Sashe 9
Abin Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta bata amsa tana zama a karamar kujera, ta buÉ—e ledan taga kwalin waya wato sabuwa ya siya mata kimanin na dubu hamsin da biyar, wani tsalle ta daka tana murna tare da cewa.
Inna waya toch ya siya mini wlh kin ganta sabuwa dal a kwali.
Allah yasa ba matsa masa kika yi ya siya miki ba dan nasan halinki.
Kai innata! wlh hakanan yaji ra'ayin kawo mini wata kila ya samu KuÉ—i ne ko kin mance siyayyar daya yi mini shekaran jiya.
To Allah ya sanya alkhairi ya yi masa albarka. Amma ni nafi son ya turo ayi maganar auren nan zanfi samin natsuwa.
Inna tunda shi yace a bashi lokaci a jirashi, in kuma rabon wani ya ratsa ya yiwa kansa.
Me kike nufu da wannan maganar? Najwa ko dai yaudarar yaron nan kike ba sonsa kike yi ba kisa muji kunya?
Da bana sonsa inna ai bazan bari soyayyarmu tayi tsawo haka ba, kusan shekara guda fa muna tare.
Hmmm inna tace tayi bismillah ta fara alwalar sallar la'asar, Najwa kuwa ta miƙe ta shiga ɗaki ta saka wayar a caji cikin tsananin murna, ta duba takardan dake cikin ledan ta karanta sakon bada haƙuri ne, murmushi tayi tana mele baki, duk da wannan hidimar da yayi mata baisa ta sauko daga ƙudurinta ba dan gani take yi ma ta samu abinda zai sa ta samu kusanci da Aminu.
...
Ana gobe walima.
Najwa ta shirya tsaf ta tafi gidan Sameeha da nufin kwana zata yi, sai dai zuwanta da dalili saboda tana son ta samu number ɗin Aminu a wayar Sameeha, dan ta buɗe facebook tayi searching sunansa amma bata samu ba, ta san koda baya facebook to yana WhatsApp dan haka ta ke buƙatar number, saboda shawarar da suka yi kenan da Nafeesa a chat, dan tuni suka cigaba da tsare tsarensu ta online, sosai Nafeesa taji daɗin Wayar da Najwa ta samu dan ya ƙara musu kusanci da juna kuma zasu riƙa yin komai a waya ba lallai dole sai sun haɗu ba. Tana isa ta samu ana ta shirya kujeru a kasan kanofi da aka kafe su guda huɗu a tsakar gidan, tuni Sameeha ta saka aka samo mata hayarsu zuwa gobe zasu zo su kwashe, dan so take komai a yi shi cikin tsari, maganar abinci ma bayarwa tayi a yi musu bata so ta bawa Kowa aiki, tasa ayi waina da sinasir da miya, jelop din shinkafa da alale sai kaji guda talatin da aka gyaresu suna aikin suyansu ita da Ikram sai Mai aikinta, akwai rago da yaya Kamalu yace za a gasa shi a kawo musu goben, sai drinks kuma da ruwa gasu nan katam katam da yaya Kamalu ya kawo dan shine Aminu ya bawa kuɗin siyayya. Najwa tana shiga falon da sallama bata samu kowa ba dan duk suna kitchen, sai ta sauke idonta a kan katon hoton Aminu dake manne a bango ga kuma wanda suka ɗauka tare da Sameeha da kuma wanda suka ɗauka da yaran, sai ta sauke ajiyar zuciya a hankali tana cewa a zuciyarta.
'In Sha Allah saika zama mallakina sai na yi mulki a cikin zuciyarka.'
Sai ta wuce zuwa kitchen ta samesu sunata aikin suyan kaji, suka shiga murnan ganinta Ikram tana cewa.
Oyoyo matar babban yaya, ashe zaki zo?
Haba zan zo mana tunda ni nace zan zo ai. Ina yini anty Sameeha ya shirye shirye?
