Sashe 55
Fulani Psrt 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta amsa masa da dan fada domin ta matsu ya fita daga dakin. Juyawa yai cike da mamakin yadda Hajiya take masa ya fice. Mikewa tai tsaye ta isa gurin kofar ta saka mata key sannan ta dawo ta kira number Jarma, yana dagawa ta labarta masa komai shi kanshi ya cika da tsananin mamaki.
“Kin gani ba ni san mutanen nan basa taba mana karya�
“Ada can ina ganin abun kamar wasa, amman ganin wannan yarinyar ya bani tsoro kuma ya saka na yarda, yanzu miye mafita?�
“Mafita kawai a koreta daga gidan mana, babba ce?�
“Karama ce ba zata wuce warin Nana ba, ni abun ya bani mamaki ma, taya zata iya lalata mana aiki? Ko dai tana da aljanu ne?�
“Ko ma dai minene abun da nake ganin yafi kawai a koreta daga gidan, matukar tana cikin gidan nan zata bata maka lamari da tsari�
“To amman ya za ayi na koreta tun da bangarena take ba?�
“Haba Hajiya kamar ba mace ba, ki yi tunani mana, ni anjima zan shiga na gaishe da Hajiya dan na ga yarinya�
“Okay shikenan ai dole mu san abun yi kam�
Ta sauke wayar tare da sauke ajiyar zuciya tana tuna sauran abubuwan.
“Fadime Falmata Sardauna, wacece Fadime kuma? Waye Sardauna?�
Ya mike tsaye tana ta tunani.
“Sun ce akwai tafiyar da ba dawowa? Wace tafiya ce kenan? Wa zai yi? Mu ko kuma bangaren Ammy?�
Safa da marwa ta fara yi a dakin.
“Ina kyautata zaton yarinyar tana da aljanu ne wata kila zata fada ne, in ba shi ni ban ga ta inda zata iya lalata mana shiri ba? Kamata yai nai mata sanadi da gidan nan cikin ruwa sanyi ko kuma ayi mata asiri ta bar gidan gaba daya�
Sai kuma ta girgiza kai.
“No ai idan mu ka mata asirin idan tana da aljanu zata iya fadar gaskiya ta tona mana asiri�
Wayarta ta nufa ta kira Hajiya Talatu ta labarta mata abunda yake faruwa.
“Wannan maganar ba ta waya bace ranki ya dade zan shigo gobe da kaina�
Daga haka ta aje wayar, gaba daya ta rasa yadda zatai ta natsu, haka ta wuni cikin tunani kala kala ta kulla wannan ta kwance wacan ta saka wannan ta ga be yi ba, babu abun da yafi tsaya mata a rai kamar yadda Falmata zata lalata musu shiri as how kuma ta yaya? Lokaci bayan lokaci sai ta ambaci sunan Falmata Fadime Sardauna tana jinjina lamarin.
SHATTIMA POV.
A kofar gate din Hajiya a mutu ya faka motarsa duk kuwa da kasancewar Zainab ba son zuwa gidan domin yan uwan Hajiya Babba ne ita kuma ba wani shiri take da Hajiya Babba balle kuma yan'uwanta.
“Ina jin gobe zan je Yola, zan turo miki number police din da za su raka ki a can idan kin shirya kawai ki kira su zasu same ki har inda kike�
Zainab ta kalleshi.
“Amman Lafiya zaka je gobe? Ko ka sake samun hutu ne?�
“Baba Waziri ne yace yana son ganina, ya kira ni da safe yace idan zai yiyu mu hadu da a yau, nace masa sai dai gobe�
“Okay Allah ya tsare, ni ba zan dade ba, domin bana jindadi sosai kuma ina son na gama cikin kwana biyu koma�
Hannunsa ya mika ya dauko diary sa yai rubutu a kai ya cire paper ya mika mata.
“Ki ba wani ya karbo miki wannan maganin�
“Thank you�
Ta fada bayan ta karba, sannan ta bude motar ta bita, sai ya jira ta dauki akwatinta dake boot sannan yaja motarsa ya dauki hanyar asibitin, gaba daya wunin ranar daya tuna abun da Fadime ta saka Ra'ees sai yai murmushi, sai yana daf da tashi aikin sannan ya kira Ra'ees a waya bugu daya abokinsa ya amsa.
