Sashe 60
Abin Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Muryan Sameeha kenan data yi magana cikin damuwa, Najwa kashe wayarta tayi ta aje ta a kan gado tana jin wani baƙin ciki yana ruruwa a zuciyarta, wannan shine karo na farko data haɗa plan ya rushe bata kawo Shamsu daɗin baki yayi mata ba, aiko yaci bashi dan ta ɗauki alwakarin yin maganinsa sai ya san wacce yaci amana, haka ta miƙe ta manna bayanta a bango tana huci zuciyarta tana tafarfasa, dakar ta tausa kanta ta koma ta kwanta tana sauke ajiyar zuciya, yanzu kenan yasa taji kunya a idon su Sameeha, da wani ido ma zata kallesu? tana ganin ba zata sake taka ƙafarta ba zuwa inda suke dan abin da kunya, ba zata yarda ma inna ta san da wannan abin da tayi ba saboda tasan zasu kwashi rikici, addu'a take Allah yasa su rufa mata asiri su bar maganar a haka.
Su Sameeha kam Ibrahim sosai ya yi musu nasiha yace kuma su bar zancen a tsakaninsu dan kar wasu suji suyi dariya tunda naka naka ne komin lalacewa Najwa jininsu ce, dan haka su barta da halinta kuma su rufe maganar kar ma su nuna mata ko a fuska, daga bisani suka yi sallama da juna wajen ƙarfe sha ɗaya da minti sha shida suka fito Ikram da Shamsu har mota suka rakasu kana suka wuce, sai suka dawo ciki Ikram sai ɓoye fuska take yi cike da jin kunyar abinda tayi wa Shamsu, da taji maganar Sameeha da bata riski kanta a haka ba, shiko Shamsu nuna wa yayi ko kaɗan bai damu ba kuma komai ya wuce.
Duk da wannan abin ya faru bai hana gidaje biyu amare da angwaye sun more amarcinsu ba, dan kuwa ko wanne ya baza komar soyayyar sa ya kwashi roman so da ƙauna. Washe gari ne da yamma aka shirya kayataccen walima a cikin farfajiyar gidan Hajiya nan second gate, 'yan gidansu Ikram ma sun zo dan dama wasu sai a ranar ne suka samu damar zuwa ganin ɗakin amare, Ikram ma Shamsu ya kawota ta sauka a sashin Sameeha sai da lokacin walima yayi kafin suka tattara zuwa sashin hajiya, kota wani ɓangare soyayya ake nuna musu Masha Allah abun dai sai wanda ya gani, sun san sunyi dace da dangin miji saura musu kyautatawa da kuma kama mazajensu hannu bibbiyu. Duk waɗanda suka zo wannan walimar sai da suka tafi da kyautar zanin atamfa da kuma kayan ciye ciye, ga wa'azin da aka gabatar ya kayatar wanda mutane sun tafi da malama Haajara a baki saboda iya sarrafa harshe da kuma ilimin zaman aure da ta baje musu suka kwashi garaɓasa. Bayan sallar magrib kowa ya watse gida ya rage sai dangi na jiki, Ikram a sashin Sameeha ta zauna, sosai Sameeha ta kuma yi mata faɗa akan abinda ta yiwa Shamsu jiya, ta kuma nusar da ita yadda ake zaman rayuwa sosai, domin ita tana da wayewa da sani akan zaman aure dan jiya ba yau ba ne, Ikram ta yi mata godiya ta ɗaura da cewa.
Nayi mamakin abinda Najwa ta aika jiya hakan yana nuna tana bakin ciki da aurena, kin ga kenan ashe bada zuciya É—aya ta shigo jikinmu ba aketa hidimar biki da ita tunda kinga yauma bata zo ba sai Inna, wai harda cewa inna ta faÉ—a mana ba tada lafiya ne, banda kunce a rufe maganar da sai na faÉ—awa Inna abinda ta mini.
Ikram ki bar komai ya wuce kin fita har a gurin Allah, sannan ki cire damuwarki akanka ki fuskanci aurenki, idan ta zo ta nima sulhu shikenan mu cigaba da zumuncinmu tunda son zuciya ya sa tayi haka, kuma ma da kunya tace zata ƙara aikata aikin rashin gaskiya a garemu.
