Sashe 77
Abin Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hmmmm Allah ya kyauta, kuma dole mu bar maganar, sannan Taju ina so Ka yiwa malam Sadi mai yiwa yara karatun islamiyar nan gidan magana ko zai iya aurenta, bana so ka rufe masa matsalarta ka sanar da shi in ya amince sati mai zuwa za a ɗaura aurensu, zan bashi gida kyauta da zasu zauna da ita ke kuma daga yau karna sake ganin ƙafarki koda a tsakar gida ne, sannan Hajiya ki amsa wayarta ki kawo mini. Batun Binafa kuma Taju kaje ka sanar da iyayenta.
Alhaji yana gama faɗar haka ya miƙe ya bar sashin, Nafeesa ta ƙara rushewa da kuka akan haɗin da za ayi mata da Sadi, duk da ba mummuna bane amma bayi da komai talaka ne futuk, kuma babban ci baya ne a auransa ita da take da wayewa da ilimin zamani. Tsawan da Taju ya daka mata yasa tayi shiru ya cigaba da dura mata zagi yana cewa.
Hukuncin Abbansu shine dai dai, haka ya fice daga falon rai a ɓace, Hajiyarsu ta miƙe ta kamota ta zaunar a cushing ta shiga rarrashinta tana cewa.
Dama ki daina wannan kukan kiyi fatan Sadi ya amince da aurenki domin kuwa auren nan shine kaɗai rufin asirinmu, jin daɗi da gata yasa kika saka mana da mummunar tabo amma dai dai gwargwado ina kula da tarbiyyarku, kiyi haƙuri ki barwa Allah zaɓinsa yasa hakan ya zama miki alkhairi, kuma In Sha Allah za ayi miki biki na gata kamar yadda akewa kowa kinji.
Nafeesa ta ɗaura kanta a kan cinyar momynsu tana yin marayan kuka jikinta har ciccira yake yi, dana sani sosai ya wanke zuciyarta wanda take jin dama ana mayar da hannun agogo baya tabbas da ta gyara kuskuran data aikata, tana jin dole ne ta nima yafiyar Sameeha wata ƙila ta samu sassauci daga halin ta taje ciki, dole ne ta saduda ta amsa ƙaddarar data kira da hannunta wanda tarin son zuciya ya kaita ya baro, fatanta Allah yasa Sadi ya yarda da aurenta, a yanzu ba tada zaɓi face zaɓin iyayenta da kuma karɓan ƙaddararta, wataƙila ta samu dacewa ta rabauta, sannan dama ba tada mashinshini ko wanda tasan zai aureta a yanzu, sai ta kara sakin kuka mai tsuna zuciya, ta tuna da Aminu da kuma Najwa tasan itama ko bajima ko ba daɗe dole asiri zai tonu, zata bar Aminu bari na har abada dan ta kama dahir, sannan zata yi ƙoƙarin sanar da Najwa gaskiya ko ƙila zata hankalta ta kama aurenta da kyau, Momyn ta cigaba da buga bayanta ita kuma kukan nadama take fiyarta gwanin tausayi.
[7/7, 13:04] BuhainatðŸ˜: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*
48.
Nafeesa sai da zazzaɓi mai zafi ya rufeta saboda kukan data yi, da kyar momynsu ta lallaɓata ta kaita ɗaki ta samu barci, sai ta fito ta cigaba da ayyukanta. Taju daya fita yayan Binafa ya kira a waya ya tambaye shi ko yana gida, sai yace yana nan a haka suka aje wayar ya ɗauki motarsa zuwa gidan. Daya isa part ɗin mazan gidan ya wuce ya same shi a ɗakinsa wato falo, yana ganinsa ya miƙe cikin fara'a ya miƙa masa hannu suka gaisa kana suka zauna a cushing, Taju yace cikin zolaya.
Maza ya kamata a barwa su Auwal gidan nan ka koma naka gidan, ayi mutum yaƙi aure yana niman tsufa a gida.
Haba dame kwaÉ—o yafi gaya ai kaima ba jimawa kayi da auren ba, wato ka ji daÉ—insa zaka fara yi mini gori, to bama wannan ba nasan duk in ka nimeni da akwai magana, meye labari?.
Hmmm Nafeesa da Binafa ne suka nima chager mini kai yaran nan ƙiri ƙiri suna niman ɓata sunan zuri'armu.
