Sashe 64
Abin Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ahaf sai dai ba Najwa ba, wlh zata aikata fiye da haka ma, na karanci yarinyar nan kamar yunwar cikina tana mugun son abin duniya da hangen na sama da ita, kunga kuwa daga haka sai Hasssada da kyashi ya samu gurbi a zuciyarta, Allah ya kyauta sai yanzu na ƙara godewa Allah daya rabani da ita, dan wlh ba zan jure wannan halin nata na son rai ba, taje can ta yiwa wani.
Wlh yaya ta bani mamaki ai kaga da kunya tazo inda muke, har yau bata san kalar É—akunanmu ba dan bata zo ba.
Cewar Ikram, Zaidu yace cikin taɓe baki.
Taya zata zo ta tafka abin kunya, ai wlh Najwa sai dai taci darajar Inna aje mata biki amma da dan halinta ne kare ba zata gani ba.
Allah ya kyauta ya shiryeta ni wlh lamarin ta ya fara bani tsoro.
Cewar Umma, Sameeha tace.
Ai sai dai addu'a dan kuwa in da tayi nadamar abinda ta yi to da ta tako ƙafarta tazo gidajenmu ta bamu hakuri, ke kuma Ikram kin kyauta da kika fasa maganar, sai dai dan Allah mu barshi a tsakaninmu kar wanda ya nuna mata.
Dama wa yake da lokacinta, darajar inna dai zata ci Allah yasa ta zauna a auren, dan wannan bakin hali gareta.
Zaidu bana son haka dan fata na gari lamiri, duk lalacewarta jininmu ce fatan shiriya za muyi mata.
Cewar umma, haka suka cigaba da hira har aka kira sallar La'asar suka tashi kowa yaje ya gabatar da nashi. Sai gabda Magrib su Sameeha suka bar gida, umma ce ma ta korasu da so suka yi sai bayan sallar isha'i su tafi tace bata amince ba su tafi ido na ganin ido, cikin farin ciki suka rabu da juna bayan sunyi guzurin sauran waina da farfesu, sannan Sameeha ta turawa Zaidu kuɗi masu kauri akan ya ƙara musu kayan abinci sannan Ikram ta bada dubu hamsin akan akaiwa Inna gudunmawarsu su duka, Zaidu kuma ya bawa umma dubu ashirin ta bada nata gudunmawar, wannan ahali suna cikin rufin asirin Allah da kuma kwanciyar hankali. Samedha sai da ta sauke Ikram a gida kafin ta wuce gidanta itama, a sashin Hakiya ta yada zango da tsarabar data soya a cewarta Umma ce ta ce a kawo musu tare da waina da farfesu, wanda Hajiya shi taci a abincin daranta, dan tana son waina sosai kuma taji dadin wannan, sai wajen ƙarfe goma saura Sameeha ta bar sashin Hajiya ta wuce ɓangaren ta.
Washe gari Ibrahim yazo tunda ya dawo bai zauna ba dan haka a gurin uwargida ya sauka ya kwana, washe gari ma ya ƙara kwana sai ranar monday suka bar Kaduna da Sameeha. Koda suka isa Abuja gida ne mai matukar girma da kyau shima gidan sama ne har yafi gidanta na Kaduna kyau da tsaruwa, haka ta fara sabuwar rayuwa a gidan, Allah yasa akwai maikata har da me aiki wata dattijuwa mai suna iya, cikin kwana biyu ta saba da ita har suke ɗan taɓa hira in ta sauko ƙasa, saboda Ibrahim In ya fita tun safe sai dare yake dawowa, Sameeha bata yarda ta zauna ba dan ita ke girma musu abinci, sai dai Iya ta girka nasu da masu aikin gidan. A rana na uku ne Ibrahim ya kaita gidan Anty Amina can ta wuni sai dare ya biya ya ɗauketa suka koma gida.
***
Ranar asabar.
