← Book details Madadi Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 37 OF 143

Sashe 37

Madadi Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kai tsaye tace"Bana jin yunwa."? jimm! yayi yana nazarin maganarta yasan karya takeyi kawai tayi fushi ne saboda yayi mata fada, yace."Sabida kinyi laifi anyi miki fada shine zakiyi wa kanki horo da yunwa." shuru tayi ba tare da ta tanka masa ba..........Ganin ta'ki cewa komai yasa ya girgiza kanshi ya kama hanya ya fita daga dakin, yasan dai yunwa ba kanwar lasa bace lokacin da zata nemi abinci babu wanda zai sani, shi dai ya sauke nauyin dake kansa, Koda ya shiga dakin nasa bai sa key a kofar ba barinta yayi a bude wai ko zata shigo ta kwanta......gajiya yayi da jiran shigowarta dakin bacci mai nauyi ya dauke shi...
*Littafin na kudi ne....!*
Koda zaki ganshi a group's to na sata ne idan kina so ki biya kudin karatu to ga yanda abin yake.

VIP Gruop #600
Normal gruop#300
Accont: 0542382124....Binta Umar gtbabk idan katin waya zaki turo kiyi min magana ta whasap da wannan numbar
07084653262
*BINTA UMAR ABBALE*
BHRBN
*26*
Da safe yaran suka tashi cikin walwala da farin ciki, Naja'atu kuwa kwana tayi cikin 'kunci da takurewar zuciya kafin ma tayi bacci sai da taci kukanta ta koshi sannan.......... dalilin kukan da tayi yasa ta tashi da jan ido Mussadiq yaron da ya damu da ita sosai shine ya dameta da tambayar mai ya samu idonta yayi ja, tace masa ciwo yake mata, yaron ya yarda da maganar data fad'a ita kuwa Saddiqa jinta kawai tayi da kunne ta riga ta gane kuka ne ya mayar mata da ido kamar jan gauta...........Tana cikin taimakawa Mussadiq gurin sanya takalminsa ya shigo dakin, yana sanye da jallabiya ba'ka mai yankakken hannu, as'usul hannusa da k'aramin carbi yana ja...Yaran suka shiga rige-rigen gaishe shi ya dinga amsawa cikin sakin fuska, da kulawa.

Kanta a kasa ba tare data d'ago ba tace"Ina kwana." Ya amsa lokacin da yake kokarin fita daga dakin, yaran ne suka biyo bayansa kai tsaye suka nufi dannig domin karyawa, sai dai me? babu komai a kan dannig din....Abin ya bashi mamaki sosai ya kalli Saddiqa yace."Baku had'a break bane."?

Tace''Ai bamu tashi da wuri ba shiyasa." shuru yayi takaici kamar yasa zuciyarsa ta buga, yace."Yi maza kije ki dafa muku indomee kafin Salim din yazo." Da sauri ta nufi kicin din...Dakin Halisa ya nufa, ya tarar da ita tana sallah! sai bayan da ta idar sannan yace."Ashe bayan na fita komawa kikayi kika kwanta wai me yasa kike wasa da sallah ne."?

Ya kalli agogon hannunsa yana kallonta babu faraa a fuskarsa yace'' dubi lokaci bakwai da kusan rabi kina kwance baki yi sallah ba bayan kuma kin san da cewar yara zasuje makaranta."
Cikin 'kosawa da maganarsa tace"bayan nasan yara zasuje makaranta to me zanyi musu ?

Saddiqa ta iya komai idan ma ita Naja'atun ba za tayi ba ai Saddiqar sai ta dafa musu abinda zasu ci da wanda zasu tafi dashi tunda kasan ni ba lafiya ce dani ba." Yace."Duk da haka me zai hana ki 'kokarta ki shiga kicin d'in kiyi wani abun." Shuru tayi masa domin itafa ba zata dinga katsewa kanta bacci ba ta tashi tana wani hidimar yara....Yace."Tunda dake da Naja'atun duk kun zama 'yan kanku zan sa a kawo min mai aiki wacce zata dinga kulawa da yarana, ke kina ganin kyashin kulawa dasu tunda ba ke kika haifesu ba ita kuma tana fama da kuruciya da rashin hankali okey ku cigaba da abinda kuke zan dauki mataki." Yana kare maganarsa ya fita daga dakin.

