Sashe 76
Abin Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Najwa tana gama karanta haka ta saki shu'umin murmushi kana ta kuma kashe data ta kwantar da bayanta a jikin mota ta lumshe ido tare da jin wani farin ciki yana ratsata akan abinda ta aikata, tace a ranta.
Yadda na muzanta na rasa farin ciki kuma sai kun rasa shi wlh, saboda tare daku muka aikata komai, dole ko wanne ya amsa nashi rabon baƙin cikin.
A haka ta dinga tunani har barci ya É—auketa, sai da Saleema ta tasheta tana cewa.
Yadda kika samu barcin nan ya nuna alamar zaki samu natsuwa a garinmu, na tashe ki ne saboda mun kusa sauka tun É—azu muka shigo Kano.
Wlh da yake banyi barci mai daÉ—i ba shiyasa ga gajiyar biki dana duka.
Ta faÉ—a cikin sanyin murya.
Allah sai ya saka miki In Sha Allah.
Saleema ta faɗa tare da yin shuru tana duba agogon hannunta. A takaice sun isa gida gurin ƙarfe uku na rana suna shiga yaran Saleema suka rugo suna yi musu oyoyo da uniform ɗin makaranta a jikinsu, suka amsa trolley Najwa suka wuce part ɗinsu, sai da suka sha ruwa suka zauna a cushing tana tambayar babbar 'yarta Ikilima me suka dafa? tace taliya ce dafadukan manja kuma ya ƙare, sai tace ta shiga kitchen ta dafa musu indimie guda Huɗu dan da yunwa suka shigo, tace to kana ta wuce kitchen, a lokacin ne ɗan kishiyarta ya shigo yana ce mata babansu yana kiranta a ɓangarensa, tace to kana ta miƙe ta mayar da mayafinta tabi bayan yaron. Babban gida ne da yake da part huɗu nata ɗaya sai na kishiyarta uwar gidan malam sai kuma na amaryarsa da bai jima da aurenta ba sannan nashi ɓangaren da yake ganawa da mutanensa, sannan kuma turakarsa ne duk me girki can take samunsa. Saleema tana shiga ta sameshi zaune a dadduma ya jingina da jikin cushing da fara'arta ta ƙarasa ta zauna a carpet tana gaishe shi ya amsa fuska a haɗe tare da cewa.
An sanar dani kin dawo tare da baƙuwa shine na kira naji dalilin zuwa da ita ba tare da kin sanar dani ba.
Wlh zuwan bana shiri bane shiyasa na tawo da ita, dama nace in muka ƙaraso sai na sanar da kai.
Ke bana son shashanci taya zaki yi gaban kanki saboda baki ɗaukeni a bakin komai ba, Saleema na fa gaji da halinki duk cikin matana ke ce mai taurin kai kike bani matsala, banda ina duba darajar yaranmu da tuni na rabu dake wlh, to ina so ki tattarata ta bar mini gidana tun kafin dare yayi, dan kinsan bana karɓan baƙon da ba a sanar dani ba.
Subhanallahi haba malam, meyasa zaka yanke mini hukunci irin wannan ba tare da kaji uzuri na ba kuma...
Ki tashi ki bar mini falo tun kan ki harzuƙani, na kula ke zuma ce dole sai da wuta, in ba raini ba taya zaki yanke hukunci baki sanar dani ba, to na baki umarni ta bar mini gidana yanzu yanzu.
Yayi maganar a tsawace jikin Saleema yana rawa ta miƙe saboda tana mugun jin tsoronsa dan ba haka ya barta ba, da tashin hankali ta baro sashinsa da tunanin ina zata kai Najwa ta zauna kafin ta shawo kan malam ya haƙura.
*****
Nafeesa.
Tun ranar data bar gidan Najwa take jin ranta babu daɗi dan bata taɓa zaton Najwa zata yi mata haka ba, duk da tasan itace ta ci amanar ta amma amintarsu da kuma taimakon data yi mata na samun cikar burinta bata cancanci irin wannan wulaƙancin ba, yanzu babban tashin hankalinta data san sirrinta data jima tana ɓoyewa, tasan kuma halin Najwa muddun ta matsa mata to zata iya tona mata asiri, dole ne ta nima hanyar sulhu su ahirya ta kuma rabu da Aminu shine kaɗai mafita a garera dan ba zata so abinda tabirne ya tonu ba. Har zuwa washe gari da tunanin ta tashi ta yanke zuwa gidan Najwa dan suyi sulhu. Wajen ƙarfe sha biyun rana ta je gidan sai dai maigadi ya tabbatar mata da babu kowa a gidan tun safe da suka fita da Aminu basu dawo gidan ba, sannan koda ta kira wayarta a kashe cikin sanyin guiwa ta koma gida da tunanin gobe in Allah ya kaimu zata koma ta sameta, kamar zata wuce gidansu Binafa sai kuma ta fasa ta koma gida ta kwanta dakinsu ba jimawa barci ya ɗauke ta saboda jiya bata samu barcin kirki ba.