Da yamma Ibrahim ya ɗauketa zuwa wani super market dan tayi siyayyan kayan abinci data duba babu wasu a cikin cefanen da aka yi mata, Ibrahim yasha ƙananun kaya yayi kyau ita kuma ta saka ash ɗin jallabiya tasha aiki ta yane kanta da gyalen abayar, suna isa suka yi parking Security suka fito suka buɗe musu motar dan dama suna biye da motarsu a baya, sannan suka take musu baya suka shiga ciki, wani sucurity ya kamawa Sameeha keke ita kuma tana zabar abinda take so tana sakawa a ciki. Aminu tun shigowarsu ya angeta sai yayi sauri ya tare yaran kar su ganta saboda tare dasu ya zo siyayyar kayan ciye ciye na makarantarsu, tunda ya ganta zuciyarsa ta shiga bugawa da sauri da sauri yaga ta sauya komai nata ya nuna hutu da jin daɗi, yadda yaga Ibrahim yana take mata baya yasan mijinta ne kuma dama ya waye shi tunda Senator Ibrahim dole mutane sun waye shi, ko ba a fili ba a hoto ko a tv, Allah Allah ya riƙa yi su fita dan kar yaran su ganta shiyasa yayi sauri ya jasu suka isa wajen biyan Kuɗi duk da basu gama sayayyar ba, ya biya kuɗi aka zuba musu a leda ma'aikata gurin suka kai musu mota, ya buɗe mota da sauri yaran suka shiga shima ya shiga mazaunin driver yana shirin tada mota, Sameeha ce ta fito da sauri zata ɗauki wayarta data bari mota akan zata kira iya mai aikinta ta tambayeta wasu abubuwan da babu a kitchen ɗinsu na abinci su saya musu, Abi shine ya fara ganinta yayi wani zullo yana cewa da ƙarfi.
Laaaa Abba ga Mamanmu wlh ita ce mamanmu ce, Amrah ga Mama.
Amrah ta shiga raba ido tana kallon inda Abi yake nuna mata, aiko tana tozali da Sameeha ta buɗe mota ta fita da gudun ta bi ta isa gurin Sameeha data buɗe mota ta miƙa hannu dan ɗaukar wayarta sai taji an faɗa mata ta baya an riƙe ta da ƙarfi ana haki ba tare da anyi magana ba, da sauri ta juyo dan taga waye sai kawai tayi tozali da Abi yanata yi mata dariya ga hawaye kwance aidonsa, Amrah kuwa taƙi sakinta dan ta ruƙunƙumeta tana kuka, dan ji take kamar zata ɓacewa ganinta, Sameeha cikin rawar murya tace.
Abi Amrah kune, in abbanku?
Yana mota har zamu tafi mun gama sayayya naga kin fito daga ciki ashe Mama kina cikin garin nan baki zo ba.
Mama wlh saina biki gida bazan koma gurin Abba ba.
Cewar Amrah data ɗago tana kallonta ido shaɓe shaɓe da hawaye, kallonsu kawai take yi yaran sun sauya mata dan sosai suka ƙara yi mata girma ga fresh da suka yi na hutu, ta tabbatar suna samun kulawa mai kyau a gurin mahaifinsu. Ibrahim ne ya fito ya dubata dan yaji shurun yayi yawa sai ya hangeta tare da yara suna magana, ya ƙaraso security na biye dashi su biyu, yana ganin yaran ya tabbatar da yaranta ne saboda Amrah tayi kama da ita sosai, cikin fara'a yace.
Ko ban faÉ—a ba yaranki ne ko? Big boy ya sunanka.?
Ya miƙawa Abi hannu sai dai mai miƙa mata ba ya tsaya yana kallonsa dan bai waye shi ba, Sameeha ta dan yi murmushin yaƙe tana cewa.
Abi shima babanku ne ka amsa masa magana mana.
Abi yace sunana Adam, wannan kuma Ƙanwata ce Amratu.
Masha Allah Allah ya muku albarka Amin. Hajiyata ya aka yi kika haÉ—u da yaran nan.
Suma siyayya suka zo yi sun gama zasu wuce shine suka hango fitowata.
Ayya to bari na jiraki ki gama da su kin san nan É—in ba tsaro sosai.
Cewar Ibrahim kana ya buɗe mota back seat ya zauna ya rufe ya shiga amsa waya, Aminu yana hango su amma yaƙi zuwa ganin yaran zasu bata masa lokaci ya fito yana kwala musu kira.
Kai Abi Amrah kuzo mu wuce.
Ni dai Mama ke zan bi.
Cewar Amrah tana maƙewa babansu kafaɗa, Abi da yake yaron yana da wayo ya fahimci wani abu dan haka ya isa gurin Amrah yace.
Kizo muje Abba zai kaimu gurinta kinji.
Ni dai ba zan je ba.
