba."

Da fara'a tace "Ba komai mama, ai daga na ke, kuma tare da yaya na mu ke, ya na sauri zai fita aikin shi na tsayar da shi."

"Kuma gaskiya hakane kam karki tsayar da shi."

Tashi ta yi ta fito ta musu sallama, tun ranar kuma Khadija ba ta sake samun damar dawowa gidan ba saboda shirye shiryen tafiyar su k'asa mai tsarki, haka lokacin tafiya ya yi kuma su ka tafi sama tare da mama da matar Ashir da ta Bashir, dan dama an had'a su da mama ne saboda dukansu zuwan su ne na farko, masha Allah sun je lafiya kuma sun dawo lafiya, dukansu sun canza musamman Khadija da dama Allah ya hallice ta da kyanta, inda ta k'awata haurunan ta da hak'oran makka guda biyu, saida su ka yi sati su na karb'ar bak'i da huta gajiya, sai dai har lokacin nan Khadija na tunanin tsohon da ta buge, tunanin ta kawai ita ce silar kwantawar shi, dan haka ta shirya da dare tare da ware kayan tsaraba dan ta kai mu su, sanye take cikin bak'ar doguwar riga har k'asa mai walkiya da kwalliya, takalma sai d'an kwalin da ta mi shi sassauk'an aji a saman kan ta, farin gilashin ta mai kewaye da bak'ar kala ya dace da fuskar ta da kuma rigar, farin man leb'e ne kawai ta shafa, yau kuma Naseer ne ya shirya zai kai ta wanda ya zo hutu, har k'ofar gidan ya dire ta shi kuma ya fito ya tsaya bakin motar, ta na zura kai cikin soron sai duhu, wayarta ta fara k'ok'arin fitowa da ita daga cikin k'aramar jakarta sai kawai ta ji ta zube a k'asa, 😂 "Ahhhhhh."

K'arar da ta saki kenan lokacin da Usman ya yi gaba da ita ta fad'i zaune a k'asa, wayarta da ledar hannun ta da kuma gilashi duka sun kama gabansu, da sauri Usman ya kunna wutar ta shi wayar dan ganin wacece, " *mai gilashi*." Abinda ya fad'a kenan, sai dai mamaki ne ya lullub'e shi ganin Khadija nata lalubar inda gilashinta ya ke, tambayar da ta zo mi shi ita ce "Ba ta gani ne? Ko kuma har yanzu duhun take gani?"

Ya na kallon ta har ta kai hannunta kan gilashin ta, da saurita d'auka ta mak'ala a ido, tarau taga Usman zik'au a gabanta da hasken fitila, da sauri ta mik'e tsaye ta na tattare kayan da su ka zube, shi kam sai ya ji ta ma ba shi haushi, guntun tsaki ya yi ya wuce ta cikin b'acin rai ya fice daga gidan yana fad'in "Idan dai ki ka ci gaba da anfani da gilashi haka kawai, wallahi kin kusa zama makauniya, in banda hauka har cikin dare ma sai kinyi fama da gilashi, kuma yanzu haka ma na masu larurar ido ne take sakawa."

Ya na fitowa ya ga Naseer tsaye, gaisawa su ka yi cikin sanin juna, dan da Usman da Ashir sunyi aji d'aya a makarantar boko, hakan ya sa su ka zama abokai sai dai ba abota irin sosai d'in nan ba, ita ma data shiga ciki k'anan Usman da suke uba d'aya ne ya mata iso har d'akin babansu, bai gusa daga wajen ba ya na kallon fuskarta da murmushin ta ya na jin kamar yace ya na son ta, har ta taso ta fito ya rakota k'ofar gida, kallon juna su ka yi ita da Usman da suke ta hira da Naseer, sallama su ka yi Naseer ya shiga mota ita kuma ta juya ta kalli *Mannir* tace "To sai anjima ko."

"Sai anjima, sai yaushe kuma?"

D'an wasa ta yi da idon ta tace "Kowane lokaci ma za ka iya gani na."

"Shikenan to, sai anjima."
Chapter 12 · 0% Book details