Yayanta Taju daya shigo gidan a hargitse ya wuce sashin mahaifinsu, nan ya same shi a falo ya zauna ya zayyana masa komai na saƙon da Najwa ta tura masa, ba ƙaramin tashin hankali babansu ya shiga ba dan haka cikin ɓacin rai suka baro part ɗinsa suka shiga sashinsu, a falo suka tadda mamanta nan itama suka sanar da ita salati take ta yi dan itama ta girgiza, Yaya Taju ya tambayi Nafeesan tana ina? Hajiyarsu tace tana ɗakinta a sama, cikin azama ya wuce zuwa ɗakin yadda ya bankaɗa ƙofar ta buɗe yasa Nafessa ta farka a firgice, sai dai kafin ta wastsake daga barci Taju ya rufeta da duka da belt ɗin wandonsa daya cire, ta shiga kwalla ihu tana kiran a ceceta sai dai babu wanda ya zo har sai da yayi mata lilis ya farfasa mata jiki kafin ya tsaya da dukan dan kansa yana mayar da numfashi, cikin huci yace.
Tashi muje falon ƙasa.
Bata yi watawata ba ta miƙe duk da ya tsamama mata jiki, haka ya tasa ƙeyarta suka sauko ƙasa, yadda taga fuskar mahaifinsu da Hajiyarsu shine ya ƙara mata tashin hankali dan nan take kwakwalwarta ta harbo mata da asirinta ya tonu Najwa ta tona mata asiri. Nafeesa ta gurfana a gabansu a ƙasa, Taju ya zauna a cushing ya ɗauko wayarsa ya soma karanta mata saƙon da aka turo masa, jikinta babu inda baya rawa dan sosai ta kaɗu da jin kamar Hamisu ne ya tona mata asiri ba Najwa ba, ana zaton wuta a makareta sai ga shi a masaka, Najwa ta bayar zata tona mata asiri sai gashi Hamisu ne yaci amanarta bayan ya ɓata mata rayuwa, sai ta rushe da kuka mai tsanani duk jijiyoyin kanta sun tashi tasan asirinta ya gama tonuwa, ƙarin takaici har da asirin Binafa ya tona, Taju ne ya daka mata tsawa akan ta faɗa musu gaskiyar abinda ya faru in kuma tayi masa ƙarya saiya karyata in yaso ayi jinyarta, to ya zata ɓoye ma bayan ranar wanka ba a ɓoyon cibi, dole ne ta amsa ƙaddararta tunda kuwa Alhaki kuikuyo ne ta tabbatar da hakkin Sameeha ne ƙila ya soma bibiyarta, tunda tasan da ita aka haɗa komai kusan itace ke ɗaura Nahwa akan yin wasu abubuwa, cikin kuka ta basu labari ta tabbatar musu da hakan ya faru harma da rayuwar da Binafa keyi na lesbian bata ɓoye ba, salati kawai iyayen suke yi Taju kuwa miƙewa yayi jikinsa babu inda bata rawa saboda masifa, ya shiga ya ɗauki Number ɗin da aka turo masa saƙon ya soma kira, sai dai baya shiga kwata kwata, ya dubeta a tsawace.
Ki bani number É—in Hamisu yanzu na kirashi.
Duk da ba waya a hannunta ta haddace number É—insa, nan take ta karanto masa ya saka a wayarsa ya kira, da aka É—aga wayar sai dai macece suka ji, Yaya Taju yace.
Ina me wayar ki bashi.
Sai suka ji ta buÉ—e murya tana cewa.
Baby baby kazo ana kiranka a waya.
Taju sansarai yayi yana jin kayan takaici, har Hamisu ya amsa wayar yana cewa.
Hello waye ne ke magana naga number ne.
Taju ya haÉ—iye miyau kwad na talaici yace cikin faÉ—a.
