← Book details So Ne Ko Kiyayya Part 1 Complete Hausa Novel. Local reading mode
READING PART 51 OF 65

Sashe 51

So Ne Ko Kiyayya Part 1 Complete Hausa Novel. · about 9 min read

Eh ita"Eh tana ciki Angama mata lallen nata tun d'azun"beyi mgn ba yatura k'ofar ya shiga yabar musu daddad'an k'amshin turarensa"nafeesa ce cikin parlourn da wasu tsaffi su biyu sai d'ayyaba dake cin Abinci"tana kallonsa tana murmushi tace"yaya Aliyu Ango"hararanta yayi beyi mgn ba"ta gaidashi tana fad'in garama da Allah yakawoka"hjy ta kafe ta hana Amaryar mu tayi wanka a toilet d'inta"gata can a bed room d'inta nafeesa ta rik'e hjy In'am d'in zata shiga"tab'e baki yayi yace"kai hjy fitinar ta sai ita"ita kuma my Angel in bacin rigima basai taje ko part d'in umma ko mommy tayi wankan ba??"wlh dukda mutane ko ina"kuma da kunya kasan iyayen namu mutan dane"balle yanzun jere za'a tafi ga wa'azi daza'ayi da k'arfe 4"duk gidan cike da mutane yake"beyi mgn ba fuska Ad'aure yanufi bed room d'in hajiyar....can k'asan mak'oshi yayi sallama ya shigo"nafeesa na rik'e da hannayen hjy"In'am na tsaye Adaidai bakin k'ofar shiga bath room d'in"tana d'aure da towel iya gwiwa sai hijab itama iya gwiwa Ajikinta "lallen da aka mata ja da bak'i yayi shar gwanin kyau da ban sha'awa"Abinka da farar mace"ga dilkan da Aka musu yasaka ta k'ara mugun haske da shek'i"har yellow yellow takeyi"fatar jikinta tayi taushi da sulbi tana d'aukar ido"ga wani irin k'amshi daya zauna Ajikinta"wanda tunda me tubarau ya shigo cikin d'akin k'amshin ke dukan hancinsa"tunda ya shigo ya tsurawa In'am ido"tun dg yatsun k'afarta har zuwa baby face nata yakebi da wani irin mayen kallo"In'am kuwa tunda taji k'amshin turarensa gabanta yabuga! ta dake tak'i kallonsa tana jin nafeesa na Amsa sallamarsa ta gaidashi....ke cikata! yafad'a yana kallon nafeesa cikin dakiya"dan gaba d'aya tunda yayi tozali da in'am yarasa nutsuwarsa"madallah da Allah yakawoka"gaskiya muddin sulaiman shine zai Auri nafeesa tofa yaAuri matsala"kanafa gani yarinyar nan sbd ta k'untata mani ta gayyato me lalle Akazo nan Aka musu sbd Acuceni Ab'atan sashe"shin dannace wannan yarinya maryam bazata min wanka nan ba sai Aga laifina fisabilillahi??"yanzun hjy matar tawa zaki hana ta shiga tayi wankan??"yafad'a ko Ajikinsa"In'am dai tayi k'asa da kanta dan jikinta yabata kallonta yakeyi.....yanzun tun kafin Ad'aura Auren kake cewa matarka?"lallai bakada ta ido"yanzun ma fisabilillahi bakayi mata girmaba"dama duk wannan miskilancin da kakeyi wannan itace kakeso ??"d'aure fuska yayi yace"hjy ki barni da wata mgn can taki"maryam wuce ki shiga kiyi wanka"In'am kasa mgn tayi"hjy ta tab'e baki tace"kajita in kasanta wlh"Ace y'ar cikinka zaka Aura.... murmushi ya sub'ucewa yaya Aliyu beyi mgn yamatso gaban hjy yana fad'in my sweet Granny kenan"kin manta jikatace ita ba y'ar cikina ba"nasan kishine ke damunki sai kuma kiyi hak'uri"yafad'a yana k'ok'arin rik'e mata hannu"In'am tayi wuf ta shige bath room d'in ta maido k'ofar ta rufe"cikani kona tsine maka Albarka lallataccen banza"cewar hjy