“Hello�
“Matsoraci�
“Uhmm Allah yasa kaji abun da naji, ba zaka gane ba ne Wallahi�
Shattima yai murmushi kasaita wanda ya karawa fuskarsa kyau da kwarji sannan ya sake magana a hankali.
“Gobe dai zaka yi duty na, zan leka Yola�
“Lafiya dai?�
“I don't know, Baba Waziri ke nema kuma tun har ya bukaci ganina kasan abu ne mai muhimmanci�
“Allah yasa alheri ne ya tsare�
“Amin�
Ya aje wayar har sai da Ra'ees ya kashe da kansa sannan ya mike tsaye ta hada komai nasa ya zuba a karamar jakarsa ta riko system dinsa ya fito daga office din.
Kai tsaye gida ya dawo daman can indai baya gida to yana gurin aiki dan kuma baya aiki to yana gida sai kuma idan wata fitar mai muhimman ta kama, domin shi ba mutum ne mai son yawo ba.
After sallah la'asar ya fito falon ya zauna yana kallon tv, be yi minti talatin ba ya soma jin laurarsa na son tashi, daman can indai zai zauna shi kadai a gurin yana tunani to zai haifar da kansa da matsala ne, cikin rashin kuzari ya mike tsaye ya shiga kitchen ya dauko cup ya ciro lemun tsaki a fridge ya yanka ya matsa a cup din ya jika Lipton ya hada ya shanye sannan ya fito ya hau sama zuwa bedroom dinsa. Wanka ya fara yi sannan ya kwanta saman katon bed din nan da nan bachi yai gaba da shi.
Be farka ba sai da aka fara kiran sallah magari, sannan ya unkura ya shiga bandaki a nan ma sai da ya sake watsa ruwa dan jin yai jikinsa ya masa nauyi sannan ya fito ya nufi masallacin unguwarsu. Ba dawo gidan ba sai after isha'i, daman can idan yai sallah magariba baya dawowa gida a masallacin zai tsaya yai ta azkar da tasbihinsa har a kira sallah isha'i.
Da wuri ya bi lafiyar gado saboda ya samu tashi da wuri domin jirgin da zai bi zai tashi ne by 7am.
(Ku ji tsoron Allah da ya hallacinku ku daina karantawa idan ba ku biya ba, ku guji hakkin wani dan Allah baya yafe hakkin wani akan wani, daka ci hakkin wani kara a ci naka, ko ba komai kasan kai ka bi shi bashi ba wai shi ya bi ka ba, kuma zai biyaka a inda ba a abiya da nera sai lada ko zunubi. Indai har za ki karanta ki karu ko kuma ki samu nishadi to miye na hassadar ko kyashin biya? Masu sharing ku cigaba da yi kowa yai na gari dan kansa, wata rana sai labari duk abun da ka aikata shi zaka gani, kuna ganin abun kamar ba komai ba ko? To Allah ya baku sa'a ya muku yadda kuke mana🙌😊)
FALMATA POV.
Bata koma ba sai kusan tara har da yan mintuna, taji tsoro sosai domin bata saba tafiyar dare ba da nisa haka sai a yan kwanakin nan da fara kaiwa dare, bata baro gidan sai yaran sun yi bachi ta kwantar da su sannan zata kamo hanyar gida.
Ta iso a gajiya sosai sai dai tararda Sani da tai a kofar gidan yana jiranta sai ya saka ta manta da gajiyar. Sai da ta fara shiga gida ta sanar da Tumba isowar ta.
“To kije waje wani na nan yana jiranki, sauran idan ya baki kudi ki boye ki shigo min hannu sake�
Falmata bata ce komai ba ta juya ta fice daga gidan, saman dakalin dake kofar gidan ta suka zauna duk maganar da zai yi sai dai ya kai bakinsa kunnenta ya fada mata, kamin ya kumna matar wata tsohuwar wakar M2, tana kallon video wani shauki na dibanta, har ta dago kai ta fada masa cewar ta hadu da M2 ba sau daya ba sai kuma wata zuciyar ta hana ta waya ni ko shi ma ya karyatata kamar yadda sauran kawayenta su kai. Sai goma har da yan mintuna yai mata sallama ya tafi be bata ko sisi ba. Da fargaba da shiga gida domin ta san ko ta fadawa Tumba ba a bata komai ba ba yarda za tai ba. Sai da tai ta mata rantsuwa kamar za tai kuka sannan ta kyaleta sai masifa take.