Lafiya lau Alhamdulillahi Najwa, yasu inna fatan kowa lafiya.
Lafiya lau sun ce a gaisheki. Inna tace ba zata samu zuwa ba saboda akwai suna a nan gida kawo.
Allah sarki nima badan taron nan ba da dani za ayi sunan, amma In Sha Allah zan je inyi musu barka.
Allah ya yarda, yanzu me zan tayaku dashi?
Zo ki karɓi suyarnan in je in watsa ruwa dan zafi nake ji.
Cewar Sameeha, Najwa tace to amma zata aje jaka ta dawo, sai ta fita ta shiga É—akin Amrah ta aje jakarta ta cire hijab ta dawo ta amsa aikin, Sameeha ta tafi É—aki ta barsu, Najwa ta kalli Ikram tana murmushi.
Bakuwa Anty tayi ne?
A'a Jamila ai 'yar aiki ce da su yaya Hauwa suka kawota.
Ashe har ta zo, 'yan mata sannunki.
Yauwa Jamila ta bata amsa a takaice, kiran daya shigo wayar Ikram ce yasa ta miƙe ta fita daga kitchen ɗin, a lokacin dabara ta faɗowa Najwa tace cikin jan Jamila da hira.
Sun barki kin É—anÉ—ana kazar kuwa?
Sun bani amma kin san kaza bata isata tunda gida babu maƙota sai ɗai ɗai.
Ɗauko ledan can ki ɗiba iya yadda kike so kije ɗakinki ki ɓoye kici abinki hankali kwance, nima kinga zan ɗiba kasona kafin su zo dan nasan halin Anty akwai rowar tsiya.
Jikin jamila yana rawa ta ɗauki baƙar leda ta ɗiba kazar iya son ranta ta fita da sauri ta shiga ɗakinta ta ɓoye kana ta dawo tana washe baki cike da mugun farin ciki.
Amma ke 'yar uwar mai gidan ce ko? Dan na kula danginsa basa shiri da anty.
Hmmm ni ƙanwarta ce amma babanta shine yayan mamana, sai dai ni ina zuwa ne saboda takurani da inna tayi, dan sam Anty Sameeha ba tada kirki.
Ai naga alama dan tunda na zo gidan nan take zuba mini dokoki ga shegen saka mini ido, abu kaɗan nayi suke kyarata ita da ƙanwarta, gaskiya naga ke kina da kirki ba halinku ɗaya ba.
Hmmm sai ma gobe zaki ga yadda zata yiwa 'yan uwan mijinta, sam basa jin daÉ—inta ni har tausayinsu nake.
Cewar Najwa tana taɓe baki, a zuciyarta kuma tana jin wani daɗi da farin ciki dan ta samu Jamila zata fara aika sakonta gurin su Hauwa, saboda ta san sun turota ne wu riƙa samun labarai a gurinta, kuma ga dukkan Alamu Jamila zata yi mata matuƙar amfani a cikin rawar da zata taka a gidan, muryar Jamila taji tana cewa a hankali dan kar ajita.
Kin san Allah na tsani matar nan addu'a nake Allah yasa Alhaji ya saketa ya auro mai mutunci.
Hmmm da nine 'yan uwansa sai na saka sun yi mata kishiya.
Cewar Najwa itama a hankali, Jamila ta saka dariya tana cewa.
Wlh kuwa da nayi murna naga ƙarshen ɗaga kai.
Jamila sunanki ko?
Eh.
Ina so za ki yi mini wani abu wanda zan biyaki da kuɗi mai tsoka amma ina so ya zama sirri a tsakaninmu, idan kika faɗawa wani wlh sai na saka an ɓatar dake dan mijin da zan aura soja ne kina yi mini ba daidai ba zan saka ya harbeki da bindigarsa.
Wlh zanyi miki kome kika so in dai zaki biya ni, amma dan Allah karki saka a harbeni.
