Sashe 74
Abin Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cewar Sameeha tana murmushi, shigowar su Abi da ledar biscuit da chocolate yasa su sauya hira, Zaidu kam sai sam barka yakewa kansa da Allah ya raba shi da Najwa, ɗan ko a ƙafa aka ɗaura masa ita baya jin zai jata.
[7/7, 13:04] BuhainatðŸ˜: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*
46.
Aminu.
Bayan ya sayowa yara kayan ciye ciye sai ya shiga mota ya wuce zuwa babban gida dan so yake yau Hauwa ta gane kuranta, yana tafiya yana duban a gogo wanda ya nuna kusan goma da mintuna yasan sun ɓata lokaci sosai a gidan umma, sai ya ji zuciyarsa fes kamar ya sauke wani mai nauyi, na farko ya wanke Sameeha ya kuma bata yaransu sannan kuma ya rabu da Najwa da yake jinsa kamar an ɗaura masa ƙarfe a wiya, yanzu ya zama free sai kuma ya mayar da hankalinta kan batun aikinsa, da farko da aka yi masa tayin aikin yaƙi amsa saboda yaransa da suke hannunsa, yaji ba zai iya barin mahaifarsa ba gwara a ɗaura wani akan tafiya London ɗin, su kuma sun fi so shi ya yi tafiyar domin sun san ba zai basu kunya ba, yafi ƙarfin wata da suke ta binsa da wannan maganar dan har bashi lokaci suka yi akan wataƙila ya sauta ra'ayinsa,sai gashi kuma cikin yardan Allah ya amsa musu da zai yi tafiyar ɗazun da safe ya kiransu, dan yana so yayi nesa da kowa ya yi rayuwa a inda ba wanda ya sanshi, kuma yana so ya mayar da hankalinsa wajen niman lafiya a can ƙila ya dace ya samu lafiyar, da tunani barkatai ya isa babban gida yayi parking a ƙofar gate ya fito ya shiga gidan, ya samu mata da yara ana ta hayaniya da alama basu daɗe da gama karyawa dan yaga kofuna da robobin na suka ci ƙosar birjik a tsakar gida, matan da suka fara ganinsa suka fara sakin guda suna ga Ango ga Ango, Aminu kam murmushin takaici yake yi yana gaishe su, a tsakar gidan ya tsaya ya tambayi Salma data fito daga ɗakin Sa'a ina Hauwa ta kira masa ita, tace masa to kana ta isa shashin Laure ta faɗa mata saƙon Aminu sai cewa tayi ta dawo tace masa ya zo sashin Laure, Aminu ya yi guntun murmushi ya ce.
Ki ce mata ta fito tsakar gidan sauri nake yi.
Salma ta koma ta faɗa mata sai gata tazo buguzum buguzum ta ƙaraso tana cewa.
Haba Ango saurin me kake yi ko amarya tayi ce kira. To gani ya kwanan amarya fatan ka yaba da zaɓina.
Ta ƙare maganar tana tsayawa a gabansa.
Aminu ya kalleta ido cikin ido yana cewa.
Gaskiya kam na yaba da zaɓinki wanda kika saka son zuciya a ciki da son kai, ban ɗauka tsanar da kika yiwa Sameeha har ya kai haka ba, ki rasa wacce zaki aura mini sai 'yar uwarta saboda kawai ki muzguna mata.
Haba Aminu meye laifina dan na zaɓa maka matar da zata share maka hawaye ta kula da kai, yarinya mahaddaciya mai tarbiyya kuma.
Bata rufe baki ba ya daga hannu ya wanka mata lafiyayyen mari kafin ta dawo dai dai ya ƙara marinta a ɗayan kuncin, a gigice Hauwa ta dafe duka kuncinta tana kallonsa a razane idonta a warwaje cike da tsantsar mamaki da tsoro tace.
Ni ka mara Aminu daga abun arziki, in yi maka fari ni kayi mini baƙi, ko dai su Sameeha sun bi boka da malamai sun sauya maka tunani.
Bata rufe baki ba ya dunƙula hannu ya nausa mata a baki wanda nan take bakin ya fashe ya soma jini, Hauwa ta tsandara ihu ta baje a ƙasa tana cewa.
Shikenan sun rabani da É—an uwana innalillahi wa inna ilaihir raji'un, Aminu ni kake duka ina matsayin yayarka.
Aminu ya daka mata uwar tsawa wanda yasa mutane duk suka taru akansu, waÉ—anda suke nesa ma da basu san ana yi ba suka matso.
