← Book details Madadi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 78 OF 143

Sashe 78

Madadi Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Halisa tace "Aikin banza kawai ki daina dena za'kewa a gidan da baki da gado dashi sai kace gidanku sai wata fuffuka kikewa mutune." Naja'atu shuru tayi bata tanka mata ba, Munira kuwa ta mayar da Halisa kamar mahaukaciya sai dariya take mata, Halisa ta cika tayi fam fam! takaicin ya isheta, aikuwa yana saukowa wai zata kai mai 'kara! ya kuwa buga mata razannaniyar tsawar da tasa ta dauki jakarta babu shiri tayi waje! bayanta yabi ba tare da ya kalli iskar da ta d'ebo su ba.
*Littafin na kudi ne...!*
Koda zaki ganshi a gruops na tasa ne idan kina bukatar ki biya kudin littafin ga yanda abin yake Vip group #600 normal gruop #300...account 0542382124...Binta umar gtbank...Idan katin waya zaki tura kiyi min mgn ta whasap da wannan numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
*MANZIR _ALWAFIR ABUJA
_*Sun tanadarwa da mata kayan gyaran jiki masu kyau da inganci magungunansu babu almundahana a ciki mutukar kika fara amfani da ingantattun magungunan company manzil alwafir to ba zaki daina ba saboda ingancin magungunansu ko wace matsala kike fama da ita mutukar ta shafi zamantakewar auranki manzil alwafir zasu share miki hawaye da akwai gruops na mussaman da suka bude domin taimakon mata masu fama da matsaltsalo a gidan auransu idan kanki na cikin duhu mutukar kinyi rijistar dasu to kukanki ya 'kare idan kina bukatar kiyi rijistar sai kiyi magana.*_
Bayan fitarsa daga palon Munira tace" Ammafa k'awata banyi tsammanin ganin Abbah Abbas haka ba wallahi na d'auka zanga ya 'kara tsufa gami da furfura sai naga kamar ma 'kuruciya aka 'kara masa yanzu dan Allah waye zai dauka waccan matar matarsa ce sam basu dace da juna ba." Naja'atu ta kalleta da mamaki a tare da ita tace"Ban gane inda maganar ki ta dosa ba Munira kina kallon mutum da girmansa da shekarunsa amma kike wata maganar 'kuruciya kawai dan dai ma'abocin ado da kwalliya ne shiyasa tsufansa baya fitowa.'' Munira tace"Nima ai abinda nake nufi kenan ba wani abuba.
*(Kunji Munira ta waske taga Abbah Abbas ta qyasa shine ta kasa yin shuru hum!)*
Shuru sukayi na minti biyu kafin kira ya shigo wayar Munira koda ta duba sai taga Bash ne da sauri ta dauka tana tambayarsa inda yake, yace yanzu haka yana masaukinsa yaje ya kama daki a hotel saboda haka gobe da wuri ta shirya su zasu tafi a 'karshe yace ta bawa Naja'atu wayar zasuyi magana....Cike da zumudi ta kar'bi wayar ta kara a kunnanta murya 'kasa-'kasa tayi masa sallama Bash jin muryarta a narke ya sake tayar masa da feelings ya rungume pillow hade da matse shi a kirjinsa yana ji tamkar ita ya rungume a jikinsa, ya shiga yi mata bayanin yanda sukayi dasu baba malam...Naja'atu ta nuna farin cikinta sosai da sosai dan bata ta'ba tsammanin iyayen nata zasu amince mata da auran Bash din ba.....Sosai ta saki jikinta dashi a waya suka dinga hira tana kyalkyala dariya hade da sake jin tsantsar kaunarsa na ratsa jikinta, Hakika Bash ya isa soyayya kuma yasan matakan sace zuciyar mace shiyasa lokaci guda ya sace raunanniyar zuciyar Naja'atu da salon soyayyarsa.....Nan Hajiya ta sauko ta samesu ta tana waya tana jin muryar hajian suna magana da Munira amma tsabar shau'kin hirar soyayyar da suke da Bash yasa ta gagara juyowa ballantana ta fahimci maganar da hajian take...Munira mikewa tayi ta nufi wani daki dake cikin palon nan hajia tace su shiga su kwanta Naja'atu motsi kasa yi domin bata so ko kadan tayi missing din kalma guda dangane da kalaman da Bash ke mata.

Munira har tayi wanka ta shirya jikinta naja'atu bata shigo ba to itama duk dare sun saba waya da Muktar dinta tasan yana can yana neman wayarta zaiyi tunanin koda wani take hira sai ta fita palon tace" sarkin soyayya yana da kyau nima ki bani wayar naji muryar masoyina." Cike da shagwaba tace"Sweetie kaji Munira tana min gori akan waya ko.