Jamila ta faÉ—a tana zare ido, Najwa ta saka dariya tana cewa.
Ke wasa nake miki naga duk kin firgita ne, kawai dai zolayarki nayi, amma naga tamu ta zo ɗaya bani number ɗinki ko gaisawa mu riƙa yi.
Sai a lokacin Jamila ta samu kwanciyar hankali ta saki murmushi tana ce mata wayarta tana ɗaki anjima zata bata, Najwa tace to suka cigaba da aiki, sai dai ita Najwa da abinda take saƙawa a cikin zuciyarta, haka nan taji ta gwada Jamila dan ta hasko ƙila nan gaba tayi mata amfani, kuma ta kula yarinyar akwai wayo da son kuɗi, ta tabbatar da hakane su Hauwa suka yi amfani suka ja ra'ayinta ta zo aiki gidan, itama zata yi amfani da wannan damar wajen samun cikar burinta.
[7/7, 13:04] BuhainatðŸ˜: *ABIN DA CIWO*
Na
©Rahma Kabir MrsMG.
Wattpad @rahmakabir
Page 7.
Ikram da ta dawo kitchen ɗin ta cewa Jamila taje ta gyara falo inji Anty Sameeha saboda gobe ba za shi sharaba sai zuwa yamma in baƙi sun tafi, Jamila ta miƙe ta fita Ikram ta zauna suka cigaba da aikin suna hira da Najwa, har suka gama suka a dana komai kafin suka fito Jamila ta soma gyaransa. Suna zaune a falo sai ga Anty Sameeha ta fito cikin doguwar rigar material da hula akanta, ta zauna a cushing tana cewa.
Ikram yanzu na gama waya da Aminu yace in kulle ɗakina dana rana kar na bari a shiga ayi mana barna, dama bana gaya miki haka zanyi ba to shima yanzu ya gama faɗa mini, dan haka ku shirya da wuri ku ɗauki duk abinda kuke buƙata ku kai shi ɗakin Jamila dan a can zamu tare, shima key ɗinsa yana hannunna koda zaku ɗauki abu sai ku faɗa mini.
Gaskiya gwara ayi haka dan bamu san mutanen da zamu zo ba Anty, tunda wannan ne karo na farkon taro da za kiyi a gidan, sannan ma a farfajiya za ayi walimar.
Cewar Ikram Sameeha tace.
Sosai ma ni da ban san ya halinsu yake ba gwara in yi wa abin tufkar hanci a rabu lafiya da kowa, ni wlh na ƙosa ma ayi a gama na huta.
Ai Anty kunyi ƙoƙari a wannan marra da muke ciki zaku yi shagali ba biki ba suna ba, kawai dan kun dawo kaduna ne fa.
To Najwa Aminu yace za a yi haka shiyasa nima na mara masa baya, gwara ayi É—in a sada zumunci dan da yawan 'yan uwansu ma ban sansu ba.
Cewar Sameeha sai ta cigaba da yi musu bayanin yadda take so su saka mata ido a gidan dan ita ba lallai ta samu damar yin haka ba saboda tarban mutane. Sai da aka kira sallamar magrib kafin suka miƙe kowa wanne ya nufi ɗaki domin yin salla. Jamila tana ɗakinta zaune tana huta gajiyar aiki data kwasa, sai kira ya shigo wayarta ta duba taga Hauwa ce sai ta mike ta zo ta rufe ƙofarta da key ta ciki ta koma ta zauna a bakin gado ta ɗauki wayar da sauri dan ta kusa tsinkewa.
Jamila meke wakana a gidan?
Jamila ta shiga karanto mata shirye shiryensu tana cewa.
Hajiya ai wlh na ci nama sosai wata 'yar uwar Anty Sameeha ta ce na ɗiba na ɓoye saboda tasan anty da baƙar rowa, itama sai zaginta take da alama 'yan uwanta suma basa jin daɗinta.