Yayar banza yayar wofi muguwa azzaluma shaiɗaiya, idan sunan Sameeha bai fita daga bakinki ba wlh sai ba kasheki in yaso nima a kasheni. Kin tarwatsa mini farin ciki na da ni da iyalina, Hauwa kin zame mini matsala a rayuwata. Kece kika saka na rasa lafiyata wanda ya jawo dalilin dana rabu da mata ta, tun lokacin da kika kirani kika fana mini rasuwar Umma nayi accident a lokacin na rasa mazantakata na rasa lafiyar da zan kusanci matata, tsawon shekara shida Sameeha tayi dani tana haƙuri ba tare dana sauke hakkin aurenta ba, bayan mun dawo Kaduna kika matsa mata kika dinga yi mata bita da ƙulli duk saboda son zuciyarki bayan Sameeha ni take rufawa asiri take zaune dani nakassashe, ban faɗa muku ba ta hana ma na sanar da kowa, bayan na saketa kika nuna kinfi kowa murna kika je kika ci musu mutunci kika kwaso yara, kika dage akan sai nayi aure na amsa miki domin na nuna miki kinyi kuskure dan nasan ni ba mai lafiya bace, babu macen da zata zauna dani a haka, amma saboda ki muzgunawa Sameeha kika haɗa baki da 'yar uwarta Najwa kika fitar da Sameeha a gidanta sannan kika aura mini Najwa dan kwai ki kai Sameeha ƙasa saboda kin tsaneta, to ni kika tsana ba ita ba, nine baki so nine kikewa hassada da baƙin ciki Hauwa, to Albishirinki zan bar miki duniyar kici abinda zaki ci a ciki, kuma na saki Najwa domin bazan yarda na zauna da ita a matsayin auren cin amana ba, babban farin cikin da nake ji inna tuna an saki Adama 'yarki saki uku lokaci ɗaya kamar yadda na saki Sameeha, Allah ya nuna miki cewar shi ba azzalumin bawansa bane sai dai bawa ya zalunci kansa, kuma alhaki kuikuiyo ne gashi ya biki, ita kuwa Sameeha ta samu mijin daya fini, 'yan uwan da suka fiku inda ake yi musu so domin Allah, tana cikin farin ciki da ahalinta Allah bai bari sun wulaƙanta ba ya ɗagasu ya ɗaukaka daraja su wanda sai dai gani sai hange, wannan izina ce a gareki dama duk mai irin halinki kuma ki saka a ranki ɗan uwanki Aminu ya mutu wannan da yake a gabanki wani ne sabo bai sanki ba, ban san daga ina kike ba, Allah ya isa tsakanina dake.
Ya ƙare maganar yana nuna ta da tsaya duk ya haɗa guimi saboda masifar da yayi, Hauwa kuka kawai take yi cike da tsantsar bakin cikin abinda Aminu yayi mata, ya wulaƙantata a gaban dangi, ya tona mata asirin mutuwar auren 'yarta da suke ta rufa rufa yanzu kowa yasan saki uku aka yi mata wanda a dalilin aurensa ne aka sakeleta. Mutane kam jugum jugum suka yi suna jin abin mamaki, musamman da Aminu ya faɗi rashin lafiyarsa, sunyi matuƙar tausaya masa, waɗanda basu san halin Hauwa ba yau sun sani sai um um da baki suke yi kowa yana tsoron furta nashi sanin halinta ta balbalesu da faɗa, duk da Aminu ma yayi mata hukunci harda fasa baki. Yaya Kamalu da Alhasan sun fito suma sunji komai da kunnensu, ba ƙaramin mamaki kalaman Aminu ya basu ba musamman na rashin lafiyarsa da kuma Najwa 'yar uwar Sameeha ce, basu ga laifin dukan Hauwa da yayi ba dan ita taja ta kuma zubar da girmanta, Aminu ya juya a fusace zai fita Alhasan ya kira sunansa sai ya juya, Aminu ya fashe da kuka ya isa gurinsa ya ɗaura kansa a kafaɗar Alhasan shi kuma yana dukan bayansa akan yayi hakuri, Aminu ya ɗago yana nuna musu Hauwa.
Kunganta ita ce gabaɗaya ta rusa mini rayuwata, duk da na yarda da ƙaddara amma itace sila.