Haba Amrata Abban kike cewa ba zaki bi shi ba, kije zan zo har gida na ɗaukeku, karki ɓatawa Abba rai yayi fushi, ko kina so Allah ya saka ki a wuta ne kin ɓata masa rai.
Cewar Sameeha, Amra ta girgizata mata kai alamar bata so Allah ya sata a wuta sai Sameeha ta kama hannunta ta jata tana cewa.
Yauwa yarinyar kirki kije gurin Abba da kaina zan zo na É—auke ku.
Amrah bata ce komai ba sai ɓata fuska data yi a haka har suka isa gurin motarsu Sameeha ta buɗe back seat ta tura Amrah ciki kana ta rufe motar ta juya ta kalli Aminu tana cewa.
Nagode da ganin yarana cikin kyakkyawar kamala, amma ina so ka gane ka daina ɗaukar alhakinmu domin ni dasu muna buƙatar juna.
Tana gama faɗar haka ta juya ta wuto gurin mijinta ko waige bata yi ba, duk da zuciyarta a karye yake abu kaɗan zai iya saka ta fashe da kuka, dan sosai kewar yaranta suka taso masa har take jin wani damuwa a zuciyarta, Aminu kam bai ce mata komai ba ya buɗe mota ya shiga ya kunna ya rufe ta ciki dan kar Amra ta yi yunƙurin buɗewa, ya jasu suka wuce Amrah tana kwalawa Sameeha kira tana kuka.
Maama, maaamaaa mun tafi dan Allah ki zo ki É—auke mu.
Sameeha buÉ—e mota tayi ta shiga ta zauna gefen Ibrahim ta shiga matsalar kwalla, bai ce mata komai ba ya cigaba da hidimarsa domin kishi ya motsa, dan gani yake ganin Aminu ne ya sata kuka ba yaran ba.
Tofa...
[7/7, 13:04] BuhainatðŸ˜: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*
40.
Sameeha tana kuka tana sharewa Ibrahim ya muskuta alamar zai fita daga motar yana cewa.
Da alama siyayyar nan ba zai yuwu yau ba tunda ganin tsohon mijinki ya tada miki hankali, ban zaci har yanzu kina son sa ba ai.
Da sauri Sameeha ta ɗago kai tana mamakin maganarsa sai a lokacin ne ma ta fahimci fuskarsa ta sauya bata wani ɓata lokaci ba ta matsa ta rungumeshi ta gefe tana share hawayenta.
Wlh yaya ta bani mamaki ai kaga da kunya tazo inda muke, har yau bata san kalar É—akunanmu ba dan bata zo ba.
Cewar Ikram, Zaidu yace cikin taɓe baki.
Taya zata zo ta tafka abin kunya, ai wlh Najwa sai dai taci darajar Inna aje mata biki amma da dan halinta ne kare ba zata gani ba.
Allah ya kyauta ya shiryeta ni wlh lamarin ta ya fara bani tsoro.
Cewar Umma, Sameeha tace.
Ai sai dai addu'a dan kuwa in da tayi nadamar abinda ta yi to da ta tako ƙafarta tazo gidajenmu ta bamu hakuri, ke kuma Ikram kin kyauta da kika fasa maganar, sai dai dan Allah mu barshi a tsakaninmu kar wanda ya nuna mata.
Dama wa yake da lokacinta, darajar inna dai zata ci Allah yasa ta zauna a auren, dan wannan bakin hali gareta.
Zaidu bana son haka dan fata na gari lamiri, duk lalacewarta jininmu ce fatan shiriya za muyi mata.
Cewar umma, haka suka cigaba da hira har aka kira sallar La'asar suka tashi kowa yaje ya gabatar da nashi. Sai gabda Magrib su Sameeha suka bar gida, umma ce ma ta korasu da so suka yi sai bayan sallar isha'i su tafi tace bata amince ba su tafi ido na ganin ido, cikin farin ciki suka rabu da juna bayan sunyi guzurin sauran waina da farfesu, sannan Sameeha ta turawa Zaidu kuɗi masu kauri akan ya ƙara musu kayan abinci sannan Ikram ta bada dubu hamsin akan akaiwa Inna gudunmawarsu su duka, Zaidu kuma ya bawa umma dubu ashirin ta bada nata gudunmawar, wannan ahali suna cikin rufin asirin Allah da kuma kwanciyar hankali. Samedha sai da ta sauke Ikram a gida kafin ta wuce gidanta itama, a sashin Hakiya ta yada zango da tsarabar data soya a cewarta Umma ce ta ce a kawo musu tare da waina da farfesu, wanda Hajiya shi taci a abincin daranta, dan tana son waina sosai kuma taji dadin wannan, sai wajen ƙarfe goma saura Sameeha ta bar sashin Hajiya ta wuce ɓangaren ta.