cikin masifa tana k'ank'ance ido"nafeesa ta duk'e ta dinga bab'b'aka dariya"shima yaya Aliyu beyi mgn ba yacikata yabar d'akin yana jin tanata zage zage"bayan fitarsa hjy ta harari nafeesa tana fad'in binta kika kallah kina dariya"ita kuma y'ar nema zata fito ta sameni"shiru nafeesa tayi tana jiran In'am ta fito itama ta shiga"In'am kuwa tajima Aciki sannan ta fito"ta sami hjy kwance samqn bed tana gyangyad'i"nafeesa tayi wuf ta shige"k'ofar d'akin in'am ta sakama key sannan ta d'auki ledar kayanta tafara shiryawa"Acikin jallabiya bak'a y'ar saudiyya me zanen brown da Adon stones ta shirya"ba k'aramin karb'an ta kayan sukayi ba"tanata zuba k'amshi"powder da kwalli da lipgloss kawai ta shafa Amma fad'in kyawun datayi b'ata bakine"sallar la'asar tayi dan har 3:30 tayi"tana cikin sallar nafeesa ta fito itama ta shirya cikin irin kayan da in'am tasaka"lokacin har baccin hjy yayi nisa"sai wajen 4 sannan suka koma part d'in ummi sbd can k'awayensu keta zuwa"sai wajen k'arfe 5 na yamma Aka fara gudanar da wa'azin"wanda maudu'i 3 Aka d'akko Ana bayani kansa"na farko"mahinmanci tsabta ga rayuwar y'a mace"sai Abu na biyu biyayya ga miji da sauke nauyinsa dake wuyan y'a mace"sai kuma Abu na k'arshe ibada da iya girki"wanda wa'azin ba k'aramin tasiri yayi Azuk'atan Amaren da sauran mutane dake sauraro ba...da wannan taro yatashi lafiya"
washe gari misalin k'arfe 7:11 pm"tun farkon shiga layin Anguwar nassarawa har zuwa cikinta"manya manyan motocine na Alfarma"wasu na shiga wasu na fita"wasuma Ak'afa suke tafiyar ko kan mashin"duk y'an matan sun cakare cikin Ankon farin leshi da head maroon"sbd yau Akeyin dinner.....wata had'add'iyar farar motace ta shigo cikin layin Aguje"wacce koba'a fad'a ba kasan motar Amare ce"brr Ahmed da tasleem na gidan gaba"itama tasha Ankon ta tana rik'e da babaynsu dake da 4 month yanzun"babban Abokin Ango shima yasha farar shadda"sbd dama Ankone"maza farar shadda mata farin leshi"back sit na kallah" nace wow masha Allah"
!dr Aliyu me tubarau na zaune yasha zazzafan wanka na suit bak'ak'e sabbi dal"yama jikinsa wanka da turare"sumar nan zuwa lallausan bak'in zagayayyen sajen sa sunsha gyara har salk'i da d'aukar ido sukeyi"kallo d'aya zaka masa kasan Angone"duk yadda yake beda fara'a sosai"Amma yau farin cikin dayakeji be b'oyewa dukda gobe ne za'a d'aura Auren"cikin nutsuwa ya bud'e k'ofar motar yafito"ya hango yesmeen tasha gayunta suna tsaye da yaya mukhtar suna mgn"da Alama sonta yakeyi"yaya Aliyu na k'ok'arin yi mata mgn In'am da k'awayensu da nafeesa suka fito dg cikin get d'in gidan ummi"sunsha Areviat gownt fara"kowace tasha make up na zamani"sunyi kyau har sun gaji"kowa fad'in masha Allah yakeyi"tun dg nesa me tubarau ke Aikowa da in'am da tattausan murmushi"ta d'ago kanta tana satar kallon gefen dayake zaune"ya Ida isowa gefenta be kalli ko wace yarinya ba yaja hannunta yana fad'in zo muje my Angel kar Ayi latti"sauran friends naku su shiga ga motoci nan"kasa mgn tayi sbd yadda yaya Aliyu ke murza tafin hannunta dake cikin nasa A cikin wani irin salo"yayinda