Anty wlh yadda na karanci Najwa sam baki gane halinta ba, na tabbatar ba zata sake zuwa inda muke ba tana da riƙo sannan kuma baƙin cikin nasarar da muka samu bazai barta ta cigaba da zumunci damu ba, ni kam ko ta dawo bazan sakar mata fuska ba dan nasan ta da mugun son zuciya.
Ni dai nace ki bar wannan maganar kuma ga sakonki nan Khairy ta ce na baki tsumi ne da kuma gumba da kayan ciye ciye dai na mata, ki riƙa amfani dasu a hankali, in kuma baki gane ba ki kirani nayi miki bayani.
Hmmm Anty khairy bata gajiya, ni dai wlh bazan sha wani abu yanzu ba dan hmmm.
Sai tayi shuru tana sunne kai, Sameeha ta yi murmushi tana cewa.
Yarinya da haka zaki saba Allah dai ya kawo 'yan dugui dugui masu albarka dan ke yanzu zaki fara aje garke nikam ba yanzu ba.
Allah anty ina fatan ki haifa mana twins, nasan yaya Ibrahim sai yayi yayyafin kuÉ—i ga mutane dan murna.
Ki fara faÉ—a a akanki kafin ni dan ina da Abi da Amrah.
Sameeha ta faɗa tana miƙewa zata ɗauko wayarta a chrgy, Ikram tayi murmushi.
Su can gidansu daban nan gidan kuma suma nasu zaki haifo musu.
Ikram yaushe muka fara irin wannan maganar dake, wato aure daÉ—i ko.
Laaa anty ni kin ma koreni, bari naje falo na jira yazo mu tafi.
Kima kirashi yazo ya É—auke ki kawai kin ji.
Cewar Sameeha tana dariya Ikram ma dariyar tayi ta fice zuwa falo. Sai wajen tara da rabi Shamsu yazo ya É—auketa suka wuce gida cike da farin ciki.
***"
Aminu.
Tunda ya tabbatar da an ɗaura auren Sameeha da wani ya kulle kansa a ɗaki da yake weekend ne ba aiki, yaci kukansa ya gode Allah daga bisani yayi mata addu'ar fatan alkhairi yasan ya rasata har abada dan abune mai matuƙar wahala ta fito daga gidan mijinta, saboda yadda yasan ta da iya kula da miji, haka ya yini yata tunanin rayuwarsu ta baya, ko yaransa a ranar sun san babansu yana cikin damuwa shiyasa basu takura shi ba da yake basu san mamansu tayi wani aure ba, baaba ce kawai ta sani itace ma ta dinga kwantarwa Aminu da hankali. Wajen misalin ƙarfe tara na dare yana zaune yana kallon tv, rabin tunaninsa yana ga Najwa da duk ranar basu yi waya ba wanda in bai kirata ba zata kirashi, sai ya bayar ko kila wani uzurin ne ya riƙe ta, yana cikin tunanin ya kirata sai wayarsa ta soma kuka ya duba yaga baƙuwar number ne, kamar ba zai ɗaga ba sai ya ɗauka ya kara a kunnensa yana sallama, ɗaya ɓangaren kuma Nafeesa ta amsa cike da natsuwa ta gaishe shi ya amsa yana tambayar wacece, sai da ta gyara kwanciyarta ta daidaita natsuwarta kafin ta amsa da cewa.
Sunana Nafeesa Sabo Mai kanti, na siya waya ce second hand a hannun wani mai sayar da waya sai na tsinci number ɗinka a cikin wayar, dalilin daya saka na kiraka saboda sunanka ya kasance sunan fiyayyen Halitta ni kuma duk abinda ya danganci Manzon Allah s.a.w yana matuƙar burgeni. Allah yasa ban takuraka ba.
Ta ƙare maganar tana jan fasali, Aminu kuwa yadda ta jero masa bayani ta kuma sako fiyayyen Halitta s.a.w sai hakan yayi matuƙar kayatar dashi, ya ƙara riƙe wayar yana cewa.
Masha Allah kuma baki takurani ba sai dai nayi mamakin ƙarfin halinki na kiran wanda baki sani ba.
Hakane amma na tabbatar Aminullah ba mai cutarwa bane domin suna linzami ne.
Gaskiya ne ina godiya na yaba halina duk da baki waye ni ba. Nagode.