Washe gari Ibrahim yazo tunda ya dawo bai zauna ba dan haka a gurin uwargida ya sauka ya kwana, washe gari ma ya ƙara kwana sai ranar monday suka bar Kaduna da Sameeha. Koda suka isa Abuja gida ne mai matukar girma da kyau shima gidan sama ne har yafi gidanta na Kaduna kyau da tsaruwa, haka ta fara sabuwar rayuwa a gidan, Allah yasa akwai maikata har da me aiki wata dattijuwa mai suna iya, cikin kwana biyu ta saba da ita har suke ɗan taɓa hira in ta sauko ƙasa, saboda Ibrahim In ya fita tun safe sai dare yake dawowa, Sameeha bata yarda ta zauna ba dan ita ke girma musu abinci, sai dai Iya ta girka nasu da masu aikin gidan. A rana na uku ne Ibrahim ya kaita gidan Anty Amina can ta wuni sai dare ya biya ya ɗauketa suka koma gida.
***
Ranar asabar.
Da yamma Ibrahim ya ɗauketa zuwa wani super market dan tayi siyayyan kayan abinci data duba babu wasu a cikin cefanen da aka yi mata, Ibrahim yasha ƙananun kaya yayi kyau ita kuma ta saka ash ɗin jallabiya tasha aiki ta yane kanta da gyalen abayar, suna isa suka yi parking Security suka fito suka buɗe musu motar dan dama suna biye da motarsu a baya, sannan suka take musu baya suka shiga ciki, wani sucurity ya kamawa Sameeha keke ita kuma tana zabar abinda take so tana sakawa a ciki. Aminu tun shigowarsu ya angeta sai yayi sauri ya tare yaran kar su ganta saboda tare dasu ya zo siyayyar kayan ciye ciye na makarantarsu, tunda ya ganta zuciyarsa ta shiga bugawa da sauri da sauri yaga ta sauya komai nata ya nuna hutu da jin daɗi, yadda yaga Ibrahim yana take mata baya yasan mijinta ne kuma dama ya waye shi tunda Senator Ibrahim dole mutane sun waye shi, ko ba a fili ba a hoto ko a tv, Allah Allah ya riƙa yi su fita dan kar yaran su ganta shiyasa yayi sauri ya jasu suka isa wajen biyan Kuɗi duk da basu gama sayayyar ba, ya biya kuɗi aka zuba musu a leda ma'aikata gurin suka kai musu mota, ya buɗe mota da sauri yaran suka shiga shima ya shiga mazaunin driver yana shirin tada mota, Sameeha ce ta fito da sauri zata ɗauki wayarta data bari mota akan zata kira iya mai aikinta ta tambayeta wasu abubuwan da babu a kitchen ɗinsu na abinci su saya musu, Abi shine ya fara ganinta yayi wani zullo yana cewa da ƙarfi.
Laaaa Abba ga Mamanmu wlh ita ce mamanmu ce, Amrah ga Mama.
Amrah ta shiga raba ido tana kallon inda Abi yake nuna mata, aiko tana tozali da Sameeha ta buɗe mota ta fita da gudun ta bi ta isa gurin Sameeha data buɗe mota ta miƙa hannu dan ɗaukar wayarta sai taji an faɗa mata ta baya an riƙe ta da ƙarfi ana haki ba tare da anyi magana ba, da sauri ta juyo dan taga waye sai kawai tayi tozali da Abi yanata yi mata dariya ga hawaye kwance aidonsa, Amrah kuwa taƙi sakinta dan ta ruƙunƙumeta tana kuka, dan ji take kamar zata ɓacewa ganinta, Sameeha cikin rawar murya tace.
Abi Amrah kune, in abbanku?
Yana mota har zamu tafi mun gama sayayya naga kin fito daga ciki ashe Mama kina cikin garin nan baki zo ba.
Mama wlh saina biki gida bazan koma gurin Abba ba.
