← Book details Abin Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 75 OF 98

Sashe 75

Abin Da Ciwo Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Junaid ƙofa yayi ya fice abinsa ransa a matuƙar ɓace, Salima tabiyo bayansa ta tsaya a tsakar gida.

Wlh babu wanda ya isa ya ƙara dukanta idan baku sonta ni ina sonta, haka kawai da wanne zata ji? Ai kowa ma yana kuskure sai ayi mata uzuri, dan haka yau ɗin nan zan tafi da ita kano ta cigaba da zama a guna ba zaku ƙara ganinta ba sai kun nimeta.

Da kin kyauta kuwa Salima, kinga kin sauƙaƙa mana baƙin cikin da ta ƙunsa mana bamu ganta ba balle mu riƙa tuna abinda ta aikata, sannan ma kin rage mana zagin mutanen unguwa, in dai Najwa ce na yafe miki ita ba kano ba ki wuce kano da, ita ai dama ba a ɗaya a dangi, na tabbatar idan Najwa tayi gadon mugun hali to kuwa a gunki ta gado shi, dan kema babu irin surutun da baki saka iyayenmu ba har suka bar duniya da tabonki.

Dama ai da abu ya taso saika goranta mini kuma su Mama basu bar duniya ba saida suka yafe mini komai, aure ne dai naƙi zamansa kuma yanzu Allah ya shieyeni ina zaune a gidan aure har da yara, abu ya wuce amma kullun sai ka dawo da magana baya, ni ba cikin shege nayi ba ko wani mugun abu, aure ne dai naƙi zamansa nayi har guda Huɗu, a na biyar ne na zauna kuma bazan zauna namiji yana cuta mini ba, ko yanzu baban su Lukuman ya yi mini iskanci zan cikawa wandona iska bazan zauna ba wlh.

Allah ya kyauta. Dan haka ni na sallami kowa biki ta watse kowa ya zo ya kama gabansa tunda me auren ma an sakota saboda mugun halinta.

Baba ya kuma faɗa ya fice daga gidan, nan fa sauran 'yan uwa kowa ya fara haɗa kaya, inna kuwa tunda ta kwanta a gado ta rufe ido bata motsa ba kuma bata son yin magana, tana jin abinda ya wakata da baba da Saleema saida tayi murmushin takaici dan kuwa baba Gaskiya ya faɗa Najwa halinta ta ɗauko dama ba a ɗaya a dangi, ga shegen son duniya da rayuwar ƙarya, haka ta gama zaga gidajen aure huɗu wanda kowa yasan arzikinsu take bi in taga bata samu yadda take so tasa miji ya saketa dole, wannan ne kawai ta zauna dan shima malami ne wataƙila wajen niman asiri ya ganta ya kuma maƙale mata saida ya aureta, daga bisani ma ya kafeta ya mallaketa shiyasa ta kasa kwakkwaran motsi a gidan dan mugun tsoronsa ma take ji, inna taji daɗin ma ta tafi da Najwa wataƙila malamin zai koya mata hankali ita ma ta dawo hayyacinta, dan zata saka baba ya kirashi ya faɗa masa komai ta yadda Najwa sai ta so dawowa nan kuma ba halin haka, sannan ya aurata mata duk wanda ya gadama zata so hakan ya faru.
[7/7, 13:04] Buhainat😁: *Littafin nan na kudi ne, don Allah da son annabi ku karfafa min guiwa, duk wanda ya ga wannan littafin ya siya result karanta domin hakkina ne. Pay N400 to 0106956864 Ramatu Muhammad Kabir Access bank (Diamond). Ko a biya a POS, ko a tura MTN card N400 a 09034940106, masu so ta pc su tura N700. Sai a tura shai wanidar biya ta number 09034940106. Dan Allah banda vtu.*

47.