“Idan ya san baya bada komai ya daina zuwa, ki sallame shi kawai�
“To�
Falmata ta amsa sannan ta shige dakinsu jikinta na rawa. Washe gari ma kamar kullum sai da ta gama gyara gidan sannan ta shiga dakinsu ta dauki karamin qur'anenta na hadda ta saka hijabinta ta fito tai ma Tumba sallama ta kama hanya tana ta kallon Naja dake shirin makarantar boko. A zatonta yau ma zata hadu da Iya kamar kullum amman sai gata wayau babu Iya a waje har ta isa cikin gidan ta hau sama ta kwankwasa kofar babu bata lokaci aka bude mata. Sai da ta gaishe da duka hadin da suke falon sannan ta wuce dakin yan uku ta fara aikin.
Misalin tara da rabi ta gama komai sannan ta dauko yaran ta fito da su domin ayi musu wanka.
“Ba a fitowa da su Falmata ki koma dasu dakin, sai kije ki kira Iya tai musu wanka tun ni ban gama aikin ba, na san Shattima be son jira Ammy tace a gama masa komai kamin ya iso zuwan safe zai yi�
Falmata ta jin Jekadiya ne kawai ba dan ta fahimci waye Shattiman ba balle, juyawa tai ta koma cikin dakin ta aje yaran sannan fito.
“Ina ne dakin Iya yake?�
Jekadiya ta umarce wata hadima da kai Falmata a bangaren Iya wanda bangare daya suke da Jekadiya da wasu manyan hadima gidan. Hadimar na gaba Falmata na binta a baya sai karanto addu'a take, sai da suka sauka kasa, suka fita daga bangaren Ammy gaba daya sannan suka isa wani madaidaicin part.
Bakin kofar Iya hadimar ta tsaya ta kwankwasa mata kofar sannan ta wuce ta bar Falmata a tsaye.
“Kin gani ba ni san mutanen nan basa taba mana karya�
“Ada can ina ganin abun kamar wasa, amman ganin wannan yarinyar ya bani tsoro kuma ya saka na yarda, yanzu miye mafita?�
“Mafita kawai a koreta daga gidan mana, babba ce?�
“Karama ce ba zata wuce warin Nana ba, ni abun ya bani mamaki ma, taya zata iya lalata mana aiki? Ko dai tana da aljanu ne?�
“Ko ma dai minene abun da nake ganin yafi kawai a koreta daga gidan, matukar tana cikin gidan nan zata bata maka lamari da tsari�
“To amman ya za ayi na koreta tun da bangarena take ba?�
“Haba Hajiya kamar ba mace ba, ki yi tunani mana, ni anjima zan shiga na gaishe da Hajiya dan na ga yarinya�
“Okay shikenan ai dole mu san abun yi kam�
Ta sauke wayar tare da sauke ajiyar zuciya tana tuna sauran abubuwan.
“Fadime Falmata Sardauna, wacece Fadime kuma? Waye Sardauna?�
Ya mike tsaye tana ta tunani.
“Sun ce akwai tafiyar da ba dawowa? Wace tafiya ce kenan? Wa zai yi? Mu ko kuma bangaren Ammy?�
Safa da marwa ta fara yi a dakin.
“Ina kyautata zaton yarinyar tana da aljanu ne wata kila zata fada ne, in ba shi ni ban ga ta inda zata iya lalata mana shiri ba? Kamata yai nai mata sanadi da gidan nan cikin ruwa sanyi ko kuma ayi mata asiri ta bar gidan gaba daya�
Sai kuma ta girgiza kai.
“No ai idan mu ka mata asirin idan tana da aljanu zata iya fadar gaskiya ta tona mana asiri�
Wayarta ta nufa ta kira Hajiya Talatu ta labarta mata abunda yake faruwa.
