← Book details Halysaah Part 6 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 173 OF 218

Sashe 173

Halysaah Part 6 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Me yasa bakya tsoron Allah Khaleesat
Cikin few seconds Khaleesat ta kashe komai ta mayar masa da controller dinsa inda yake ajiyewa, ta mayar da throw pillows dake kasan carpet zuwa kan kujera, tana juyawa taga Safiyyan har ta haura sama, ta bi bayanta da sauri suka shige dakinta, Khaleesat ta dinga kyalkyala dariya har da rike ciki, Safiyyah ta hade rai tace
To wai meye abun dariya?

Ke abinda ya kamata ayi dariya ba shi kike ma dariya ba sai wanda ba na dariya ba, yar
xu meye abun dariya don Allah a nan, ni ban ma san yamma tayi haka ba ai da tuntuni na tafi tafi hoto foon dariune do tako Khaleesat dai cute li va bude unter downtabaidan
. fito har Safiyyah ta bar apartment din gaba daya ta mike cankarshen layi tana yi tana hadawa de gudu.

Khaleesat ta kasa dena dariya ta dawo cikin apartment din ta kulle kofar ta wuce sama ta shige dakinta don kar ma ta hadu da shi.

Karfe tara saura Khaleesat ta bude kofar dakinta a hankali ta fito corridor tana leka downstairs don yunwa take ji, zaune ta gansa a parlor yana online game, ta sauko downstairs ganin ya gyara game din da suka rikitar, plate din abincin da ya ci ta kalla, saura kadan tayi dariyar da bata yi niyya ba, ga dai shi ya ci abincin da ta girka yau, kitchen ta nufa tana kallonsa, shi dai ko kallonta bai yi ba game dinsa kawai yake, ta duba sauran abincin da ya rage a kitchen din sai kuma ta fito tana kallonsa tace
Zan iya daukan sauran abincin?

Ba tare da ya kalleta ba yace
Da can tambayata kike kafin ki dauka, so you can steal it as usual ai kin saba
Juyawa tayi ta koma kitchen din ta juyo sauran abincin sannan ta fito, zaunawa tayi a bakin stairs tana cin abincin tana kallon como din da uske ul house to come cin shincin to har plato
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/B8DsB9xMdou36YgiMRcSlr Ena kuke masoyan ado da kwalliya,Ena amaran da uwayen gida masu capacity's ,oum eman ta tanadar maku hadaddun jakunkuna, takalma, abaya, dakuma duk wani nau'ika na jewelry's, masu matukar kyau da kuma quality, wani abun armashin shine muna kawo maku Kaya na Yan gayu masu class zakisa kayn mu kije unguwa kidawo batare da kinci karo damai irin Shiba , mekike jira kedai kawai shiga group domin kisami naki a price kalilan
HALYSAAH 81
Khaleesat ta langwabar da kai tana kallon Ajay a hankali tace "Good evening" Ya kusa 30 seconds tsaye yana kallonsu ya ki cewa komai, Safiyyah ta jawo handbag dinta a hankali ta rataye a kafada tana kallon Khaleesat murya kasa kasa tace "Kar Ya Musty ya fara kirana ni zan tafi gida" A tare suka bi Ajay da kallo ganin ya rufe kofar parlon ya cire makullinsa ya nufi staircase ya wuce sama, Safiyyah ta maida handbag dinta ta ajiye gefe tana washe baki tace "Ba daxu daxun nan na gama ce maki ba shi da matsala ba, wallahi dama nasan bazai ce mana komai ba don kowa yasan PS da shiga rai, ai ba kowa ne fitinanne ba" Plate din abincin da suka ci ta dauka ta kankare sauran shinkafar jiki ta cinye sannan ta ajiye ta dau Controller din da ta ajiye kan kafar Khaleesat zata ci gaba da game din tana cewa "Ai ba abinda zai ce mana wallahi, yana da saukin kai" Khaleesat tayi dariya tace "Kika san me yaje daukowa a sama, ni dai ba ruwana wallahi..." Tana fadin haka ta mike tsaye tana dariya, Safiyyah ta kara jawo handbag dinta da ta ajiye ta makala a hammata ta mike tsaye ita ma tace "Mu je ki bude min kofa ni dai kafin Ya Mustapha ya fara nemana" Khaleesat ta dafa kujera ta dinga dariya ba kakkautawa, Safiyyah ta hade rai tace "Meye haka don Allah, ina makullin gidan yake ni dai ki bude min in wuce" Ganin Khaleesat taki kulata sai dariya take ba
akawa, Safiyyah ta fixgo handbag din Khaleesat ta bude ko zata ga makullin gidan a ciki amma bata gani ba, tace "Ni don Allah meye abun dariya, ki bude min kofa in tafi kar yayana ya fara nemana mana" Khaleesat tace "Ki tafi ina?