Hmmm ba mamaki suma ba mutunta su take yi ba, In Sha Allah da wuri ma zan zo gidan.
Inna waya toch ya siya mini wlh kin ganta sabuwa dal a kwali.
Allah yasa ba matsa masa kika yi ya siya miki ba dan nasan halinki.
Kai innata! wlh hakanan yaji ra'ayin kawo mini wata kila ya samu KuÉ—i ne ko kin mance siyayyar daya yi mini shekaran jiya.
To Allah ya sanya alkhairi ya yi masa albarka. Amma ni nafi son ya turo ayi maganar auren nan zanfi samin natsuwa.
Inna tunda shi yace a bashi lokaci a jirashi, in kuma rabon wani ya ratsa ya yiwa kansa.
Me kike nufu da wannan maganar? Najwa ko dai yaudarar yaron nan kike ba sonsa kike yi ba kisa muji kunya?
Da bana sonsa inna ai bazan bari soyayyarmu tayi tsawo haka ba, kusan shekara guda fa muna tare.
Hmmm inna tace tayi bismillah ta fara alwalar sallar la'asar, Najwa kuwa ta miƙe ta shiga ɗaki ta saka wayar a caji cikin tsananin murna, ta duba takardan dake cikin ledan ta karanta sakon bada haƙuri ne, murmushi tayi tana mele baki, duk da wannan hidimar da yayi mata baisa ta sauko daga ƙudurinta ba dan gani take yi ma ta samu abinda zai sa ta samu kusanci da Aminu.
...
Ana gobe walima.
Najwa ta shirya tsaf ta tafi gidan Sameeha da nufin kwana zata yi, sai dai zuwanta da dalili saboda tana son ta samu number ɗin Aminu a wayar Sameeha, dan ta buɗe facebook tayi searching sunansa amma bata samu ba, ta san koda baya facebook to yana WhatsApp dan haka ta ke buƙatar number, saboda shawarar da suka yi kenan da Nafeesa a chat, dan tuni suka cigaba da tsare tsarensu ta online, sosai Nafeesa taji daɗin Wayar da Najwa ta samu dan ya ƙara musu kusanci da juna kuma zasu riƙa yin komai a waya ba lallai dole sai sun haɗu ba. Tana isa ta samu ana ta shirya kujeru a kasan kanofi da aka kafe su guda huɗu a tsakar gidan, tuni Sameeha ta saka aka samo mata hayarsu zuwa gobe zasu zo su kwashe, dan so take komai a yi shi cikin tsari, maganar abinci ma bayarwa tayi a yi musu bata so ta bawa Kowa aiki, tasa ayi waina da sinasir da miya, jelop din shinkafa da alale sai kaji guda talatin da aka gyaresu suna aikin suyansu ita da Ikram sai Mai aikinta, akwai rago da yaya Kamalu yace za a gasa shi a kawo musu goben, sai drinks kuma da ruwa gasu nan katam katam da yaya Kamalu ya kawo dan shine Aminu ya bawa kuɗin siyayya. Najwa tana shiga falon da sallama bata samu kowa ba dan duk suna kitchen, sai ta sauke idonta a kan katon hoton Aminu dake manne a bango ga kuma wanda suka ɗauka tare da Sameeha da kuma wanda suka ɗauka da yaran, sai ta sauke ajiyar zuciya a hankali tana cewa a zuciyarta.
'In Sha Allah saika zama mallakina sai na yi mulki a cikin zuciyarka.'
Sai ta wuce zuwa kitchen ta samesu sunata aikin suyan kaji, suka shiga murnan ganinta Ikram tana cewa.
Oyoyo matar babban yaya, ashe zaki zo?
Haba zan zo mana tunda ni nace zan zo ai. Ina yini anty Sameeha ya shirye shirye?
Lafiya lau Alhamdulillahi Najwa, yasu inna fatan kowa lafiya.