Me suka yi? Amma nayi mamaki daka ce har da Nafeesa dan ita tana da natsuwa da hankali ba irin Binafa da kullun cikin saka mu magana take yi ba.
Nan Taju ya gyara zama ya ciro wayarsa ya buɗe WhatsApp ya bashi saƙon da aka tura masa, Hassan ya amsa ya karanta, koda ya gama mamaki ne ya maye fuskarsa Taju ya ƙara da bashi labarin abinda Hamisu yayi masa daya kirashi, sosai ran Hassan ya ɓaci ya miƙe cikin zafin nama yana cewa.
Haba dama biri yayi kama da mutum, shegiyar yarinya kullun sai ta fita ko ta jawo mana ƙawaye su zo gidan nan, ashe iskancinta take yi son ranta wlh idan na gamu da Binafa rai kaɗan zan bar mata.
Yana gama faÉ—ar haka ya isa gurin daya saka chargy wayarsa ya É—auka sai ya dawo ya zauna ya shiga kiran layin Binafa, har sai da ya tsinke ba a É—auka ba ya kuma kira sai aka dauka yadda yaji murnar namiji ne sai ya dannw zagin daya yi niyyar dura mata, yace a dakile.
Malam ina me wayar?
Kana magana da Sagent Lawal mai wayar kuma mun kama tana nan police station bisa laifin FyaÉ—e da suka yiwa wata yarinya suka lalatata, to dama mun so ta faÉ—a mana wanda zamu kira a 'yan uwanta amma tace bata da kowa tana so mu bada belinta amma hakan ba zai yuwu ba.
Ok wane police station ne?
Nan ɗan sandan ya sanar da shi, Hassan yace gashi nan zuwa sai ya kashe wayar yana duban Taju tare da bashi labarin a taƙaice, Taju ya miƙe yana cewa.
Zama bai ganmu ba wato dai maganar da Hamisu ya faÉ—a ta tabbata, Allah ya shirya.
Hassan bai iya cewa komai ba saboda takaici sai ya miƙe suka fita tare, a motar Taju suka je police station ɗin wanda sagent ɗin da ya ɗauki wayar shine ya turasu gurin DPO ya gabatar dasu, bayan sun gaisa DPO yace.
Wlh munyi munyi su faɗa mana wani nasu amma sunƙi, iyayen yarinyar da suka yiwa Fyaɗe sun ce ba zasu haƙura ba sai anje kotu, a takaice tun wata guda daya wuce suka yaudari yarinyar suna kaita gidan Hanan a nan suka ɓata ta, yarinya 'yar shekara sha shida kuma ba sau ɗaya suka yi mata ba yafi sau biyar, mahaifiyar yarinyar ne ta kamata a ɗaki tana saka brush a gabanta shine data duketa matsa mata take faɗa mata yadda aka yi ta zama haka, to a nan gidan Hanan muka kamo su yanzu haka muna son ranar monday zamu miƙa maganar kotu tunda basu yi gardamar laifinsu ba, sai dai sun nima su bamu cin hanci dan mu rufe maganar hakan kuma ya ƙara laifinsu.
Ni sunana Hassan wannan kuma Taju mu yayyin Binafa ne dan haka ina so ku cigaba da riƙe su har sai an shiga kotu an yanke musu hukunci, kamar yadda taƙi faɗar kowa nata ina so koda danginmu sun zo nimansu ku nuna basa nan, dan Allah ina son wannan ya zama sirri karku nuna mata mun zo ma, zan tafi da wayarta ta yadda ko ta bukaci yin magana da wani ba zata samu ba ku nuna mata babu dama.
Haba Hassan ya zaka ce haka bai kamata in ta aikata laifi mu rufe maganar ga iyayenmu ba.
Cewar Taju, Hassan ya saki guntun murmushin takaici yace.
Ina so wannan ya zama babban darasi a garesu, kasan halin Binafa ba tada natsuwa ga taurin kai, ta jima tana aikata ɓarna ina son wannan ya zama hanyar shiriya a garesu, Allah yasa a kaisu gidan yari ma. DPO dan Allah kayi abinda nace maka dan wlh wannan shine kadai hanyar da zaisa Binafa ta shiga hankalinta.
Karka damu zamu yi aikin daya kamata dan ba zamu taɓa yarda a danne zalunci akan gaskiya ba.
Nan suka yi masa sallama ya basu wayar Binafa suka wuce. A mota Taju take cewa.