Ai wallahi babu inda zaki je ki bar ni a gidan nan, ba ke kika ce mu zo muyi game ba" Safiyyah tace "Da nace mu zo muyi game tunda kin san baya so ba sai kice min A'a ba, ta yaya ni zan san baya so a ta
a masa kayansa, kin ga kar raina ya baci ki bude min kofa in tafi gida, wannan wani irin iskanci ne ana magana kina dariya" Dariya kawai Khaleesat take yi kamar zata shide, ran Safiyyah yayi mugun baci ta kankance ido tana kallon Khaleesat, lkci lkci take kallon sama kar Ajay ya sauko ya riske su, a fusace tace "Wallahi ban san haka kike ba da bazan biyo ki ba, ina zaman zamana kika ce min akwai Ps5 a gidan nan, in baki gaya min ba ta yaya zan sani, nayi da na sanin biye ki wallahi" Shiru tayi ganin Ajay na saukowa downstairs, Khaleesat ta hadiye dariyar da take tana kallonsa, Safiyyah ta sha kunu bayan ta koma gefen Khaleesat ta tsaya kamar masu jiran hukunci, shi dai ko kallonsu bai yi ba ya nufi kofa ya bude ya fita, da sauri Khaleesat ta tafi tana lekasa ta windon parlor, motarsa taga ya shiga ya tafi, ta dinga kyalkyala dariya tana kallon Safiyyah dake makale jikin windown ita ma tana lekansa, bata ma san sanda ta zo jikin windan ba, Safiyyah ta washe baki tace "Atoh ba nace maki bazai ce mana komai ba amma duk kika bi kika firgice, ai Ajay mutum ne, shi dai kar ka masa rashin kunya kawai" Bata jira cewar Khaleesat ba ta koma gun game din, Khaleesat tace "Ba gida kika ce zaki tafi ba Ya Mustapha na kiran ki" Safiyyah taki tanka ta tana gyara zama ta ci gaba da game dinta, Khaleesat ta dau plate din da suka ci abinci ta kai kitchen, bude baki tayi ganin ashe duka abincin Safiyyah ta juyo masu suka cinye, gashi ya dawo ya tarar suna masa game tasan kuma dole sai yayi mata magana ko ba yau ba, ga kuma an cinye masa abinci, jingina tayi jikin cabinet din kitchen din, ko dai kawai ta dafa masa wani abincin ai ba sani zai yi ba, fara harhada ingredients din da zata yi girkin tayi, sai ga Safiyyah ta shigo kitchen din tace "Don Allah ki zo mu ci gaba mana, tunda bai ce mana komai ba alamar ya bamu permission kenan ai, ke dai kin fiye tsoro" Khaleesat tace "Sophie ashe duka kika juyo abincin, yanxu idan ya kara dawowa yaga babu wani abincin fa?" Safiyyah tace "Ba sai kice masa Housemate ne ya zo ya ci ba, ai bazai san mu muka ci ba" Khaleesat ta wani kalleta, can tace "Kawai sai in ma Housemate dina sharri, ni dai wani zan dafa masa kawai" Safiyyah tace "To ki dafa har mu don ban koshi ba dama, kuma yayi dadi irin nasa don Allah" Daga haka ta koma parlor ta saka game din ita kadai tana yi, har kusan karfe biyar na yamma Safiyyah na bakin PS a zaune tana ta yi, Khaleesat tuni ta gama girkin da take har da grilling masa chicken lap biyu yanda dai yayi sannan ta kira Safiyyah tana tambayarta yanda ta ga abincin a kitchen, Safiyyah ta jera masa yanda taga ya bar kayansa sannan suka koma suka ci gaba da game....

Wajen karfe shidda game din ya dauke ya shiga wani waje daban, kokarin gyarawa Safiyya ta dinga yi amma yaki, Khaleesat tace "Dama sai da nace mu bar game din haka kika ki ji" Safiyyah taki tanka Khaleesat sai kokarin gyarawa take, garin gyara kawai ya dauke gaba daya, Khaleesat ta bude baki tana kallonta, Safiyyah ta ajiye controller din hannunta ta jawo handbag dinta ta makala a kafada tace "Kilan ma Ya Musty na ta kirana wayar na silent" Kokarin mikewa tsaye take Khaleesat ta rikota tace "Ban gane Ya Mustapha na ta kiran ki ba, waye zai gyara masa kina ganin abu ya dauke gaba daya?" Safiyyah tace "To ni bakanikin PS5 ce, ki kashe socket din kawai ki wuce sama ni kuma in tafi gida, ai mu ma bamu san me ya samu abun ba ya dauke, kilan ya dau zafi ne" Zaro ido Khaleesat tayi jin
aran mota a garage, Safiyyah ma ta gwale ido tana kallonta, mikewa Khaleesat tayi ta tafi window da sauri tana leka garage, ganin motar Ajay ta dawo da sauri tace "Wallahi shi ne ya dawo, gashi kin lalata masa abu..." Safiyyah ta zaro ido tace "Ban gane na lalata ba?

Ni kadai nake game din?

Me yasa bakya tsoron Allah Khaleesat" Cikin few seconds Khaleesat ta kashe komai ta mayar masa da controller dinsa inda yake ajiyewa, ta mayar da throw pillows dake
asan carpet zuwa kan kujera, tana juyawa taga Safiyyan har ta haura sama, ta bi bayanta da sauri suka shige dakinta, Khaleesat ta dinga kyalkyala dariya har da rike ciki, Safiyyah ta hade rai tace "To wai meye abun dariya?

Ke abinda ya kamata ayi dariya ba shi kike ma dariya ba sai wanda ba na dariya ba, yanxu meye abun dariya don Allah a nan, ni ban ma san yamma tayi haka ba ai da tuntuni na tafi gidanmu...." Khaleesat dai bata fasa dariyar da take ba, suka ji ya bude kofar daya daga dakunan dake sama, Safiyyah na jin haka ta bude kofar dakin Khaleesat a hankali ta fice, kafin Khaleesat ta fito har Safiyyah ta bar apartment din gaba daya ta mike can karshen layi tana yi tana hadawa da gudu, Khaleesat ta kasa dena dariya ta dawo cikin apartment din ta kulle kofar ta wuce sama ta shige dakinta don kar ma ta hadu da shi.
Chapter 173 · 0% Book details