“Wannan maganar ba ta waya bace ranki ya dade zan shigo gobe da kaina�
Daga haka ta aje wayar, gaba daya ta rasa yadda zatai ta natsu, haka ta wuni cikin tunani kala kala ta kulla wannan ta kwance wacan ta saka wannan ta ga be yi ba, babu abun da yafi tsaya mata a rai kamar yadda Falmata zata lalata musu shiri as how kuma ta yaya? Lokaci bayan lokaci sai ta ambaci sunan Falmata Fadime Sardauna tana jinjina lamarin.
SHATTIMA POV.
A kofar gate din Hajiya a mutu ya faka motarsa duk kuwa da kasancewar Zainab ba son zuwa gidan domin yan uwan Hajiya Babba ne ita kuma ba wani shiri take da Hajiya Babba balle kuma yan'uwanta.
“Ina jin gobe zan je Yola, zan turo miki number police din da za su raka ki a can idan kin shirya kawai ki kira su zasu same ki har inda kike�
Zainab ta kalleshi.
“Amman Lafiya zaka je gobe? Ko ka sake samun hutu ne?�
“Baba Waziri ne yace yana son ganina, ya kira ni da safe yace idan zai yiyu mu hadu da a yau, nace masa sai dai gobe�
“Okay Allah ya tsare, ni ba zan dade ba, domin bana jindadi sosai kuma ina son na gama cikin kwana biyu koma�
Hannunsa ya mika ya dauko diary sa yai rubutu a kai ya cire paper ya mika mata.
“Ki ba wani ya karbo miki wannan maganin�
“Thank you�
Ta fada bayan ta karba, sannan ta bude motar ta bita, sai ya jira ta dauki akwatinta dake boot sannan yaja motarsa ya dauki hanyar asibitin, gaba daya wunin ranar daya tuna abun da Fadime ta saka Ra'ees sai yai murmushi, sai yana daf da tashi aikin sannan ya kira Ra'ees a waya bugu daya abokinsa ya amsa.
“Hello�
“Matsoraci�
“Uhmm Allah yasa kaji abun da naji, ba zaka gane ba ne Wallahi�
Shattima yai murmushi kasaita wanda ya karawa fuskarsa kyau da kwarji sannan ya sake magana a hankali.
“Gobe dai zaka yi duty na, zan leka Yola�
“Lafiya dai?�
“I don't know, Baba Waziri ke nema kuma tun har ya bukaci ganina kasan abu ne mai muhimmanci�
“Allah yasa alheri ne ya tsare�
“Amin�
Ya aje wayar har sai da Ra'ees ya kashe da kansa sannan ya mike tsaye ta hada komai nasa ya zuba a karamar jakarsa ta riko system dinsa ya fito daga office din.
Kai tsaye gida ya dawo daman can indai baya gida to yana gurin aiki dan kuma baya aiki to yana gida sai kuma idan wata fitar mai muhimman ta kama, domin shi ba mutum ne mai son yawo ba.
After sallah la'asar ya fito falon ya zauna yana kallon tv, be yi minti talatin ba ya soma jin laurarsa na son tashi, daman can indai zai zauna shi kadai a gurin yana tunani to zai haifar da kansa da matsala ne, cikin rashin kuzari ya mike tsaye ya shiga kitchen ya dauko cup ya ciro lemun tsaki a fridge ya yanka ya matsa a cup din ya jika Lipton ya hada ya shanye sannan ya fito ya hau sama zuwa bedroom dinsa. Wanka ya fara yi sannan ya kwanta saman katon bed din nan da nan bachi yai gaba da shi.
Be farka ba sai da aka fara kiran sallah magari, sannan ya unkura ya shiga bandaki a nan ma sai da ya sake watsa ruwa dan jin yai jikinsa ya masa nauyi sannan ya fito ya nufi masallacin unguwarsu. Ba dawo gidan ba sai after isha'i, daman can idan yai sallah magariba baya dawowa gida a masallacin zai tsaya yai ta azkar da tasbihinsa har a kira sallah isha'i.
Da wuri ya bi lafiyar gado saboda ya samu tashi da wuri domin jirgin da zai bi zai tashi ne by 7am.