Anya hakan bazai sa sunan zuri'armu ya ɓaci ba? bana so maganar nan taje kotu.
Wlh sai taje fa, Taju kai dai ka saka ido kawai, ai su Dady sune suka ɗaure mata gindin yin komai dan haka bana tsoron duk abinda zai faru ta yadda kowa zai gane kuransa, kuma babu sunanmu da zai ɓaci nata ne dai zai ɓaci wlh.
Haka suka dinga tattauna maganar Hassan ya roƙi Taju akan karya sanar da kowa maganar har sai anje kotu kafin maganar ta fita, ta hakane za a samu daidaiton tarbiyya dan abin yayi muni da yawa. Haka Taju ya sauke shi a gida sai ya wuce abinsa, ko shi yaji daɗin abinda Hassan yayi kawai baya son ya nuna rashin damuwarsa akai ne yasa yake ta bashi magana, amma hukuncin daya yanke shine daidai yana so Binafa ta gane kurenta ta yadda ba zata sake sha'awar wata mace ba a rayuwarta.
******
Hauwa.
Ta kasa fitowa waje saboda kunyar abinda Aminu yayi mata sai da aka yi sallar magriba kafin ta tattara yanata yanata ta koma gidanta tare da yaranta duka. Dama tun rana baƙi kowa ya kama kansa sai 'yan kauye da suka rage akan washe gari zasu wuce suma. Saboda naushin da Aminu ya yi mata sai da ya saka hakoranta na gaba yin girgiɗi alamar zasu faɗi, gashi ya sakar mata zazzaɓi sai da tasha maganin rage zugi kafin ta samu barci a ranar. Adama kuwa baƙin ciki goma da ashirin ga saki ga kuma wulaƙancin da Aminu ya yiwa mamanta ga kuma lalacewar aurensa da Najwa wanda a dalilin auren itama ta rasa nata auren, tun tana yin kukan fili har sai da ta koma yin na zuci, dan hakanan take jera ajiyar zuciya wanda ya saukar mata da ciwon kai mai tsanani da alama jininta ya hau, da kyar ta samu barci.
Washe gari Hauwa ta tashi saman dashishinta ya kumbura daga sama, sun tabbata fita zasu yi dan sosai suke yi mata ciwo, da kyar ma ta iya karyawa, bini bini take jan tsaki ta ƙumdumawa Aminu ashar, a haka Laure ta shigo gidan domin ta ƙara dubata da kuma jaje. Bayan sun gaisa Hauwa take cewa.
Alhaji yana gama faɗar haka ya miƙe ya bar sashin, Nafeesa ta ƙara rushewa da kuka akan haɗin da za ayi mata da Sadi, duk da ba mummuna bane amma bayi da komai talaka ne futuk, kuma babban ci baya ne a auransa ita da take da wayewa da ilimin zamani. Tsawan da Taju ya daka mata yasa tayi shiru ya cigaba da dura mata zagi yana cewa.
Hukuncin Abbansu shine dai dai, haka ya fice daga falon rai a ɓace, Hajiyarsu ta miƙe ta kamota ta zaunar a cushing ta shiga rarrashinta tana cewa.
Dama ki daina wannan kukan kiyi fatan Sadi ya amince da aurenki domin kuwa auren nan shine kaɗai rufin asirinmu, jin daɗi da gata yasa kika saka mana da mummunar tabo amma dai dai gwargwado ina kula da tarbiyyarku, kiyi haƙuri ki barwa Allah zaɓinsa yasa hakan ya zama miki alkhairi, kuma In Sha Allah za ayi miki biki na gata kamar yadda akewa kowa kinji.
Nafeesa ta ɗaura kanta a kan cinyar momynsu tana yin marayan kuka jikinta har ciccira yake yi, dana sani sosai ya wanke zuciyarta wanda take jin dama ana mayar da hannun agogo baya tabbas da ta gyara kuskuran data aikata, tana jin dole ne ta nima yafiyar Sameeha wata ƙila ta samu sassauci daga halin ta taje ciki, dole ne ta saduda ta amsa ƙaddarar data kira da hannunta wanda tarin son zuciya ya kaita ya baro, fatanta Allah yasa Sadi ya yarda da aurenta, a yanzu ba tada zaɓi face zaɓin iyayenta da kuma karɓan ƙaddararta, wataƙila ta samu dacewa ta rabauta, sannan dama ba tada mashinshini ko wanda tasan zai aureta a yanzu, sai ta kara sakin kuka mai tsuna zuciya, ta tuna da Aminu da kuma Najwa tasan itama ko bajima ko ba daɗe dole asiri zai tonu, zata bar Aminu bari na har abada dan ta kama dahir, sannan zata yi ƙoƙarin sanar da Najwa gaskiya ko ƙila zata hankalta ta kama aurenta da kyau, Momyn ta cigaba da buga bayanta ita kuma kukan nadama take fiyarta gwanin tausayi.