Cewar Amrah data ɗago tana kallonta ido shaɓe shaɓe da hawaye, kallonsu kawai take yi yaran sun sauya mata dan sosai suka ƙara yi mata girma ga fresh da suka yi na hutu, ta tabbatar suna samun kulawa mai kyau a gurin mahaifinsu. Ibrahim ne ya fito ya dubata dan yaji shurun yayi yawa sai ya hangeta tare da yara suna magana, ya ƙaraso security na biye dashi su biyu, yana ganin yaran ya tabbatar da yaranta ne saboda Amrah tayi kama da ita sosai, cikin fara'a yace.
Ko ban faÉ—a ba yaranki ne ko? Big boy ya sunanka.?
Ya miƙawa Abi hannu sai dai mai miƙa mata ba ya tsaya yana kallonsa dan bai waye shi ba, Sameeha ta dan yi murmushin yaƙe tana cewa.
Abi shima babanku ne ka amsa masa magana mana.
Abi yace sunana Adam, wannan kuma Ƙanwata ce Amratu.
Masha Allah Allah ya muku albarka Amin. Hajiyata ya aka yi kika haÉ—u da yaran nan.
Suma siyayya suka zo yi sun gama zasu wuce shine suka hango fitowata.
Ayya to bari na jiraki ki gama da su kin san nan É—in ba tsaro sosai.
Cewar Ibrahim kana ya buɗe mota back seat ya zauna ya rufe ya shiga amsa waya, Aminu yana hango su amma yaƙi zuwa ganin yaran zasu bata masa lokaci ya fito yana kwala musu kira.
Kai Abi Amrah kuzo mu wuce.
Ni dai Mama ke zan bi.
Cewar Amrah tana maƙewa babansu kafaɗa, Abi da yake yaron yana da wayo ya fahimci wani abu dan haka ya isa gurin Amrah yace.
Kizo muje Abba zai kaimu gurinta kinji.
Ni dai ba zan je ba.
Haba Amrata Abban kike cewa ba zaki bi shi ba, kije zan zo har gida na ɗaukeku, karki ɓatawa Abba rai yayi fushi, ko kina so Allah ya saka ki a wuta ne kin ɓata masa rai.
Cewar Sameeha, Amra ta girgizata mata kai alamar bata so Allah ya sata a wuta sai Sameeha ta kama hannunta ta jata tana cewa.
Yauwa yarinyar kirki kije gurin Abba da kaina zan zo na É—auke ku.
Amrah bata ce komai ba sai ɓata fuska data yi a haka har suka isa gurin motarsu Sameeha ta buɗe back seat ta tura Amrah ciki kana ta rufe motar ta juya ta kalli Aminu tana cewa.
Nagode da ganin yarana cikin kyakkyawar kamala, amma ina so ka gane ka daina ɗaukar alhakinmu domin ni dasu muna buƙatar juna.
Tana gama faɗar haka ta juya ta wuto gurin mijinta ko waige bata yi ba, duk da zuciyarta a karye yake abu kaɗan zai iya saka ta fashe da kuka, dan sosai kewar yaranta suka taso masa har take jin wani damuwa a zuciyarta, Aminu kam bai ce mata komai ba ya buɗe mota ya shiga ya kunna ya rufe ta ciki dan kar Amra ta yi yunƙurin buɗewa, ya jasu suka wuce Amrah tana kwalawa Sameeha kira tana kuka.
Maama, maaamaaa mun tafi dan Allah ki zo ki É—auke mu.
Sameeha buÉ—e mota tayi ta shiga ta zauna gefen Ibrahim ta shiga matsalar kwalla, bai ce mata komai ba ya cigaba da hidimarsa domin kishi ya motsa, dan gani yake ganin Aminu ne ya sata kuka ba yaran ba.
Tofa...
[7/7, 13:04] BuhainatðŸ˜: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*
40.
Sameeha tana kuka tana sharewa Ibrahim ya muskuta alamar zai fita daga motar yana cewa.
Da alama siyayyar nan ba zai yuwu yau ba tunda ganin tsohon mijinki ya tada miki hankali, ban zaci har yanzu kina son sa ba ai.
Da sauri Sameeha ta ɗago kai tana mamakin maganarsa sai a lokacin ne ma ta fahimci fuskarsa ta sauya bata wani ɓata lokaci ba ta matsa ta rungumeshi ta gefe tana share hawayenta.