Bash yayi wata birgima akan bed din da yake kwance yasa hannu kan katuwar jijiyarsa data mike cikin sar'kewar murya yace."Darling bata wayarta insha Allah gobe kafin mu tafi zan baki daya daga cikin wayoyina sai mu dinga gaisawa da juna kafin Allah ya mallaka mana junanmu." Tace"To godiya nake sweetie Allah ya kara mana kaunar junanmu." a sar'ke yace."ameen babyna ammafa yau da kyar zan iya bacci dan gabadaya kin tayar min da sha'awa gabana ya mike sosai ke kadai nake bukata beb." Wani irin yanayi ta shiga jin abinda yace sai itama taji tana sha'awar kadaicewa dashi lumshe idonta tayi a sanyaye tace" Nima ina cikin kewarka Bash sai dai muyi hakuri da juna har sai sanda Allah ya mallaka mana junanmu." Bash ya sauke ajiyar zuciya yana sake danne joystick dinsa dake ta faman motsi tana kara hawa yace."Yanzu ba zaki taimaka min da wani abuba ki dauki hoton nononki yanzu ki turo min dashi ta whasap din Munira nasan kallon breast dinki zai sanya na samu sassauci."
Gabanta ya tsananta faduwa jin abinda yace murya na rawa tace"Kayi hakuri Bash ba zan iya ba ka bari na zama mallakina zakiyi duk abinda kake so dani." Sai ta kashe wayar tana kallon munira wacce ke tsaye tana jin muryar bash din sama sama da abinda yake bukata a gurin kawarta...Tace"Haba Naja'atu meye dan kin tura masa brest dinki kece fa kika tayar masa da hankali ba sai kiyi kokarin kawo masa nutsuwa ba wallahi tun yanzu ki kama zuciyarsa a hannuki dan na fada miki tarin 'yan matansa idan kika sake kika zauna gardama to zaki sha mamaki.''
Naja'atu shuru tayi tana tunanin maganganun Munira anya kuwa zata iya daukar hoton nononta ta tura masa, gaskiya ba zata iya ba, Mikewa tayi hade da mikawa Munira wayarta ta nufi daki, munira tabi bayanta da kallo tana ta'be bakinta ita a ganinta ba laifi bane dan budurwa ta nunawa saurayi wani sashe na jikinta ai duk a cikin so ne( 'kalubale gareku 'yan matan da zawarawan da suke da irin wannan d'abi'a wallahi duk saurayi ko bazawarin da zaice miki yana so yaga wani bangare na jikinki to ba sonki yake ba dan iska ne yana so ku watse ne a waje koda ya aureki auran ba zaiyi qarko ba dan zargi ne zai shiga a tsakaninku ayi ta samu matsala ba'a namiji dan iska sai mace mutukar kika bada 'kofa to shi kuma namiji dama haka yake so zai shigo miki da iskanci iri-iri duk iskanci namiji idan bai ga kofa ba dole ya kyaleki)
Washe gari tsaf suka shirya Naja'atu da Munira suna fitowa palo tayi tozali da 'Ya'yanta a zaune Baba larai ta kawo su....Sai dai yanayin yanda taga fuskokinsu cikin rashin walwala yasa jikinta yayi sanyi....Ta zauna a hankali tana rike hannun Mussadiq da fadin yaushe kuka zo.?

Yaron babu walwala a fuskarsa ya gaisheta..Saddiqa da mufida suma suka gaisheta babu walwala a tare dasu ta amsa cikin damuwa da yanayin data gansu a ciki.

Baba larai cikin ya'ke da kokarin danne damuwarta tace"Naja'atu banji dadin abinda kikayi ba wallahi ashe duk abinda nake fada miki a gida ba kya dauka shuru kawai kike min ashe ke kin san abinda kika shiryawa kanki da 'kuruciyarki da komai zaki 'bata rayuwarki."
Zum'bura baki tayi tace"Dan Allah baba larai mu bar maganar nan ta riga ta wuce hajiya ma tace a daina tayar da ita duk abinda ya faru Allah ne ya hukunta amma ku daina dora laifi a kaina." Baba larai tace"To Allah ya huci zuciyarki naga kamar bakiji dadin maganata ba, dama Alhaji ne yace a kawo miki kayanki gasu can a gefe guda."
Kallon inda kayan nata tayi taga akwatin nan lefanta da sauran kayanta na gidan dauke kanta tayi ba tare da tace komai ba....Hajiya ce ta sauko daga sama ganin Larai da yaran a zazzaune yasa ta saki fuskarta ta zauna kan kujera suna gaisawa da larai hade da tambayarta hidima da yara....Larai tace alhmdullhi sannan ta fada mata abinda ya kawota gidan
Hajia tace"Hakan yayi dama nayi tunanin wanda zan tura ya kwaso mata kayanta to Allah yasa haka shi yafi alkairi." Larai ta amsa da amin....Saddiqa ce ta mike fuskar nan ta a had'e ta kalli su Mussadiq da fad'in ''Ku taso mu shiga gidan Baba malam." Yaran suka mike da sauri....Hajia tace"A'a kishiyata kumbure kumburen me kikeyi ko gaisuwa babu." Saddiqa ba tare da ta kula ta ba tasa takalmanta ta fice daga palon tana kokarin mayar da kwallar dake so ta zubo mata....Gani take kamar hajian ce ke daurewa Naja'atu gindi tana abinda take so! hajia a maimakon ta nuna damuwarta dangane da faruwar al'amarin sai taga kamar ma murna take tana nunawa duniya kamar ba itace ta haifi Abbansu ba...........Baki a sake suka bi yaran da kallo har suka fice daga palon.
Chapter 78 · 0% Book details