[7/7, 13:04] BuhainatðŸ˜: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*
48.
Nafeesa sai da zazzaɓi mai zafi ya rufeta saboda kukan data yi, da kyar momynsu ta lallaɓata ta kaita ɗaki ta samu barci, sai ta fito ta cigaba da ayyukanta. Taju daya fita yayan Binafa ya kira a waya ya tambaye shi ko yana gida, sai yace yana nan a haka suka aje wayar ya ɗauki motarsa zuwa gidan. Daya isa part ɗin mazan gidan ya wuce ya same shi a ɗakinsa wato falo, yana ganinsa ya miƙe cikin fara'a ya miƙa masa hannu suka gaisa kana suka zauna a cushing, Taju yace cikin zolaya.
Maza ya kamata a barwa su Auwal gidan nan ka koma naka gidan, ayi mutum yaƙi aure yana niman tsufa a gida.
Haba dame kwaÉ—o yafi gaya ai kaima ba jimawa kayi da auren ba, wato ka ji daÉ—insa zaka fara yi mini gori, to bama wannan ba nasan duk in ka nimeni da akwai magana, meye labari?.
Hmmm Nafeesa da Binafa ne suka nima chager mini kai yaran nan ƙiri ƙiri suna niman ɓata sunan zuri'armu.
Me suka yi? Amma nayi mamaki daka ce har da Nafeesa dan ita tana da natsuwa da hankali ba irin Binafa da kullun cikin saka mu magana take yi ba.
Nan Taju ya gyara zama ya ciro wayarsa ya buɗe WhatsApp ya bashi saƙon da aka tura masa, Hassan ya amsa ya karanta, koda ya gama mamaki ne ya maye fuskarsa Taju ya ƙara da bashi labarin abinda Hamisu yayi masa daya kirashi, sosai ran Hassan ya ɓaci ya miƙe cikin zafin nama yana cewa.
Haba dama biri yayi kama da mutum, shegiyar yarinya kullun sai ta fita ko ta jawo mana ƙawaye su zo gidan nan, ashe iskancinta take yi son ranta wlh idan na gamu da Binafa rai kaɗan zan bar mata.
Yana gama faÉ—ar haka ya isa gurin daya saka chargy wayarsa ya É—auka sai ya dawo ya zauna ya shiga kiran layin Binafa, har sai da ya tsinke ba a É—auka ba ya kuma kira sai aka dauka yadda yaji murnar namiji ne sai ya dannw zagin daya yi niyyar dura mata, yace a dakile.
Malam ina me wayar?
Kana magana da Sagent Lawal mai wayar kuma mun kama tana nan police station bisa laifin FyaÉ—e da suka yiwa wata yarinya suka lalatata, to dama mun so ta faÉ—a mana wanda zamu kira a 'yan uwanta amma tace bata da kowa tana so mu bada belinta amma hakan ba zai yuwu ba.
Ok wane police station ne?
Nan ɗan sandan ya sanar da shi, Hassan yace gashi nan zuwa sai ya kashe wayar yana duban Taju tare da bashi labarin a taƙaice, Taju ya miƙe yana cewa.
Zama bai ganmu ba wato dai maganar da Hamisu ya faÉ—a ta tabbata, Allah ya shirya.
Hassan bai iya cewa komai ba saboda takaici sai ya miƙe suka fita tare, a motar Taju suka je police station ɗin wanda sagent ɗin da ya ɗauki wayar shine ya turasu gurin DPO ya gabatar dasu, bayan sun gaisa DPO yace.