Najwa tunda taji Anty Saleema tace zata je da ita kano sai taji ɗan sanyi a ranta, dan yanzu abinda tafi so shine tayi nesa da inda take da kowa ma ƙila hakan zai saka ta samu sassauci daga halin da take ciki, sai kawai ta miƙe cikin zafin nama duk da tsamin da jikinta yayi na dukan jiya da yau, amma haka ta soma haɗa kayanta dan ko kayan akwatinta a yanzu bata buƙatarsu, kuma kayanta na gida ba a riga an kai mata ba dan haka cikin ƙanƙanin lokaci ta gama komai ta zura babban hijab ɗinta ta saka safa da niƙaf dan so take tayi ɓadda kama yadda babu wanda zai ganeta saboda tana kunyar mutane su ganta kar suyi mata dariya, a dalilin aurenta ta wulaƙanta mutane da yawa ta rabu da ƙawayenta na kan layinsu da yawa a ganinta ta wuce hulɗa da ƙananun mutane, ta jawo trolley ɗin kayanta tsakar gida ta tsaya tare da ɗaga niƙaf ɗinta ta rungume hannu tana jiran fitowar Saleema dan tasan ba zata ƙara kwana a gidan ba saboda itama akwai zuciya, ilai fitowarta da minti goma sai gata ta fito da jakar kayanta tana kwalawa inna kira akan ita zata wuce, ganin Najwa a tsaye da shirin tafiya yasa ta saki murmushi.

Kunga 'yar halak harta kimtsa, aiko dama yanzu nake shirin yi miki magana ki shirya ashe harma kin fini zaƙuwar mu tafi, to In Sha Allah alkhairinki yana Kano sai mutane sunga irin wanda zaki aura, yadda kike da kyau da hasken fata mazan Kano ba ƙaramar ƙaunar farar mace suke yi ba.

Hmmm ayi dai mu gani in tusa zata hura wuta, ni sai dai nayi muku fatan ku sauka lafiya amma in har Najwa bata sauya halinta ba to wlh kema sai ta gundureki. Najwa ina miki faran shiriya kuma In Sha Allah addu'ata kenan kullun dan hannu bai taɓa ruɓewa ka yanke ka yar, Saleema ki gaida maigidanki da abokan zamanki.

Cewar inna data fito daga ɗaki cike da ƙarfin guiwa dan ba ƙaramar farin cikin tafiya da Najwa tayi ba, Saleema ta taɓe baki tana cewa.

Ai dama nasan bakinki É—aya da yaya, ko min abinku Najwa dai In Sha Allah sai ta zama zakaran gwajin dafi.

To saleema ai banyi miki musu ba Allah ya sauke ku lafiya.

Inna ta faɗa tana wucewa gurin kitchen dan ta ɗauki kofin Baba da aka wanke. Saleema bata ce komai ba ta gyara mazaunin gyalenta ta yi gaba Najwa ta sauke niƙaf ɗinta ta bi bayanta da trolley suka fice daga gidan, suna fita sauran 'yan uwa suka shiga zancen tafiyarsu Inna tana ji bata saka baki ba dan fatanta ma kowa ya watse ya bar mata gida ko zata shaƙi iska mai daɗi saboda abinda ya faru har yanzu baisa ta samu natsuwa mai kyau ba.