shima yaya sulaiman ya iso cikin irin suit irin na yaya Aliyu yaja tashi Amaryar suka shige mota.....yaya Aliyu kuwa In'am yafara b'udema motar ta shiga sannan shima ya shiga ya zauna gab da ita"jikinsu na gugar juna"tayi k'ok'arin matsawa lokacin da brr Ahmed ke bama motar wuta"shima koma matsowar yayi murya can k'asa yace"my Angel kinyi kyau sosai"uhmm ina wuni?"Alhamdllh" saidai kewar kice kawai ta dameni"sbd ni yasaka wayarki kashe Acikin kwanakin nan ko?"to Ai duk wani guje guje ki gama gobene za'a d'aura ko?"kasa mgn tayi k'irjinta na bugawa.....hannunsa guda ya Aza samqn nata yanufi bakinsa dashi ya sumbaci bayan hannunta....saida taji tsikar jikinta ta tashi musammun yadda sajen fuskarsa yasoki tafin hannun nata"my Angel"uhmm! meyasa kike guduna baki yarda muna had'uwa dake??"bbu komai fa yaya"ta fad'a yadda shine kawai zai iya ji"shiru yayi be koma mgn yana kallon titi "jefi jefi kuma yana Amsa wayar mutane"da haka suka iso wajen dinner d'in"wajen yacika da mutane Anata hayaniya"yaya Aliyu yatab'e baki sbd beson hayaniya"sai sannan in'am tace"yaya Ahmed ina wuninku??"lafiya qlau Amaryar mu"Ai na d'auka sai mun siyi baki kiyi mgn?"yafad'a yana dariyar tsokana suka fito shida tasleem"yayinda In'am batayi mgn ba"my Angel mu fita ko?"make up d'in nan yayi yawa ga gashin kanki Anfito mun dashi waje"kayi hak'uri yaya Abune nad'an lokaci Ayi Agama fa"hakane Amma sai naga kamar bakison Auren ko?"bafa haka bane"to fad'amun naji kina son Auren??"yafad'a cikin wata iriyar muryar da bata sanshi da itaba"kukan shagwab'a ta saka tak'i mgn"yayi murmushi yabud'e k'ofar motar suka fito"matsowa yayi yasak'alo hannunsa Agefen k'ugunta"wanda hakan yayi daidai da isowar marok'a wajen"da tauwagar danginsu irinsu"Auwal da mahmood da Abdulhakeem,da yasmeen da yaya mukhtar da yaya yusuf"da brr Ahmed da wasu Abokan yaya Aliyu suka fara yi musu lik'i da y'an 1k da y'an 500"yaya Aliyu baki yak'i rufuwa"ita kanta in'am taji dad'in Abun Aranta"sai murmushi takeyi....tun dg bakin motar ake musu lik'i har suka shiga cikin hall d'in suka zauna"wak'okin music masu dad'i natashi"bayan sun zauna saiga nafeesa da yaya sulaiman da isma'il da zainab suma Anata
musu lik'i har suka zauna"bayan MC yayiwa couples d'in sannu da zuwa yagabatar da Abinda yatara su Awajen"sannan yabukaci duk sutaso su yanka cake"bayan kowane ya yanka shida Amaryar sa"Aka fara pics da vedio"dg bisani duk couples d'in suka fito tsakar filin suna rawa"Aranar fans d'in SONE KO K'IYAYYA sunyiwa me tubarau da In'am k'ara ba kad'an ba"dan ba k'aramin barin kud'i suka yiba musammun maman noor...lolx
sai wajen k'arfe 11 pm taro yatashi lafiya kowa yabaro wajen Agajiye....motar brr Ahmed na gama parking"In'am dama ready take"da hanzari tayi wuf ta fice"shi yaya Aliyu ma dariya tabashi"yakuma gane dalilinta na wannan gudun nasa datakeyi"fitowa yayi shima Agajiye"bebi takan tsokanar da brr Ahmed ke masaba sukayi sallama yawuce gida"sbd ya d'auki motarsa ya wuce gidansa shida In'am dake jan bulo"dan tun jiya yakwashe komai nasa yamayar Acan....