Kicin din ya nufa Allah sarki sai ya shiga taimawa Saddiqar cikin tausayinsa tace"Abba kaje ka huta zan iya komai." Girgiza mata kai kurrum yayi ya cigaba da feraye dankali yana sawa a ruwa.....Hawaye ta goge tace"Dan Allah Abbah kaje ka huta wallahi zan iya ka bari." Tafada tana kar'bar wukar hannunsa,
da sauri ta zuba indomee din ta cigaba da fareye dankali yana tsaye yana kallonta, tausayi yaran suke bashi! gabadaya basu san wani abu damuwa ba a lokacin da mahaifiyarsu take raye babu abinda ta gaza musu tana sauke hakkinsu dake kanta ta kowanne 'bangare, babu shakka Allah baya barin wani dan wani yaji dadi.

Naja'atu ce ta fito palon ta samu Mufida da Mussadiq a zaune a kan kujera, gurin cin abincin ta kalla taga babu komai a kai tace"Ke Mufida ba kuyi break bane."?

Mufida tace"Eh Mommyna bata da lafiya shine Abbanmu yace ."Yaya Saddiqa ta dafa mana indomee." Sai taji tausayin yaran ya kamata da sauri ta nufi kicin din...Turus! tayi ganinsa tsaye a jikin drowar kicin suna magana da Saddiqa wacce take aikin soya dankali.

Kanta a 'kasa ta shiga kicin din sosai, shi kuma ganin ta shigo kicin din yasa ya fita ba tare da yace komai ba.......A gurguje suka gama had'a abin karyawa, Saddiqa ta shirya musu dannig din suka zauna suna karyawa, Halisa ta fito daga dakinta ko kunya babu ta zauna gurin cin abincin, ita kuwa Naja'atu barin gurin tayi cike da takaicin abinda Halisan keyi a gidan............Salim ne ya shigo wanda yayi dai-dai da fitowar Abba Abbas din daga da'ki! musabaha sukayi da juna Salim kamar wani mutumin kirki sai sunkuyar da kansa yake yana tsokanar Mussadiq Abba Abbas ya zauna kan kujera yana kallonsa yace."Idan ka kaisu skull din ka wuce kasuwa kawai sai misalin sha biyu sai kazo ka dauke ni." Yace."Kawu ina fata dai lafiya."?

Yace."Lafiya lau zan dan huta a gida ne kafin lokacin."
Salim ya lura Kawun nasa kamar yana da damuwa farin ciki ne ya cika masa zuciya yana addua Allah yasa hoton jiya ya gani ya d'aga masa hankali......Hanyar fita ya nufa yana karkad'a key din mota yaran suka bi bayansa cikin sauri.

Halisa tana gama break din mikewa tayi ta dawo kusa dashi ta zauna hade da d'ora kanta a kafadarsa.

Tace"Na fahimci tun jiya kake cikin damuwa kayi hakuri dan Allah ni dai duk abubuwan nan da suke faruwa ba'a son raina ba dan da inada lafiya da babu abinda ba zanyi ba, kuma magungunan dana shane suka kashe min jiki shiyasa ban tashi da wuri ba amma insha Allah hakan ba zata sake faruwa ba."
Wannan maganganun na Halisa sun wanke masa zuciya sai ya daina ganin laifinta gabad'aya ya dauki laifin ya d'orashi kan kan Najaatu.......Halisa shigewa jikinsa ta cigaba dayi tana dan matsa masa ga'bobin! jikinsa lokaci guda jikinsa ya mutu! kasala da sha'awa suka saukar masa sai kawai ya gyara zamansa kan kujerar hakan ya bata damar hawa jikinsa sosai tana cigaba matsa masa jiki jallabiyarsa take kokarin cire masa.... dai-dai lokacin Naja'atu a fito daga dakin, ganin abinda ke faruwa yasa gabanta ya fad'i! gabadaya ma su basu san ta fito ba dan Halisa ta samu nasarar cire masa jallabiyarsa shi kuma ya rungumeta 'kam! yana sansana jikinta had'e da sumbatar wuyanta........Ji tayi kafafunta na rawa! da sauri ta juya domin komawa dakin hawaye na nema ya zubo mata!!