Lafiya lau sun ce a gaisheki. Inna tace ba zata samu zuwa ba saboda akwai suna a nan gida kawo.
Allah sarki nima badan taron nan ba da dani za ayi sunan, amma In Sha Allah zan je inyi musu barka.
Allah ya yarda, yanzu me zan tayaku dashi?
Zo ki karɓi suyarnan in je in watsa ruwa dan zafi nake ji.
Cewar Sameeha, Najwa tace to amma zata aje jaka ta dawo, sai ta fita ta shiga É—akin Amrah ta aje jakarta ta cire hijab ta dawo ta amsa aikin, Sameeha ta tafi É—aki ta barsu, Najwa ta kalli Ikram tana murmushi.
Bakuwa Anty tayi ne?
A'a Jamila ai 'yar aiki ce da su yaya Hauwa suka kawota.
Ashe har ta zo, 'yan mata sannunki.
Yauwa Jamila ta bata amsa a takaice, kiran daya shigo wayar Ikram ce yasa ta miƙe ta fita daga kitchen ɗin, a lokacin dabara ta faɗowa Najwa tace cikin jan Jamila da hira.
Sun barki kin É—anÉ—ana kazar kuwa?
Sun bani amma kin san kaza bata isata tunda gida babu maƙota sai ɗai ɗai.
Ɗauko ledan can ki ɗiba iya yadda kike so kije ɗakinki ki ɓoye kici abinki hankali kwance, nima kinga zan ɗiba kasona kafin su zo dan nasan halin Anty akwai rowar tsiya.
Jikin jamila yana rawa ta ɗauki baƙar leda ta ɗiba kazar iya son ranta ta fita da sauri ta shiga ɗakinta ta ɓoye kana ta dawo tana washe baki cike da mugun farin ciki.
Amma ke 'yar uwar mai gidan ce ko? Dan na kula danginsa basa shiri da anty.
Hmmm ni ƙanwarta ce amma babanta shine yayan mamana, sai dai ni ina zuwa ne saboda takurani da inna tayi, dan sam Anty Sameeha ba tada kirki.
Ai naga alama dan tunda na zo gidan nan take zuba mini dokoki ga shegen saka mini ido, abu kaɗan nayi suke kyarata ita da ƙanwarta, gaskiya naga ke kina da kirki ba halinku ɗaya ba.
Hmmm sai ma gobe zaki ga yadda zata yiwa 'yan uwan mijinta, sam basa jin daÉ—inta ni har tausayinsu nake.
Cewar Najwa tana taɓe baki, a zuciyarta kuma tana jin wani daɗi da farin ciki dan ta samu Jamila zata fara aika sakonta gurin su Hauwa, saboda ta san sun turota ne wu riƙa samun labarai a gurinta, kuma ga dukkan Alamu Jamila zata yi mata matuƙar amfani a cikin rawar da zata taka a gidan, muryar Jamila taji tana cewa a hankali dan kar ajita.
Kin san Allah na tsani matar nan addu'a nake Allah yasa Alhaji ya saketa ya auro mai mutunci.
Hmmm da nine 'yan uwansa sai na saka sun yi mata kishiya.
Cewar Najwa itama a hankali, Jamila ta saka dariya tana cewa.
Wlh kuwa da nayi murna naga ƙarshen ɗaga kai.
Jamila sunanki ko?
Eh.
Ina so za ki yi mini wani abu wanda zan biyaki da kuɗi mai tsoka amma ina so ya zama sirri a tsakaninmu, idan kika faɗawa wani wlh sai na saka an ɓatar dake dan mijin da zan aura soja ne kina yi mini ba daidai ba zan saka ya harbeki da bindigarsa.
Wlh zanyi miki kome kika so in dai zaki biya ni, amma dan Allah karki saka a harbeni.
Jamila ta faÉ—a tana zare ido, Najwa ta saka dariya tana cewa.