Da yayan Nafeesa kake magana, wato irin cin amanar da kayi mana kenan ka rabata da mutuncinta sannan ka sa ƙafa ka rabu da ita saboda mugunta, to dan haka ina so mu haɗu ka zo gidamu domin a yi sulhu a gyara lamarin tunda kai ka ɓata ta kai ne zaka aureta..
Kut wlh ni yanzu babu Nafeesa a rayuwata domin kuwa makon daya gabata nayi aure, dama inata son kusan abinda ya faru domin na nima tafiyar ku, don Allah kuyi haƙuri tsautsayi ne amma ina yi mata fatan alkhairi allah ya bata miji nagari, saboda wlh inna ce zan aureta zamanmu bazai yi daɗi ba saboda zargi ne zai shiga tsakaninmu.
Kutumar kaza kazanka ne, ka lalata mana yarinya sannan kana cewa ba zaka aureta ba, to ko yau kayi aure saika auri Nafisa in ba haka ba kuwa ka saurare sammaci daga kotu.
Hmmm yaya kenan, in kuka yi haka ai 'yarku kuka ciwa mutunci domin duk wanɗanda basu san me takaikata zasu sani, kunga kun ɓata sunan gidanku da zubewar mutuncinku, ni kuma duk abinda nayi ado ne wlh babu abinda zai ɓata mutunci na tunda nasan yadda zan kare kaina. Nafisa ko kyautarta kuka bani wlh bazan iya aurenta ba domin na ci moriyar ganga, kuma zuri'arku babu tarbiyya daga 'yan lesbian sai mai bin maza, idan kuma kace zaka ja maganar ina shirye daku.
Sai kit ya kashe wayarsa, tsabar jikin Taju daya yi sanyi komawa yayi ya zauna yama kasa magana, Iyayensu ma kasa maganar suka yi dan a handsfree ya saka wayar sunji duk maganarsa, Nafeesa kuwa kukan baƙin ciki take yi wanda yake cike da dana sani, ƙarin haushinta wai yayi aure ita ya gama da ita, mahaifiyarsu ce ta katse shurun da cewa.
Ya riga ya gama cutar damu kuma kema kin cucemu Nafeesa, yadda nake kula da tarbiyyarku ban taɓa zaton haka ba, dan haka ni zai fi kyau a bar maganar dan mu tsire da mutuncinmu shi kuma mu bar shi da Allah, sai mu tari matsalar mu samu wani mu haɗashi aure da ita, dan wlh aurenta shine namu rufin asirin.
Yadda na muzanta na rasa farin ciki kuma sai kun rasa shi wlh, saboda tare daku muka aikata komai, dole ko wanne ya amsa nashi rabon baƙin cikin.
A haka ta dinga tunani har barci ya É—auketa, sai da Saleema ta tasheta tana cewa.
Yadda kika samu barcin nan ya nuna alamar zaki samu natsuwa a garinmu, na tashe ki ne saboda mun kusa sauka tun É—azu muka shigo Kano.
Wlh da yake banyi barci mai daÉ—i ba shiyasa ga gajiyar biki dana duka.
Ta faÉ—a cikin sanyin murya.
Allah sai ya saka miki In Sha Allah.
Saleema ta faɗa tare da yin shuru tana duba agogon hannunta. A takaice sun isa gida gurin ƙarfe uku na rana suna shiga yaran Saleema suka rugo suna yi musu oyoyo da uniform ɗin makaranta a jikinsu, suka amsa trolley Najwa suka wuce part ɗinsu, sai da suka sha ruwa suka zauna a cushing tana tambayar babbar 'yarta Ikilima me suka dafa? tace taliya ce dafadukan manja kuma ya ƙare, sai tace ta shiga kitchen ta dafa musu indimie guda Huɗu dan da yunwa suka shigo, tace to kana ta wuce kitchen, a lokacin ne ɗan kishiyarta ya shigo yana ce mata babansu yana kiranta a ɓangarensa, tace to kana ta miƙe ta mayar da mayafinta tabi bayan yaron. Babban gida ne da yake da part huɗu nata ɗaya sai na kishiyarta uwar gidan malam sai kuma na amaryarsa da bai jima da aurenta ba sannan nashi ɓangaren da yake ganawa da mutanensa, sannan kuma turakarsa ne duk me girki can take samunsa. Saleema tana shiga ta sameshi zaune a dadduma ya jingina da jikin cushing da fara'arta ta ƙarasa ta zauna a carpet tana gaishe shi ya amsa fuska a haɗe tare da cewa.
An sanar dani kin dawo tare da baƙuwa shine na kira naji dalilin zuwa da ita ba tare da kin sanar dani ba.