Yana gama faɗar haka ya juya ya fice daga gidan yana share hawayensa, su Alhasan basu hanashi ba domin yana buƙatar kaɗaici, kallon Hauwa suke yi zaune a ƙasa sai suka danƙara mata mugun kallo kana Alhasan yayi waje Kamalu ma yabi bayansa, koda suka fita sai dai suka tadda kurar motar Aminu dan tuni yayi gaba abinsa, nan suka zauna ƙofar gida suna mayar da magana dan sosai suma suka ji kamar su rufe Hauwa da duka, suma banda a tsaye suke da haka zata tasa rayuwarsu a gaba dan Hauwa tana da mugun sa ido da shiga harkan da ba nata ba. Hauwa kuwa miƙewa tayi jiki a sanyaye ta wuce sashin Laure duk abin duniya ya dameta, domin wulaƙantata da Aminu yayi a bainan nasi ya tsaya mata a rai matuƙa, ga kuma tona sakin da aka yiwa 'yarta, ji tayi idan bata rama abinda yayi mata ba bata haifu ba, sai ta saka rayuwarsa a uku masifa ta yadda sai yazo akan guiwarta yana bata haƙurin abinda ya aikata mata, dan wlh idan zata ja duwawu ne sai ta lalata dukiyarsa dama duk wani abu daya ke taƙamata dashi, girgiza kai kawai take yi tana cizon leɓenta da ƙan8ance idanunta, tana jin su Laure suna bata haƙuri amma bata su take ba dan alwashin sai Aminu ya wulaƙanta take a zuciyarta.
******
Najwa.
Suna shiga gida ta wuce É—akinta tana kuka, Junaid ya shiga É—akinsa shima ya ciro belt É—insa ya sameta a É—akin ya shiga dukanta yana cewa.
Wlh idan ban dukeki ba bazan huce takaicin baƙin ciki da kika ƙunsa mana ba, kinci mutuncin gidanmu kin ɓata manq sunanmu, shegiya mai mugun hali Allah ya wadaranki Najwa.
Yaya ka kashe! nima na huta na tsani komai bana son wannan rayuwar ka kashe!
Najwa tana faÉ—a cikin gunjin kuka tana kuma sosa jikinta da dukan da yake yi mata, sauran 'yan biki ne suka shigo É—akin suka ceci Najwa, Salima ta wanke Junaid da mari tana zaginsa.
Dan ubanka kasheta zaka yi, ka bari muji da abu É—aya mana, ace jiya jiya aka É—aura aure an sakota kazo kuma zana dukanta da wannan zata ji.
[7/7, 13:04] BuhainatðŸ˜: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*
46.
Aminu.
Bayan ya sayowa yara kayan ciye ciye sai ya shiga mota ya wuce zuwa babban gida dan so yake yau Hauwa ta gane kuranta, yana tafiya yana duban a gogo wanda ya nuna kusan goma da mintuna yasan sun ɓata lokaci sosai a gidan umma, sai ya ji zuciyarsa fes kamar ya sauke wani mai nauyi, na farko ya wanke Sameeha ya kuma bata yaransu sannan kuma ya rabu da Najwa da yake jinsa kamar an ɗaura masa ƙarfe a wiya, yanzu ya zama free sai kuma ya mayar da hankalinta kan batun aikinsa, da farko da aka yi masa tayin aikin yaƙi amsa saboda yaransa da suke hannunsa, yaji ba zai iya barin mahaifarsa ba gwara a ɗaura wani akan tafiya London ɗin, su kuma sun fi so shi ya yi tafiyar domin sun san ba zai basu kunya ba, yafi ƙarfin wata da suke ta binsa da wannan maganar dan har bashi lokaci suka yi akan wataƙila ya sauta ra'ayinsa,sai gashi kuma cikin yardan Allah ya amsa musu da zai yi tafiyar ɗazun da safe ya kiransu, dan yana so yayi nesa da kowa ya yi rayuwa a inda ba wanda ya sanshi, kuma yana so ya mayar da hankalinsa wajen niman lafiya a can ƙila ya dace ya samu lafiyar, da tunani barkatai ya isa babban gida yayi parking a ƙofar gate ya fito ya shiga gidan, ya samu mata da yara ana ta hayaniya da alama basu daɗe da gama karyawa dan yaga kofuna da robobin na suka ci ƙosar birjik a tsakar gida, matan da suka fara ganinsa suka fara sakin guda suna ga Ango ga Ango, Aminu kam murmushin takaici yake yi yana gaishe su, a tsakar gidan ya tsaya ya tambayi Salma data fito daga ɗakin Sa'a ina Hauwa ta kira masa ita, tace masa to kana ta isa shashin Laure ta faɗa mata saƙon Aminu sai cewa tayi ta dawo tace masa ya zo sashin Laure, Aminu ya yi guntun murmushi ya ce.