Ke wasa nake miki naga duk kin firgita ne, kawai dai zolayarki nayi, amma naga tamu ta zo ɗaya bani number ɗinki ko gaisawa mu riƙa yi.
Sai a lokacin Jamila ta samu kwanciyar hankali ta saki murmushi tana ce mata wayarta tana ɗaki anjima zata bata, Najwa tace to suka cigaba da aiki, sai dai ita Najwa da abinda take saƙawa a cikin zuciyarta, haka nan taji ta gwada Jamila dan ta hasko ƙila nan gaba tayi mata amfani, kuma ta kula yarinyar akwai wayo da son kuɗi, ta tabbatar da hakane su Hauwa suka yi amfani suka ja ra'ayinta ta zo aiki gidan, itama zata yi amfani da wannan damar wajen samun cikar burinta.
[7/7, 13:04] BuhainatðŸ˜: *ABIN DA CIWO*
Na
©Rahma Kabir MrsMG.
Wattpad @rahmakabir
Page 7.
Ikram da ta dawo kitchen ɗin ta cewa Jamila taje ta gyara falo inji Anty Sameeha saboda gobe ba za shi sharaba sai zuwa yamma in baƙi sun tafi, Jamila ta miƙe ta fita Ikram ta zauna suka cigaba da aikin suna hira da Najwa, har suka gama suka a dana komai kafin suka fito Jamila ta soma gyaransa. Suna zaune a falo sai ga Anty Sameeha ta fito cikin doguwar rigar material da hula akanta, ta zauna a cushing tana cewa.
Ikram yanzu na gama waya da Aminu yace in kulle ɗakina dana rana kar na bari a shiga ayi mana barna, dama bana gaya miki haka zanyi ba to shima yanzu ya gama faɗa mini, dan haka ku shirya da wuri ku ɗauki duk abinda kuke buƙata ku kai shi ɗakin Jamila dan a can zamu tare, shima key ɗinsa yana hannunna koda zaku ɗauki abu sai ku faɗa mini.
Gaskiya gwara ayi haka dan bamu san mutanen da zamu zo ba Anty, tunda wannan ne karo na farkon taro da za kiyi a gidan, sannan ma a farfajiya za ayi walimar.
Cewar Ikram Sameeha tace.
Sosai ma ni da ban san ya halinsu yake ba gwara in yi wa abin tufkar hanci a rabu lafiya da kowa, ni wlh na ƙosa ma ayi a gama na huta.
Ai Anty kunyi ƙoƙari a wannan marra da muke ciki zaku yi shagali ba biki ba suna ba, kawai dan kun dawo kaduna ne fa.
To Najwa Aminu yace za a yi haka shiyasa nima na mara masa baya, gwara ayi É—in a sada zumunci dan da yawan 'yan uwansu ma ban sansu ba.
Cewar Sameeha sai ta cigaba da yi musu bayanin yadda take so su saka mata ido a gidan dan ita ba lallai ta samu damar yin haka ba saboda tarban mutane. Sai da aka kira sallamar magrib kafin suka miƙe kowa wanne ya nufi ɗaki domin yin salla. Jamila tana ɗakinta zaune tana huta gajiyar aiki data kwasa, sai kira ya shigo wayarta ta duba taga Hauwa ce sai ta mike ta zo ta rufe ƙofarta da key ta ciki ta koma ta zauna a bakin gado ta ɗauki wayar da sauri dan ta kusa tsinkewa.
Jamila meke wakana a gidan?
Jamila ta shiga karanto mata shirye shiryensu tana cewa.
Hajiya ai wlh na ci nama sosai wata 'yar uwar Anty Sameeha ta ce na ɗiba na ɓoye saboda tasan anty da baƙar rowa, itama sai zaginta take da alama 'yan uwanta suma basa jin daɗinta.
Hmmm ba mamaki suma ba mutunta su take yi ba, In Sha Allah da wuri ma zan zo gidan.