← Book details So Ne Ko Kiyayya Part 1 Complete Hausa Novel. Local reading mode
READING PART 47 OF 65

Sashe 47

So Ne Ko Kiyayya Part 1 Complete Hausa Novel. · about 8 min read

In'am ta shigo gidan cikin nutsuwa"tana k'arema bakin get zuwa parking lot kallo Amma bbu Alamar yaya Aliyu Awajen"Atake ranta yabata yana b'angaren sa"badan tasoba ta nufi hanyar shashen nasa dan maganganun ummi data yimata nasiha yanzun sunyi matuk'ar tasiri sosai Azuciyarta.....tun dg nesa ta hango yaya Aliyu shida brr Ahmed zaune kan resting chairs suna mgn"shi yaya Aliyu yana cin Abincin data Aiko masa dashi"ya wanku cikin k'ananu kaya"ramar da yayi ta k'ara fito masa da kyawunsa"d'auke Idonta In'am tayi dg barin kallon su"Aranta tana fad'in yau yaya be gyara sajensa ba"da wannan tunanin ta iso gefensu kamar me tausayin k'asa sbd yadda take tafiyar cikin nutsewa"Assalamu Alaikum! ta fad'a cikin siririyar muryarta"bazan Amasa ba tunda kin shanyani"tunfa 2 pm muka dawo dg Asibiti my Angel shine kikak'i zuwa ki ganni sai yanxun ko??"yafad'a Ahankali yana tsareta da Golden Eyes nashi"brr Ahmed yayi murmushi ya Amsa sallamar tata"Aransa yana fad'in maza bamuda kunya duk girman mu.....bafa haka bane yaya Aliyu na tsaya ne ina maka girki"zanzo kuma saika Aiko ko?"niban huce ba"d'an murmushi tayi kanta Ak'asa bata yadda ta kallesuba sbd wata iriyar kunyarsa dashi kansa brr Ahmed d'in takeji"cikin nutsuwa ta duk'a k'asa tana fad'in yaya ina wuninku ??"lafiya qlau"cewar brr Ahmed"me tubarau dake kallonta yaji kamar ya janyota jikinsa dan ba k'aramin kyau ta masa ba"tashi kizo ki zauna"batayi musuba ta tashi ta zauna dg gefensa"Aransa ba k'aramin dad'i yajiba da yanda ta gaidasu da kuma bin umarninsa datayi"yatabbatar da cewa ko bayan Aurensu In'am zata masa biyayya tunda ko'a baya tana masa dama.....kinyi shiru Amaryar mu?"cewar brr Ahmed cikin tsokana"In'am gabanta yafad'i ta d'ago kanta Atsorace tana bin yaya Aliyu da kallon tambaya??" ya gyad'a mata kansa yana sakin murmushin gefen baki"tayi k'asa da kanta"shi kuma yama kama brr Ahmed harara da kallon gargad'i"dan dama firan In'am d'in ce sukeyi yana sanar masa tayi accepting d'in soyayyar sa d'azun sai gata ta zoma"nidai bara na wuce tunda ga madam taka nan tazo"sai munyi waya ko?"okay"yaya Aliyu yafad'a Atak'aice" yana kallon mutuniyar tasa datayi k'asa da kanta"In'am na tafi ki gaida ummi"to zataji"ta Amsa Ahankali tana zuba ruwan dake Ajiye cikin cup ta d'ago kanta tana fad'in yaya gashi kasha"kallonta yayi murya can k'asa yace"my Angel haka Ake bama miji abu dama?"baki kalleniba kuma babu d'an murmushi sai kawai na Amsa?.....tsabar yadda taji kunyar maganarsa sai taji kamar k'asa ta tsage ta shige ciki"Amma ta lura shifa ko'a jikinsa yana fad'a ne iya Abinda ke ransa"kinyi shiru my Queen?"nidai ka Amsa konayi tafiyata"kuma wannan yaya Ahmed d'in shine yake cemun Amarya??wani miskilin murmushi yasaki yana Ajiye spoon d'in hannunsa da plate d'in Abincin kafin cikin k'asa da murya yace"Ai gaskiya yafad'a ke Amaryar me tubarau ce ko my Angel?"sbd kefa na zama tuzurun k'arfi da yaji ai kin tausayamun kizam....kukan shagwab'a tasaka tana fad'in ko kayi shiru wlh ko nayi tafiyata"shiru yayi ya Amshi ruwan yana fad'in shikenan tunda bakya son maganar nayi shiru"batayi mgn ba kanta Ak'asa"bayan yagama shan ruwan ya kalleta Ahankali yace"kinyi kyau my beauty"yau kuma hijab kika saka?"uhmm! mgn fa zaki mun ba uhmm ba"na lura tunda Abba yatambayeki kina SONA shikenan kika dena sakin jikinki dani"ni kuma bana son hakan"karki manta kece fa babbar k'awata"gaki kuma Amaryata....ni Allah zan tashi na tafi"dama haka kake yaya Aliyu?"ni banyi komai ba my Angel"kawai shawara zan baki kima Ajiye zancen kunya"dan rayuwar turawa na tsara mana zamuyi"bani son rayuwar duhun kai kaida family naka....tashin dayaga In'am na k'ok'arin yi yasaka yayi shiru yanata murmushi shima ya mik'e tsaye"kinsan Allah kina yin taku guda rungumeki zanyi"miye laifina daga na fad'i gsky??"to Amma yaya niba yarinya bace"dan Allah fa?"ya tambaya yana kallonta"ta ballah masa hararar wasa"ta miki kyau my Angel"kinma san mena tuna?"girgiza kanta tayi"idan na miki wani abu ki murgud'a wannan d'an bakin naki "koki mun gwalo kina zaton bana ganinki duk ina kallonki cikin tubarau d'ina"d'an zaro ido tayi sai kuma ta rufe fuskarta da tafikan hannayenta tana dariya"Eh mana kin zata yaya Aliyu baya kallonki ko?"to bari kiji my Angel sbd nadinga ganinki yadda nakeso shiyasa nake saka black glass"to Ai yanzun naganoka ko?"to ai bbu komai tunda kin kusan zama tawa ko?"ina fatan kinci Abinci ko?"naci yaya"kaima yanzun kaci Amma bakasha magani ba ko?"sai zuwa 4 zan sha haka tsarinsa yake"girkin nan yamun dad'i sosai fa"saidai kuma idan kinzo gidanki kukune zai dinga mana girki ke hutawa zakiyi ina rainon ki ko?"kai yaya da gaske?"Eh mana my Angel"nifa kamar baby girl y'ar 2 yrs nake ganinki sbd haka karki damu"murmushi tayi cikin jin dad'i Ahankali tace"zan tafi gida Amma ni saika rakani"babu damuwa my !