Ki ce mata ta fito tsakar gidan sauri nake yi.
Salma ta koma ta faɗa mata sai gata tazo buguzum buguzum ta ƙaraso tana cewa.
Haba Ango saurin me kake yi ko amarya tayi ce kira. To gani ya kwanan amarya fatan ka yaba da zaɓina.
Ta ƙare maganar tana tsayawa a gabansa.
Aminu ya kalleta ido cikin ido yana cewa.
Gaskiya kam na yaba da zaɓinki wanda kika saka son zuciya a ciki da son kai, ban ɗauka tsanar da kika yiwa Sameeha har ya kai haka ba, ki rasa wacce zaki aura mini sai 'yar uwarta saboda kawai ki muzguna mata.
Haba Aminu meye laifina dan na zaɓa maka matar da zata share maka hawaye ta kula da kai, yarinya mahaddaciya mai tarbiyya kuma.
Bata rufe baki ba ya daga hannu ya wanka mata lafiyayyen mari kafin ta dawo dai dai ya ƙara marinta a ɗayan kuncin, a gigice Hauwa ta dafe duka kuncinta tana kallonsa a razane idonta a warwaje cike da tsantsar mamaki da tsoro tace.
Ni ka mara Aminu daga abun arziki, in yi maka fari ni kayi mini baƙi, ko dai su Sameeha sun bi boka da malamai sun sauya maka tunani.
Bata rufe baki ba ya dunƙula hannu ya nausa mata a baki wanda nan take bakin ya fashe ya soma jini, Hauwa ta tsandara ihu ta baje a ƙasa tana cewa.
Shikenan sun rabani da É—an uwana innalillahi wa inna ilaihir raji'un, Aminu ni kake duka ina matsayin yayarka.
Aminu ya daka mata uwar tsawa wanda yasa mutane duk suka taru akansu, waÉ—anda suke nesa ma da basu san ana yi ba suka matso.
Yayar banza yayar wofi muguwa azzaluma shaiɗaiya, idan sunan Sameeha bai fita daga bakinki ba wlh sai ba kasheki in yaso nima a kasheni. Kin tarwatsa mini farin ciki na da ni da iyalina, Hauwa kin zame mini matsala a rayuwata. Kece kika saka na rasa lafiyata wanda ya jawo dalilin dana rabu da mata ta, tun lokacin da kika kirani kika fana mini rasuwar Umma nayi accident a lokacin na rasa mazantakata na rasa lafiyar da zan kusanci matata, tsawon shekara shida Sameeha tayi dani tana haƙuri ba tare dana sauke hakkin aurenta ba, bayan mun dawo Kaduna kika matsa mata kika dinga yi mata bita da ƙulli duk saboda son zuciyarki bayan Sameeha ni take rufawa asiri take zaune dani nakassashe, ban faɗa muku ba ta hana ma na sanar da kowa, bayan na saketa kika nuna kinfi kowa murna kika je kika ci musu mutunci kika kwaso yara, kika dage akan sai nayi aure na amsa miki domin na nuna miki kinyi kuskure dan nasan ni ba mai lafiya bace, babu macen da zata zauna dani a haka, amma saboda ki muzgunawa Sameeha kika haɗa baki da 'yar uwarta Najwa kika fitar da Sameeha a gidanta sannan kika aura mini Najwa dan kwai ki kai Sameeha ƙasa saboda kin tsaneta, to ni kika tsana ba ita ba, nine baki so nine kikewa hassada da baƙin ciki Hauwa, to Albishirinki zan bar miki duniyar kici abinda zaki ci a ciki, kuma na saki Najwa domin bazan yarda na zauna da ita a matsayin auren cin amana ba, babban farin cikin da nake ji inna tuna an saki Adama 'yarki saki uku lokaci ɗaya kamar yadda na saki Sameeha, Allah ya nuna miki cewar shi ba azzalumin bawansa bane sai dai bawa ya zalunci kansa, kuma alhaki kuikuiyo ne gashi ya biki, ita kuwa Sameeha ta samu mijin daya fini, 'yan uwan da suka fiku inda ake yi musu so domin Allah, tana cikin farin ciki da ahalinta Allah bai bari sun wulaƙanta ba ya ɗagasu ya ɗaukaka daraja su wanda sai dai gani sai hange, wannan izina ce a gareki dama duk mai irin halinki kuma ki saka a ranki ɗan uwanki Aminu ya mutu wannan da yake a gabanki wani ne sabo bai sanki ba, ban san daga ina kike ba, Allah ya isa tsakanina dake.