Nice da godiya daka saurareni amma in ba damuwa zan iya cigaba da kiranka muna gaisawa saboda soyayyar Manzon Allah s.a.w .
Tunda kika ce Manzon Allah s.a.w ai kin gama magana, kuma masoyina ne da babu tamkarsa a duk duniya, ina kuma son mu'amala da duk wanda yake ƙaunar Rasulillahi.
Nagode sosai a gaida iyalin, zan barka haka karna cikaka da surutu. Idan kana yin WhatsApp chart zamu riƙa gaisawa ta can dan ba kowa ne ke son amsa waya ba.
Ayya? ni chart bai dameni ba amma gaisawan ma ba damuwa nagode.
Nima na gode sai da Safe yaya Aminullah.
Bata jira amsar sa ba ta kashe wayar tana sakin murmushin farin ciki, shima Aminu tsintar kansa yayi yana yin murmushi dan sosai yaji ta rage masa damuwar da yake ciki saboda tsara zancenta, tunatar dashi da tayi akan soyayyar Manzon Allah s.a.w, sai nan take ya soma yi masa salati saboda yasan yin salati ga Annabi s.a.w waraka ce daga damuwa, mafita ce daga ruÉ—ani, sannan kuma kuma samar da farin ciki da natsuwar ruhi.
Muje zuwa....
[7/7, 13:04] BuhainatðŸ˜: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*
39.
Aminu a daren saida ya rayashi da sallolin nafila ya mayar da lamarinsa ga Allah, kafin daga bisani ya samu barci mai daɗi sosai, haka ya wayi gari wasai ba tare da sauran damuwa ba, hakika ya ƙara tabbatar da duk wanda ya bar Allah to shima sai ya barshi, da tun farko ya mayar da lamarinsa ga Allah to ba zai tsinci kansa a damuwa da auren Sameeha ba. Bayan ya kammala karyawa sai ya tuna da Najwa hakan yasa shi kiranta, wayar harta tsinke bata ɗauka ba a kira na biyu ne ta dauka bayan sun gaisa yake tambayarta lafiyarta tace tana fama da ciwon kai shine yasa ma jiya bata kira ba, yayi mata fatan samun lafiya kana suka ɗan taba hira daga bisani suka yi sallama akan zai kara kira anjima yaji jikinta, yana ƙoƙarin miƙewa saƙo ya shigo wayarsa ya duba yaga number jiya ce da ko saving bai yi ba, ya duba saƙon tana cewa.
Barka da safiya mai babban suna fatan ka tashi lafiya ya kwanan iyali? Na duba ka a WhatsApp sai naga baka hau ba shiyasa na gaisheka ta nan, ka yini lafiya.
Guntun murmushi yayi yana cewa a fili.
Su Sameeha kam Ibrahim sosai ya yi musu nasiha yace kuma su bar zancen a tsakaninsu dan kar wasu suji suyi dariya tunda naka naka ne komin lalacewa Najwa jininsu ce, dan haka su barta da halinta kuma su rufe maganar kar ma su nuna mata ko a fuska, daga bisani suka yi sallama da juna wajen ƙarfe sha ɗaya da minti sha shida suka fito Ikram da Shamsu har mota suka rakasu kana suka wuce, sai suka dawo ciki Ikram sai ɓoye fuska take yi cike da jin kunyar abinda tayi wa Shamsu, da taji maganar Sameeha da bata riski kanta a haka ba, shiko Shamsu nuna wa yayi ko kaɗan bai damu ba kuma komai ya wuce.
Duk da wannan abin ya faru bai hana gidaje biyu amare da angwaye sun more amarcinsu ba, dan kuwa ko wanne ya baza komar soyayyar sa ya kwashi roman so da ƙauna. Washe gari ne da yamma aka shirya kayataccen walima a cikin farfajiyar gidan Hajiya nan second gate, 'yan gidansu Ikram ma sun zo dan dama wasu sai a ranar ne suka samu damar zuwa ganin ɗakin amare, Ikram ma Shamsu ya kawota ta sauka a sashin Sameeha sai da lokacin walima yayi kafin suka tattara zuwa sashin hajiya, kota wani ɓangare soyayya ake nuna musu Masha Allah abun dai sai wanda ya gani, sun san sunyi dace da dangin miji saura musu kyautatawa da kuma kama mazajensu hannu bibbiyu. Duk waɗanda suka zo wannan walimar sai da suka tafi da kyautar zanin atamfa da kuma kayan ciye ciye, ga wa'azin da aka gabatar ya kayatar wanda mutane sun tafi da malama Haajara a baki saboda iya sarrafa harshe da kuma ilimin zaman aure da ta baje musu suka kwashi garaɓasa. Bayan sallar magrib kowa ya watse gida ya rage sai dangi na jiki, Ikram a sashin Sameeha ta zauna, sosai Sameeha ta kuma yi mata faɗa akan abinda ta yiwa Shamsu jiya, ta kuma nusar da ita yadda ake zaman rayuwa sosai, domin ita tana da wayewa da sani akan zaman aure dan jiya ba yau ba ne, Ikram ta yi mata godiya ta ɗaura da cewa.