Abinda kikeso shine za'a yi"naji dad'in gyaramun part nawa da kikayi my Angel"pls ki dena wannan jin kunyar nawa banaso kin jiko?"shikenan nadena yaya "Amma nida nafeesa muka gyara maka Ai"kinga pic d'in wata yarinya??"murmushi tayi tace"niface yaya"hakane dannaji meye zaki fad'a"yaya Aliyu! na'am my Angel"yafad'a yana kallon ta suna dg tsayen"turo baki tayi tana b'ata fuska tace"ina wannan dr salma d'in??"murmushi jin dad'i yasaki Aransa yace"kishi! tana nan muna waya da ita koda.....saurin rik'e gefen hijab nata yayi yana murmushi har fararen jerarrun hakoransa suka bayyana"nika cikani kaje ka kirata mana"maida wuk'ar tawan"yaya Aliyu naki da soyayyar maryam kad'ai aka haliccesa"najima da korarta dg Asibiti nah"to bayan itafa?"my Angel kefa kikace mun yarinya ce ke?"shine kike kishi haka?"okay tunda kishin laifine cikani"kuma Ai banice kawai ke kishin ba... d'an murmushi yasaki dan shi burgesa takeyi wayo kawai yake mata tana zaro mgn"yanzun kuma ya yarda d'ari bisa d'ari In'am na matuk'ar son sa"dukda yana ganin irin son dayake mata sai iyayenta ne kawai zasuyi mata irinsa"my Angel baki yadda dani bane?"kema fa kinsan halina bbu ruwana da mata"yafad'a cikin rarrashi"kukan shagwab'a tasaka tana so ta janye gefen hijab nata daya rik'e"zo mu zauna kiji wata mgn"yafad'a murya Akasale"na lura rigima kawai kikeji ko maryam?"nok'e kafard'arta tayi tak'i mgn"me kikeso yanzun Ayi ?fad'amun naji? nika rakani gida"kuma ni Allah kadena duba mata suyita kallonka ko?"my Angel Aikina ne dubasu hak'uri zakiyi"bayan dubasu bbu komai tsakanina da wata"toba suna jin....sai tayi shiru"shikenan yanzun idan Akayi Auren mu saimu dinga zuwa office tare ko?"skul of nursing d'in fa?"kikace kin fasa"nidai Allah shine zanyi kodan sbd na dinga binka asibitin ko?"kin kyauta my Angel" kinga saiki dinga kulawa dani bbu wacce ta isa ta k'wace miki niko?"kanta ta gyad'a masa tana murmushi"shima yasaki murmushin yaja karan hancinta yana fad'in kinyi kyau sosai my lovely Angel"kaima haka yaya Amma shine baka gyara sajen naka ba?"d'an ware idonsa yayi yace"kinaso na gyara ne?"Eh mana zakafiyin kyau"to shikenan zo muje ki rakani na gyara"ummi fa najirana yaya"idan ka gyara muyi vedio call saina gani ko?"shikenan my Angel"kodai hakan be maka ba?"ta fad'a Ahankali"no! kome kikeso inaso nima"yanzun muje na rakaki ko?"yafad'a suna jerawa suna tafiya"yana janta da fira"ta hango nafeesa zata shiga part d'in umma"gafa k'awarki can kona tsaida miki ita??"ah ah yaya ka barta kawai"to my Angel da dare zanzo na ganki sannan naje na kwanta ko?"to yaya Allah yakaimu lafiya"goben idan da sauk'i saika kaini islamiyar ko?"driving zan fara koya miki duk week end fa insha Allah"Abinda islamiyar kun kusan idawa"hakane Amma naso kota week end ne naci gaba da zuwa pls"Eh zaki iya cigaba da zuwa sbd ilimi kogi ne"yafad'a suna tsayawa Adaidai bakin get d'in gidansu In'am"ta kallesa suka had'a ido"ya langab'e mata kansa"menene yaya Aliyu?"banaso ki tafi ki barni my Angel"ka koma ka hau online sai muyi fira ko?"nima bana son nisa dakai gashi baka lafiya"ai na warke tunda naji kin Amshi soyayya ta Azuciyarki maryam"Allah yabarmu tare"yafad'a yanata kallonta"cikin jin kunya ta Amsa da Ameen ta shige cikin gidan"yabita da kallo harta b'acewa ganinsa"sannan yakoma gida cike da tunaninta.....
**************
Acikin y'an kwanakin bbu Abinda masoyan keyi sai zuba love"dg yaya sulaiman har nafeesa da manyan lovers birds"wato In'am da me tubarau"wata irin kulawa da kafa kafa yaya Aliyu keyi da in'am"wani lokacin acan part d'in mommy sukecin Abinci a plate guda"wata rana Abba yasamesu "Aikuwa washe garin ranar yasaka ranar Aurensu wata ukku masu zuwa su 6"Aliyu da In'am,nafeesa da sulaiman, isma'il da zainab....tunda Aka saka bikin kimanin kwana 3 kenan yau In'am ke wasar y'ar b'uya da yaya Aliyu"shima kuma yayi busy sbd yana yin Aikinsa"saidai yakirata ta waya"Amma yasha alwashin yau da yamma har part d'in ummin zaije yasameta...