Ya ƙare maganar yana nuna ta da tsaya duk ya haɗa guimi saboda masifar da yayi, Hauwa kuka kawai take yi cike da tsantsar bakin cikin abinda Aminu yayi mata, ya wulaƙantata a gaban dangi, ya tona mata asirin mutuwar auren 'yarta da suke ta rufa rufa yanzu kowa yasan saki uku aka yi mata wanda a dalilin aurensa ne aka sakeleta. Mutane kam jugum jugum suka yi suna jin abin mamaki, musamman da Aminu ya faɗi rashin lafiyarsa, sunyi matuƙar tausaya masa, waɗanda basu san halin Hauwa ba yau sun sani sai um um da baki suke yi kowa yana tsoron furta nashi sanin halinta ta balbalesu da faɗa, duk da Aminu ma yayi mata hukunci harda fasa baki. Yaya Kamalu da Alhasan sun fito suma sunji komai da kunnensu, ba ƙaramin mamaki kalaman Aminu ya basu ba musamman na rashin lafiyarsa da kuma Najwa 'yar uwar Sameeha ce, basu ga laifin dukan Hauwa da yayi ba dan ita taja ta kuma zubar da girmanta, Aminu ya juya a fusace zai fita Alhasan ya kira sunansa sai ya juya, Aminu ya fashe da kuka ya isa gurinsa ya ɗaura kansa a kafaɗar Alhasan shi kuma yana dukan bayansa akan yayi hakuri, Aminu ya ɗago yana nuna musu Hauwa.
Kunganta ita ce gabaɗaya ta rusa mini rayuwata, duk da na yarda da ƙaddara amma itace sila.
Yana gama faɗar haka ya juya ya fice daga gidan yana share hawayensa, su Alhasan basu hanashi ba domin yana buƙatar kaɗaici, kallon Hauwa suke yi zaune a ƙasa sai suka danƙara mata mugun kallo kana Alhasan yayi waje Kamalu ma yabi bayansa, koda suka fita sai dai suka tadda kurar motar Aminu dan tuni yayi gaba abinsa, nan suka zauna ƙofar gida suna mayar da magana dan sosai suma suka ji kamar su rufe Hauwa da duka, suma banda a tsaye suke da haka zata tasa rayuwarsu a gaba dan Hauwa tana da mugun sa ido da shiga harkan da ba nata ba. Hauwa kuwa miƙewa tayi jiki a sanyaye ta wuce sashin Laure duk abin duniya ya dameta, domin wulaƙantata da Aminu yayi a bainan nasi ya tsaya mata a rai matuƙa, ga kuma tona sakin da aka yiwa 'yarta, ji tayi idan bata rama abinda yayi mata ba bata haifu ba, sai ta saka rayuwarsa a uku masifa ta yadda sai yazo akan guiwarta yana bata haƙurin abinda ya aikata mata, dan wlh idan zata ja duwawu ne sai ta lalata dukiyarsa dama duk wani abu daya ke taƙamata dashi, girgiza kai kawai take yi tana cizon leɓenta da ƙan8ance idanunta, tana jin su Laure suna bata haƙuri amma bata su take ba dan alwashin sai Aminu ya wulaƙanta take a zuciyarta.
******
Najwa.
Suna shiga gida ta wuce É—akinta tana kuka, Junaid ya shiga É—akinsa shima ya ciro belt É—insa ya sameta a É—akin ya shiga dukanta yana cewa.
Wlh idan ban dukeki ba bazan huce takaicin baƙin ciki da kika ƙunsa mana ba, kinci mutuncin gidanmu kin ɓata manq sunanmu, shegiya mai mugun hali Allah ya wadaranki Najwa.
Yaya ka kashe! nima na huta na tsani komai bana son wannan rayuwar ka kashe!
Najwa tana faÉ—a cikin gunjin kuka tana kuma sosa jikinta da dukan da yake yi mata, sauran 'yan biki ne suka shigo É—akin suka ceci Najwa, Salima ta wanke Junaid da mari tana zaginsa.
Dan ubanka kasheta zaka yi, ka bari muji da abu É—aya mana, ace jiya jiya aka É—aura aure an sakota kazo kuma zana dukanta da wannan zata ji.