Nayi mamakin abinda Najwa ta aika jiya hakan yana nuna tana bakin ciki da aurena, kin ga kenan ashe bada zuciya É—aya ta shigo jikinmu ba aketa hidimar biki da ita tunda kinga yauma bata zo ba sai Inna, wai harda cewa inna ta faÉ—a mana ba tada lafiya ne, banda kunce a rufe maganar da sai na faÉ—awa Inna abinda ta mini.
Ikram ki bar komai ya wuce kin fita har a gurin Allah, sannan ki cire damuwarki akanka ki fuskanci aurenki, idan ta zo ta nima sulhu shikenan mu cigaba da zumuncinmu tunda son zuciya ya sa tayi haka, kuma ma da kunya tace zata ƙara aikata aikin rashin gaskiya a garemu.
Anty wlh yadda na karanci Najwa sam baki gane halinta ba, na tabbatar ba zata sake zuwa inda muke ba tana da riƙo sannan kuma baƙin cikin nasarar da muka samu bazai barta ta cigaba da zumunci damu ba, ni kam ko ta dawo bazan sakar mata fuska ba dan nasan ta da mugun son zuciya.
Ni dai nace ki bar wannan maganar kuma ga sakonki nan Khairy ta ce na baki tsumi ne da kuma gumba da kayan ciye ciye dai na mata, ki riƙa amfani dasu a hankali, in kuma baki gane ba ki kirani nayi miki bayani.
Hmmm Anty khairy bata gajiya, ni dai wlh bazan sha wani abu yanzu ba dan hmmm.
Sai tayi shuru tana sunne kai, Sameeha ta yi murmushi tana cewa.
Yarinya da haka zaki saba Allah dai ya kawo 'yan dugui dugui masu albarka dan ke yanzu zaki fara aje garke nikam ba yanzu ba.
Allah anty ina fatan ki haifa mana twins, nasan yaya Ibrahim sai yayi yayyafin kuÉ—i ga mutane dan murna.
Ki fara faÉ—a a akanki kafin ni dan ina da Abi da Amrah.
Sameeha ta faɗa tana miƙewa zata ɗauko wayarta a chrgy, Ikram tayi murmushi.
Su can gidansu daban nan gidan kuma suma nasu zaki haifo musu.
Ikram yaushe muka fara irin wannan maganar dake, wato aure daÉ—i ko.
Laaa anty ni kin ma koreni, bari naje falo na jira yazo mu tafi.
Kima kirashi yazo ya É—auke ki kawai kin ji.
Cewar Sameeha tana dariya Ikram ma dariyar tayi ta fice zuwa falo. Sai wajen tara da rabi Shamsu yazo ya É—auketa suka wuce gida cike da farin ciki.
***"
Aminu.
Tunda ya tabbatar da an ɗaura auren Sameeha da wani ya kulle kansa a ɗaki da yake weekend ne ba aiki, yaci kukansa ya gode Allah daga bisani yayi mata addu'ar fatan alkhairi yasan ya rasata har abada dan abune mai matuƙar wahala ta fito daga gidan mijinta, saboda yadda yasan ta da iya kula da miji, haka ya yini yata tunanin rayuwarsu ta baya, ko yaransa a ranar sun san babansu yana cikin damuwa shiyasa basu takura shi ba da yake basu san mamansu tayi wani aure ba, baaba ce kawai ta sani itace ma ta dinga kwantarwa Aminu da hankali. Wajen misalin ƙarfe tara na dare yana zaune yana kallon tv, rabin tunaninsa yana ga Najwa da duk ranar basu yi waya ba wanda in bai kirata ba zata kirashi, sai ya bayar ko kila wani uzurin ne ya riƙe ta, yana cikin tunanin ya kirata sai wayarsa ta soma kuka ya duba yaga baƙuwar number ne, kamar ba zai ɗaga ba sai ya ɗauka ya kara a kunnensa yana sallama, ɗaya ɓangaren kuma Nafeesa ta amsa cike da natsuwa ta gaishe shi ya amsa yana tambayar wacece, sai da ta gyara kwanciyarta ta daidaita natsuwarta kafin ta amsa da cewa.