Agefe guda kuma mama gaje taji zancen saka ranar"wanda kuma ita tanata shirya yadda zata yiwa umma dubara tazo suje ta kaita wajen dodon tsafin su"dan rabon mama gaje da gidan tunda Abba yakoreta"taji zafin saka ranar"saidai tasha Alwashin bayan mutuwar umma zataje wajen boka yamata Aiki Afasa auren In'am da Aliyu"sai Aliyun ya Auri y'arta zubaida"shiyasa da umma ta sanar mata ta waya sai nunawa tayi bbu komai haka Allah yatsara"itama umman sai batayi mgn ba tayi shiru kawai.....

Farooq kuwa mugayen Alwashi yasha sosai kan In'am"kasancewar safwaan na bibiyar komai na metubarau da in'am"har fad'an da in'am tayi da farooq harta maresa saida safwan yasami labari"hakan yasa yanemi farooq yasakar masa kud'i kan yatura mahaifinsa yanema masa Auren In'am wajen dangin ubanta"ta hakane zai takata yarama Abinda ta masa"kuma ta hakane dr Aliyu zai shiga damuwa da tashin hankali"bbu b'ata lokaci farooq ya d'auki shawaran safwan"sai gashi kuma al'amari ya sauya saidai sukaji zancen saka ranar Aurensu itada me tubarau.....

Ayau misalin k'arfe 5 na yamma"duk suna tsaitsaye da bak'ak'en kaya da huluna ja samqn kansu"safwan da mama gaje suka fito dg tsakkiya"safwan yace"dodo nayi Alk'awari zan bada bahbah babban yarona kuma k'anina"mama gaje tace"dodo nayi Alk'awari zan bada hauwa yayata y'ar uwata.....wani irin mugun farin ciki safwan yaji domin yasan mahaifiyar dr Aliyu me tubarau take nufi"yasha Alwashin idan haka yafaru da kansa zaije da y'an daba har gidansu me tubarau yasanar masa komai game da mutuwar mahaifiyarsa"sannan yakashesa da hannunsa"bayan duk sun gama Abinda yatarusu"kamar kowane lokaci safwan ya d'akko su mama gaje da hjy wasilah Amotarsa suka wuce gida gab da sallar magrib"bayan ya mik'a su gida "kai tsaye get house nasa safwan ya wuce bbu tunanin yaje masallaci yayi sallah"dan tun bayan yashiga k'ungiyar yadena sallah...
Chapter 47 · 0% Book details