Wlh munyi munyi su faɗa mana wani nasu amma sunƙi, iyayen yarinyar da suka yiwa Fyaɗe sun ce ba zasu haƙura ba sai anje kotu, a takaice tun wata guda daya wuce suka yaudari yarinyar suna kaita gidan Hanan a nan suka ɓata ta, yarinya 'yar shekara sha shida kuma ba sau ɗaya suka yi mata ba yafi sau biyar, mahaifiyar yarinyar ne ta kamata a ɗaki tana saka brush a gabanta shine data duketa matsa mata take faɗa mata yadda aka yi ta zama haka, to a nan gidan Hanan muka kamo su yanzu haka muna son ranar monday zamu miƙa maganar kotu tunda basu yi gardamar laifinsu ba, sai dai sun nima su bamu cin hanci dan mu rufe maganar hakan kuma ya ƙara laifinsu.
Ni sunana Hassan wannan kuma Taju mu yayyin Binafa ne dan haka ina so ku cigaba da riƙe su har sai an shiga kotu an yanke musu hukunci, kamar yadda taƙi faɗar kowa nata ina so koda danginmu sun zo nimansu ku nuna basa nan, dan Allah ina son wannan ya zama sirri karku nuna mata mun zo ma, zan tafi da wayarta ta yadda ko ta bukaci yin magana da wani ba zata samu ba ku nuna mata babu dama.
Haba Hassan ya zaka ce haka bai kamata in ta aikata laifi mu rufe maganar ga iyayenmu ba.
Cewar Taju, Hassan ya saki guntun murmushin takaici yace.
Ina so wannan ya zama babban darasi a garesu, kasan halin Binafa ba tada natsuwa ga taurin kai, ta jima tana aikata ɓarna ina son wannan ya zama hanyar shiriya a garesu, Allah yasa a kaisu gidan yari ma. DPO dan Allah kayi abinda nace maka dan wlh wannan shine kadai hanyar da zaisa Binafa ta shiga hankalinta.
Karka damu zamu yi aikin daya kamata dan ba zamu taɓa yarda a danne zalunci akan gaskiya ba.
Nan suka yi masa sallama ya basu wayar Binafa suka wuce. A mota Taju take cewa.
Anya hakan bazai sa sunan zuri'armu ya ɓaci ba? bana so maganar nan taje kotu.
Wlh sai taje fa, Taju kai dai ka saka ido kawai, ai su Dady sune suka ɗaure mata gindin yin komai dan haka bana tsoron duk abinda zai faru ta yadda kowa zai gane kuransa, kuma babu sunanmu da zai ɓaci nata ne dai zai ɓaci wlh.
Haka suka dinga tattauna maganar Hassan ya roƙi Taju akan karya sanar da kowa maganar har sai anje kotu kafin maganar ta fita, ta hakane za a samu daidaiton tarbiyya dan abin yayi muni da yawa. Haka Taju ya sauke shi a gida sai ya wuce abinsa, ko shi yaji daɗin abinda Hassan yayi kawai baya son ya nuna rashin damuwarsa akai ne yasa yake ta bashi magana, amma hukuncin daya yanke shine daidai yana so Binafa ta gane kurenta ta yadda ba zata sake sha'awar wata mace ba a rayuwarta.
******
Hauwa.
Ta kasa fitowa waje saboda kunyar abinda Aminu yayi mata sai da aka yi sallar magriba kafin ta tattara yanata yanata ta koma gidanta tare da yaranta duka. Dama tun rana baƙi kowa ya kama kansa sai 'yan kauye da suka rage akan washe gari zasu wuce suma. Saboda naushin da Aminu ya yi mata sai da ya saka hakoranta na gaba yin girgiɗi alamar zasu faɗi, gashi ya sakar mata zazzaɓi sai da tasha maganin rage zugi kafin ta samu barci a ranar. Adama kuwa baƙin ciki goma da ashirin ga saki ga kuma wulaƙancin da Aminu ya yiwa mamanta ga kuma lalacewar aurensa da Najwa wanda a dalilin auren itama ta rasa nata auren, tun tana yin kukan fili har sai da ta koma yin na zuci, dan hakanan take jera ajiyar zuciya wanda ya saukar mata da ciwon kai mai tsanani da alama jininta ya hau, da kyar ta samu barci.
Washe gari Hauwa ta tashi saman dashishinta ya kumbura daga sama, sun tabbata fita zasu yi dan sosai suke yi mata ciwo, da kyar ma ta iya karyawa, bini bini take jan tsaki ta ƙumdumawa Aminu ashar, a haka Laure ta shigo gidan domin ta ƙara dubata da kuma jaje. Bayan sun gaisa Hauwa take cewa.