Wlh zuwan bana shiri bane shiyasa na tawo da ita, dama nace in muka ƙaraso sai na sanar da kai.
Ke bana son shashanci taya zaki yi gaban kanki saboda baki ɗaukeni a bakin komai ba, Saleema na fa gaji da halinki duk cikin matana ke ce mai taurin kai kike bani matsala, banda ina duba darajar yaranmu da tuni na rabu dake wlh, to ina so ki tattarata ta bar mini gidana tun kafin dare yayi, dan kinsan bana karɓan baƙon da ba a sanar dani ba.
Subhanallahi haba malam, meyasa zaka yanke mini hukunci irin wannan ba tare da kaji uzuri na ba kuma...
Ki tashi ki bar mini falo tun kan ki harzuƙani, na kula ke zuma ce dole sai da wuta, in ba raini ba taya zaki yanke hukunci baki sanar dani ba, to na baki umarni ta bar mini gidana yanzu yanzu.
Yayi maganar a tsawace jikin Saleema yana rawa ta miƙe saboda tana mugun jin tsoronsa dan ba haka ya barta ba, da tashin hankali ta baro sashinsa da tunanin ina zata kai Najwa ta zauna kafin ta shawo kan malam ya haƙura.
*****
Nafeesa.
Tun ranar data bar gidan Najwa take jin ranta babu daɗi dan bata taɓa zaton Najwa zata yi mata haka ba, duk da tasan itace ta ci amanar ta amma amintarsu da kuma taimakon data yi mata na samun cikar burinta bata cancanci irin wannan wulaƙancin ba, yanzu babban tashin hankalinta data san sirrinta data jima tana ɓoyewa, tasan kuma halin Najwa muddun ta matsa mata to zata iya tona mata asiri, dole ne ta nima hanyar sulhu su ahirya ta kuma rabu da Aminu shine kaɗai mafita a garera dan ba zata so abinda tabirne ya tonu ba. Har zuwa washe gari da tunanin ta tashi ta yanke zuwa gidan Najwa dan suyi sulhu. Wajen ƙarfe sha biyun rana ta je gidan sai dai maigadi ya tabbatar mata da babu kowa a gidan tun safe da suka fita da Aminu basu dawo gidan ba, sannan koda ta kira wayarta a kashe cikin sanyin guiwa ta koma gida da tunanin gobe in Allah ya kaimu zata koma ta sameta, kamar zata wuce gidansu Binafa sai kuma ta fasa ta koma gida ta kwanta dakinsu ba jimawa barci ya ɗauke ta saboda jiya bata samu barcin kirki ba.
Yayanta Taju daya shigo gidan a hargitse ya wuce sashin mahaifinsu, nan ya same shi a falo ya zauna ya zayyana masa komai na saƙon da Najwa ta tura masa, ba ƙaramin tashin hankali babansu ya shiga ba dan haka cikin ɓacin rai suka baro part ɗinsa suka shiga sashinsu, a falo suka tadda mamanta nan itama suka sanar da ita salati take ta yi dan itama ta girgiza, Yaya Taju ya tambayi Nafeesan tana ina? Hajiyarsu tace tana ɗakinta a sama, cikin azama ya wuce zuwa ɗakin yadda ya bankaɗa ƙofar ta buɗe yasa Nafessa ta farka a firgice, sai dai kafin ta wastsake daga barci Taju ya rufeta da duka da belt ɗin wandonsa daya cire, ta shiga kwalla ihu tana kiran a ceceta sai dai babu wanda ya zo har sai da yayi mata lilis ya farfasa mata jiki kafin ya tsaya da dukan dan kansa yana mayar da numfashi, cikin huci yace.
Tashi muje falon ƙasa.