Sunana Nafeesa Sabo Mai kanti, na siya waya ce second hand a hannun wani mai sayar da waya sai na tsinci number ɗinka a cikin wayar, dalilin daya saka na kiraka saboda sunanka ya kasance sunan fiyayyen Halitta ni kuma duk abinda ya danganci Manzon Allah s.a.w yana matuƙar burgeni. Allah yasa ban takuraka ba.
Ta ƙare maganar tana jan fasali, Aminu kuwa yadda ta jero masa bayani ta kuma sako fiyayyen Halitta s.a.w sai hakan yayi matuƙar kayatar dashi, ya ƙara riƙe wayar yana cewa.
Masha Allah kuma baki takurani ba sai dai nayi mamakin ƙarfin halinki na kiran wanda baki sani ba.
Hakane amma na tabbatar Aminullah ba mai cutarwa bane domin suna linzami ne.
Gaskiya ne ina godiya na yaba halina duk da baki waye ni ba. Nagode.
Nice da godiya daka saurareni amma in ba damuwa zan iya cigaba da kiranka muna gaisawa saboda soyayyar Manzon Allah s.a.w .
Tunda kika ce Manzon Allah s.a.w ai kin gama magana, kuma masoyina ne da babu tamkarsa a duk duniya, ina kuma son mu'amala da duk wanda yake ƙaunar Rasulillahi.
Nagode sosai a gaida iyalin, zan barka haka karna cikaka da surutu. Idan kana yin WhatsApp chart zamu riƙa gaisawa ta can dan ba kowa ne ke son amsa waya ba.
Ayya? ni chart bai dameni ba amma gaisawan ma ba damuwa nagode.
Nima na gode sai da Safe yaya Aminullah.
Bata jira amsar sa ba ta kashe wayar tana sakin murmushin farin ciki, shima Aminu tsintar kansa yayi yana yin murmushi dan sosai yaji ta rage masa damuwar da yake ciki saboda tsara zancenta, tunatar dashi da tayi akan soyayyar Manzon Allah s.a.w, sai nan take ya soma yi masa salati saboda yasan yin salati ga Annabi s.a.w waraka ce daga damuwa, mafita ce daga ruÉ—ani, sannan kuma kuma samar da farin ciki da natsuwar ruhi.
Muje zuwa....
[7/7, 13:04] BuhainatðŸ˜: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*
39.
Aminu a daren saida ya rayashi da sallolin nafila ya mayar da lamarinsa ga Allah, kafin daga bisani ya samu barci mai daɗi sosai, haka ya wayi gari wasai ba tare da sauran damuwa ba, hakika ya ƙara tabbatar da duk wanda ya bar Allah to shima sai ya barshi, da tun farko ya mayar da lamarinsa ga Allah to ba zai tsinci kansa a damuwa da auren Sameeha ba. Bayan ya kammala karyawa sai ya tuna da Najwa hakan yasa shi kiranta, wayar harta tsinke bata ɗauka ba a kira na biyu ne ta dauka bayan sun gaisa yake tambayarta lafiyarta tace tana fama da ciwon kai shine yasa ma jiya bata kira ba, yayi mata fatan samun lafiya kana suka ɗan taba hira daga bisani suka yi sallama akan zai kara kira anjima yaji jikinta, yana ƙoƙarin miƙewa saƙo ya shigo wayarsa ya duba yaga number jiya ce da ko saving bai yi ba, ya duba saƙon tana cewa.
Barka da safiya mai babban suna fatan ka tashi lafiya ya kwanan iyali? Na duba ka a WhatsApp sai naga baka hau ba shiyasa na gaisheka ta nan, ka yini lafiya.
Guntun murmushi yayi yana cewa a fili.