washe gari
.wannan book d'in nakudine idan kina buk'atar siya serious normal grp 300
Vip grp 1000
via 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
Ki turo shaidar biyanki ta what's app number d'ina 08100084251
Idan kika karanta mun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitarmun Allah ya isa ban yafe miki ba
SONE KO K'IYAYYA
65&66
*washe gari*
Da misalin k'arfe 11:00 na safiyar yau satday dubban jama'a suka shaida d'aurin auren *Aliyu Ibrahim me tubarau da maryam yakubu lawal* Akan sadaki naira dubu d'ari biyu kacal"kasan cewar nasu yaya Aliyu Aka fara d'aurawa kafin Ad'aura na sauran"gaba d'aya bakin Ango yak'i rufuwa"sbd irin tsantsar farin cikin dayake Aciki"ya cakare cikin farar shadda y'ar ciki da malun malun An mata Aiki da dark brown d'in zare"takalmi, Agogo,hula duk dark brown yasaka"yayi wani irin kyau na ban mamaki"jikinsa na fitar da wani irin fitinan nan k'amshi"kyakykyawar fuskarsa na fitar da Annuri"har wani haske ya k'ara"babban Amininsa wato brr Ahmed na gefensa"shima yaci wankan light blue d'in shadda"yayinda mazan gidan ummi dana gidan umma sunyi Ankon milk d'in shadda"yaya sulaiman da yaya isma'il suma fararen shaddojine Ajikinsu"gaba d'aya fuskokin Angunan cike suke da Annuri"y'an jarida da marok'a sukayiwa yaya Aliyu caa"sai gashi da bakinsa yana basu Amsar duk tambayar da suka masa"gefen zuciyarsa kuwa son ganin In'am da irin kyalliyar datayi ne" Awannan rana ta musammun me d'inbun tarihi ga rayuwarsu"wanda be tab'a zaton zai mallaki In'am ta cikin sauk'i irin haka ba"sai kallon d'inbun jama'ar da suka masa kara suka halacci d'aurin Auren sa yakeyi"ya dubi brr Ahmed daketa yima marok'a kyauta ta bajinta yasaki murmushi yana Ida sallamar y'an jaridar" ya nufi gefen brr Ahmed yana fad'in Abokina sai mun shiga ciki An mana pics da my Angel da ummi sai mu shiga cikin gida"tunda reception d'in sai k'arfe 12 zamuyi"to shikenan Ango"Ai komai kakeso haka za'ayi"yaya Aliyu yayi murmushi ya rungume brr Ahmed yana fad'in hak'ika kai Aboki na garine Ahmed"banida bakin yimaka godiya Arayuwata saidai na maka fatan Alkhairi"Allah yatsare shaid'anun mutane Atsakaninmu"Ameen yah Allah Abokina karka damu"nima bazan tab'a manta Alkhairin dakamun Arayuwa ba"Ayanzun haka kaine sanadin yadda danake yanzun" Allah shine sanadi"bbu komai Abokina muje"cewar yaya Aliyu"yafad'a suna tafiya cikin nutsuwa sauran Abokansu na biye dasu"kasancewar Anan babban masallacin Anguwar Aka d'aura Auren"Ak'afa ma suka iso gida"gaba d'aya gidajen biyu cike yake da d'an Adam"dukda kuwa da safe ne"dan ummi wannan shine bikin farko datayi.....
Chapter 51 · 0% Book details