Najwa suna fita suka samu napep ya wuce dasu tasha ba ɓata lokaci suka samu motar Kano suka shiga, Saleema ta biya kuɗin, mota tana cika suka kama hanya, sai a lokacin ne Najwa ta soma fidda zafafan hawaye taji duniyar ta yi mata kamun kazar kuku, tana gani ta rasa komai duk wani burinta ya ƙare a lokaci guda, dana sanin yadda ta kamu da son Aminu ta soma yi, ba wai dan tayi nadama ba sai dan dana sanin akan baida lafiyar da zai iya ɗauke nauyin duk Sha'awarta data jima tana yi akansa, ashe duk wani tanadi data yi masa aikin banza tayi, ji take duk abinda ya sameta Sameeha ce sila da bata dawo taje gidanta ba da duk haka bai faru ba, shiyasa take jin itace babbar maƙiyiyarta sai Ikram sannan Aminu da kuma Nafeesa data faɗo mata a rai, nan take ma ta tuna da tona mata asirin da tace zata yi domin tana so yadda ta rasa komai ta muzanta to itama Nafeesa ta shiga halin ƙunci, domin itama ta taka muhimmiyar rawa wajen sata yin wasu abubuwan, sai kuma su Binafa da suma ta yi alwashin tona musu asiri kowa kwaɓarsa sai tayi ruwa, a sannan ne ta saki murmushi wanda yake cike da tarin mugunta, ta ciro wayarta dake jaka sai ta tuna da ta ci screen, sai ta kalli Saleema tana cewa.

Anty dan Allah ara mini wayarki akwai abinda nake son tura wa yanzu.

Ba musu ta ciro wayar a jaka ta bata, Najwa ta saka sabon sim ɗin data yiwa Ikram text lokacin bikinta a wayar Saleema, sai ta kunna data ta sauya WhatsApp ɗin Saleema ta mayar da nata Number ɗin, dama duk numbers ɗin da take so tayi savimg a nan, dan haka cikin kankanin lokaci ta rubuta saƙo kamar haka ta turawa number ɗin yayan Nafeesa da take cewa.

Ɗan uwa ina son in sanar da kai wani lamari wanda nake fatan mu samu masalaha a cikinta, nine Saurayin Nafeesa wanda muka samu matsala da ita muka rabu, dalilin akwai wani sirri da muka rufe wanda ya dameni sosai shiyasa na buƙaci na sanar da kai ko hakan zai sa mu samu maslaha. A lokacin da take zuwa Poly wani tsautsayi ya faɗa a tsakaninmu har na kusanceta sai kuma ciki ya samu, to gaskiya na shiga damuwa sosai wanda yasa nace dole sai an zubar saboda mu rufawa kanmu asiri, to shine ta samu cousin ɗinku Binafa suka san yadda suka yi aka zubar da ciki sai asirinmu ya rufu, daga nan kuma muka cigaba da mu'amalarmu amma tana yin planning yadda ciki bai sake samuwa ba. Ita Binafa ta rufa mana asiri muma mun rufa mata saboda munyi ban gishiri ne in baka manda, domin itama cikakkiyar 'yar lesbian ce wacce har aure tayi da wata ƙawarta Hanan a ɓoye, abubuwa dai da yawa sun faru kuma suna kan faruwa, to gaskiya wannan dalilin yasa naji bazan iya auren Nafeesa ba saboda zargi da ya shiga tsakanimu, amma bayan 'yan kwana biyu naji sam banyi mata adalci ba dana rabu da ita sai dai bazan iya cigaba da ɓoye wannan sirrin ba dole sai na fito na faɗa, wataƙila zamu samu maslaha ku yafe mini.

Ta tura masa dan dama a ranar da aka kaita kafin ta yiwa Nafeesa magana lokacin da zata cire sim ɗinta ta ɗauki number ɗinsa a wayar Nafeesa tayi saving a ƙaramar wayarta. Najwa nan take taga yayi marking sai ta kashe data ta shiga hotunan Saleema tana kallo tana jin farin ciki a zuciyarta na tona musu asiri.

Bayan awa guda ta ƙara kunna data sai ga sakon yayan Nafeesa kamar haka.

Innalillahi wa inna ilaihir raji'un. Amma Hamisu kaci amana bamu zaci haka daga gareka ba, ai ko tunda abinda ya faru kenan dole ma ka aureta dan baka isa ka ɓatatq ba kace zaka rabu da ita, yanzu ina hanyar zuwa gida za ayi duk wacce za a yi ma.
Chapter 75 · 0% Book details