(Ku ji tsoron Allah da ya hallacinku ku daina karantawa idan ba ku biya ba, ku guji hakkin wani dan Allah baya yafe hakkin wani akan wani, daka ci hakkin wani kara a ci naka, ko ba komai kasan kai ka bi shi bashi ba wai shi ya bi ka ba, kuma zai biyaka a inda ba a abiya da nera sai lada ko zunubi. Indai har za ki karanta ki karu ko kuma ki samu nishadi to miye na hassadar ko kyashin biya? Masu sharing ku cigaba da yi kowa yai na gari dan kansa, wata rana sai labari duk abun da ka aikata shi zaka gani, kuna ganin abun kamar ba komai ba ko? To Allah ya baku sa'a ya muku yadda kuke mana🙌😊)
FALMATA POV.
Bata koma ba sai kusan tara har da yan mintuna, taji tsoro sosai domin bata saba tafiyar dare ba da nisa haka sai a yan kwanakin nan da fara kaiwa dare, bata baro gidan sai yaran sun yi bachi ta kwantar da su sannan zata kamo hanyar gida.
Ta iso a gajiya sosai sai dai tararda Sani da tai a kofar gidan yana jiranta sai ya saka ta manta da gajiyar. Sai da ta fara shiga gida ta sanar da Tumba isowar ta.
“To kije waje wani na nan yana jiranki, sauran idan ya baki kudi ki boye ki shigo min hannu sake�
Falmata bata ce komai ba ta juya ta fice daga gidan, saman dakalin dake kofar gidan ta suka zauna duk maganar da zai yi sai dai ya kai bakinsa kunnenta ya fada mata, kamin ya kumna matar wata tsohuwar wakar M2, tana kallon video wani shauki na dibanta, har ta dago kai ta fada masa cewar ta hadu da M2 ba sau daya ba sai kuma wata zuciyar ta hana ta waya ni ko shi ma ya karyatata kamar yadda sauran kawayenta su kai. Sai goma har da yan mintuna yai mata sallama ya tafi be bata ko sisi ba. Da fargaba da shiga gida domin ta san ko ta fadawa Tumba ba a bata komai ba ba yarda za tai ba. Sai da tai ta mata rantsuwa kamar za tai kuka sannan ta kyaleta sai masifa take.
“Idan ya san baya bada komai ya daina zuwa, ki sallame shi kawai�
“To�
Falmata ta amsa sannan ta shige dakinsu jikinta na rawa. Washe gari ma kamar kullum sai da ta gama gyara gidan sannan ta shiga dakinsu ta dauki karamin qur'anenta na hadda ta saka hijabinta ta fito tai ma Tumba sallama ta kama hanya tana ta kallon Naja dake shirin makarantar boko. A zatonta yau ma zata hadu da Iya kamar kullum amman sai gata wayau babu Iya a waje har ta isa cikin gidan ta hau sama ta kwankwasa kofar babu bata lokaci aka bude mata. Sai da ta gaishe da duka hadin da suke falon sannan ta wuce dakin yan uku ta fara aikin.
Misalin tara da rabi ta gama komai sannan ta dauko yaran ta fito da su domin ayi musu wanka.
“Ba a fitowa da su Falmata ki koma dasu dakin, sai kije ki kira Iya tai musu wanka tun ni ban gama aikin ba, na san Shattima be son jira Ammy tace a gama masa komai kamin ya iso zuwan safe zai yi�
Falmata ta jin Jekadiya ne kawai ba dan ta fahimci waye Shattiman ba balle, juyawa tai ta koma cikin dakin ta aje yaran sannan fito.
“Ina ne dakin Iya yake?�
Jekadiya ta umarce wata hadima da kai Falmata a bangaren Iya wanda bangare daya suke da Jekadiya da wasu manyan hadima gidan. Hadimar na gaba Falmata na binta a baya sai karanto addu'a take, sai da suka sauka kasa, suka fita daga bangaren Ammy gaba daya sannan suka isa wani madaidaicin part.
Bakin kofar Iya hadimar ta tsaya ta kwankwasa mata kofar sannan ta wuce ta bar Falmata a tsaye.