Bata yi watawata ba ta miƙe duk da ya tsamama mata jiki, haka ya tasa ƙeyarta suka sauko ƙasa, yadda taga fuskar mahaifinsu da Hajiyarsu shine ya ƙara mata tashin hankali dan nan take kwakwalwarta ta harbo mata da asirinta ya tonu Najwa ta tona mata asiri. Nafeesa ta gurfana a gabansu a ƙasa, Taju ya zauna a cushing ya ɗauko wayarsa ya soma karanta mata saƙon da aka turo masa, jikinta babu inda baya rawa dan sosai ta kaɗu da jin kamar Hamisu ne ya tona mata asiri ba Najwa ba, ana zaton wuta a makareta sai ga shi a masaka, Najwa ta bayar zata tona mata asiri sai gashi Hamisu ne yaci amanarta bayan ya ɓata mata rayuwa, sai ta rushe da kuka mai tsanani duk jijiyoyin kanta sun tashi tasan asirinta ya gama tonuwa, ƙarin takaici har da asirin Binafa ya tona, Taju ne ya daka mata tsawa akan ta faɗa musu gaskiyar abinda ya faru in kuma tayi masa ƙarya saiya karyata in yaso ayi jinyarta, to ya zata ɓoye ma bayan ranar wanka ba a ɓoyon cibi, dole ne ta amsa ƙaddararta tunda kuwa Alhaki kuikuyo ne ta tabbatar da hakkin Sameeha ne ƙila ya soma bibiyarta, tunda tasan da ita aka haɗa komai kusan itace ke ɗaura Nahwa akan yin wasu abubuwa, cikin kuka ta basu labari ta tabbatar musu da hakan ya faru harma da rayuwar da Binafa keyi na lesbian bata ɓoye ba, salati kawai iyayen suke yi Taju kuwa miƙewa yayi jikinsa babu inda bata rawa saboda masifa, ya shiga ya ɗauki Number ɗin da aka turo masa saƙon ya soma kira, sai dai baya shiga kwata kwata, ya dubeta a tsawace.
Ki bani number É—in Hamisu yanzu na kirashi.
Duk da ba waya a hannunta ta haddace number É—insa, nan take ta karanto masa ya saka a wayarsa ya kira, da aka É—aga wayar sai dai macece suka ji, Yaya Taju yace.
Ina me wayar ki bashi.
Sai suka ji ta buÉ—e murya tana cewa.
Baby baby kazo ana kiranka a waya.
Taju sansarai yayi yana jin kayan takaici, har Hamisu ya amsa wayar yana cewa.
Hello waye ne ke magana naga number ne.
Taju ya haÉ—iye miyau kwad na talaici yace cikin faÉ—a.
Da yayan Nafeesa kake magana, wato irin cin amanar da kayi mana kenan ka rabata da mutuncinta sannan ka sa ƙafa ka rabu da ita saboda mugunta, to dan haka ina so mu haɗu ka zo gidamu domin a yi sulhu a gyara lamarin tunda kai ka ɓata ta kai ne zaka aureta..
Kut wlh ni yanzu babu Nafeesa a rayuwata domin kuwa makon daya gabata nayi aure, dama inata son kusan abinda ya faru domin na nima tafiyar ku, don Allah kuyi haƙuri tsautsayi ne amma ina yi mata fatan alkhairi allah ya bata miji nagari, saboda wlh inna ce zan aureta zamanmu bazai yi daɗi ba saboda zargi ne zai shiga tsakaninmu.
Kutumar kaza kazanka ne, ka lalata mana yarinya sannan kana cewa ba zaka aureta ba, to ko yau kayi aure saika auri Nafisa in ba haka ba kuwa ka saurare sammaci daga kotu.
Hmmm yaya kenan, in kuka yi haka ai 'yarku kuka ciwa mutunci domin duk wanɗanda basu san me takaikata zasu sani, kunga kun ɓata sunan gidanku da zubewar mutuncinku, ni kuma duk abinda nayi ado ne wlh babu abinda zai ɓata mutunci na tunda nasan yadda zan kare kaina. Nafisa ko kyautarta kuka bani wlh bazan iya aurenta ba domin na ci moriyar ganga, kuma zuri'arku babu tarbiyya daga 'yan lesbian sai mai bin maza, idan kuma kace zaka ja maganar ina shirye daku.
Sai kit ya kashe wayarsa, tsabar jikin Taju daya yi sanyi komawa yayi ya zauna yama kasa magana, Iyayensu ma kasa maganar suka yi dan a handsfree ya saka wayar sunji duk maganarsa, Nafeesa kuwa kukan baƙin ciki take yi wanda yake cike da dana sani, ƙarin haushinta wai yayi aure ita ya gama da ita, mahaifiyarsu ce ta katse shurun da cewa.
Ya riga ya gama cutar damu kuma kema kin cucemu Nafeesa, yadda nake kula da tarbiyyarku ban taɓa zaton haka ba, dan haka ni zai fi kyau a bar maganar dan mu tsire da mutuncinmu shi kuma mu bar shi da Allah, sai mu tari matsalar mu samu wani mu haɗashi aure da ita, dan wlh aurenta shine namu rufin asirin.