Abbah da Halisa shafe-shafen su sukayi a palon kafin su nufi daki domin biyawa kansu bukata.

Zama tayi ta zabga tagumi!! daga zarar ta tuno lokacin da yake sumbatar wuyan Halisa sai gabanta ya fad'i tsigar jikinta duk ta tashi, zazzafar soyayyar da yake mata ta dinga dawo mata a 'kwa'kwalwarta! wani irin kishin Halisa ya cika mata zuciya, mike tayi ta shiga zagaye dakin so take ta fita amma tana jin tsoron kada ta fita taje taga abinda zai tarwatsa mata zuciya.

Hawaye ta dinga sharcewa tana kai kawo a dakin...Yanke shawarar fita tayi ta tarwatsu!! kawai taga basa palon sai jallabiyarsa da dankwalin les din Halisa!

Tsaye tayi kan doguwar kujerar da suka tashi, ta dinga kallon kujerar kamar su take kallo! a fusace! ta dauki jallabiyar tasa da dankwalin Halisan ta watsa su bakin kofar dakinsa!

Zama tayi ta rufe fuskarta da hannayeta ta shiga rera kuka! zuciyarta na wani irin bugawa! yanzu me sukeyi a daki!

Ta bude fuskarta da sauri tana kallon kofar dakin nasa, taji kamar taje ta 'balle kofar! hanci ta sha'ka! a fusace! ta mi'ke ta nufi dakin su Saddiqa ruf da ciki ta kwanta kan gadon Mussadiq ta dinga kuka tana dukan pillo..........Ta jima cikin wannan yanayin kafin ta sake mikewa ta fita palon....Ikon Allah har yanzu suna ciki basu fito ba, agogon dake kafe a bangon palon ta kalla taga kusan goma da wani abun sunyi awa d'aya da rabi da shiga dakin........

Cikin kyarmar jiki ta nemi guri ta zauna tana fuskantar kofar dakin da suke ciki.

Halisa tana can maganin 'Yar Sa'adu na aiki Eh lallai babu shakka maganin yaci kudinsa dan gabadaya Abbah Abbas ya rikice sai faman sasakar Halisa yake kamar babu gobe yi yake tamkar zai farketa ya kawo kusan sau uku amma ya kasa hakura!

Halisa tun tana taimaka masa har ta daina dan ta galabaita sosai! bata ta'ba tsammanin maganin aikinsa ya kai hakaba!

Amma saboda ta cuzgunawa Naja'atu ta'ki saduda ta kwaci kanta bashi take yana ci sai kace jaka.

Naja'atu tana zaune tsuru a palo motsi kadan ta kalli agogo sha daya tayi ga sha biyu ta kawo kai babu labarin masu gidan, cikin karaya da sarewa ta mi'ke tana rangaji zata nufi daki.....Yaya Ramlatu ta rangad'a sallama a palon...Da sauri ta tsaya tana kallonta, Yaya Ramlatu ganin yarinyar a firgice yasa ta daka mata tsawa tace"Ke meye kika, tsaya kina kallona sai kace baki sanni ba."
Ji tayi hawaye naso su zubo mata sai dai ta daure bata bari sun zubo ba cikin rawar baki tace"Yaya Sannu da zuwa ga guri zauna."
Yaya Ramlatu tace"Da kece kike nuna min gurin zama kaji yarinya da iyayi mtssw ina matar gidan take."? tafada tana rarraba idanunta a palon.

Cikin kokarin danne damuwarta tace"Tana daki." Yaya Ramlatu ta mike ta nufi dakin Halisan tana surutai......Tsaye tayi tana jiran fitowar Yaya Ramlatun, ta fito ranta a bace tace" Kince tana daki to yana duba banganta ba ashe na zama abokiyar wasanki.

Girgiza kanta tace"A'a kiyi hakuri mybe to tana dakin Abbah." Ramlatu tace"Maijin naku bai fita bane."?

Da sauri tace"Ya fita tun safe." Tsaki!

Ramlatu taja ta nufi dakin Abbah Abbas din kawai ta shiga bugawa da karfi tana kiran sunan Halisa.
Chapter 37 · 0% Book details