← Book details Fulani Psrt 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 161 OF 172

Sashe 161

Fulani Psrt 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ya fashe da kuka, daman tun da hankalinsa ya dawo yake cikin damuwar abubuwan da ya aikata, Falmata ma hawaye take, Tumba na kukan nadama da dana sani.

“Na tabbatar idan na mutu a halin nan, sai Allah ya hukunta ni domin yaya ma suna da hakki akan uwaye kamar yadda uwaye suke da hakkin akan yaya�

Falmata ya matsa kusa da shi tana hawaye.

“Ba halinka ba ne Baba, da can ba haka kake mana ba, idan har akwai wani hakki nawa da yake kanka Wallahi n yafe maka shi duniya da lahira, kuma ina rokon Allah wanda ke tsakaninka da Mama ya daukar maka, na jidadi Baba yanzu ka gane gaskiya�

“Hakika ba hali ba ne, halin wacan bakar matar ne, tun da ta shigo rayuwata komai ya lalace min, dangina ma yaushe rabon da na je ganinsu? Ta zallumci ni ta cutar da ni, na sa na ci amanar uwar yayana kuma na ci amanar yayana, Allah ya isa tsakani da ke Tummmba Tummmba Allah ya tsine miki albarka, yarana kuma da kike ikirarin ba ki iya zama da su zan dawo da abuna cikin gidana kina da rai zaki gan ni da wata matar na auro mai son yayana, ke kuma Allah ya tsine miki albarka, babu irin cin amanar da ba ki yi ma yarinyar nan ba, babu kalar sherin da ba ki mata ba, kuma ni ma kika min, ina jin son yata a zuciyata ina tausayinta amman ban isa na nuna ba�

Tumba ta hade hannayenta biyu tana wani irin kuka da bata taba mafarkin zata yi ba, domin ko a lokacin da hadarin ya faru hankalinta ya bace bata san zafin ciwon da bakincikin cirewar da kafarta tai ba sai daga baya, sai abun ya zame mata kukan zuci wanda ya fi na idanuwa zafi da bakinciki, domin ta rasa kafarta ga hannu kuma sai ruwa yake.

“Malam ka dubi girman Allah ka yafe min, dan'adam ajizi ne�

“Ajizo na ce Ajizo, da can ba ki san da haka ba sai yanzu da Allah ya kama ki? Ai ko wannan kadai ya isheki ishara, ga shi nan baki ga hannu ba ki ga kafa, kuma yarinyar da kike ma fatan sheri gata nan kin jefata cikin alheri ba tare da kin sani ba, ba ki isa ki hana abun da Allah yai mata ba, gashi ijaba nan kin gani Allah ya kaita a matsayin da babu wanda ya taba taka shi a cikinmu, Allah yai miki albarka Falmata ke kuma Tumba Allah ya tsine miki, kuma Wallahi babu ni babu ke daga yau daman can ba ni wani rabon mugun iri dake, ki hada komai na ki bar min gidan na saki�

Naja ta fashe da wani irin kuka ta rugo da gudu ta zube gabansa.

“Baba dan Allah kai hakuri�

“Ni ba ubanki ba ne, tafi can ki nemi ubanki kuma na kara mata saki daya ya zama biyu�

Tumba ta daga hannunta nan daya ta fashe da kuka tana ihun da duk wanda ke makotaka da su a kusa zai ji.

“Ba ki shiga uku ba, tukuna nan yanzu na kara miki wani sakin daya sai ki shiga ukun, kuma ina rokon Allah ya tsine miki albarka�

Falmata ta rufe baki da sauri jiki na rawa jin irin sakin da Baba ya jerawa Tumba a take. Kukan da take ne yasa makota suka rika shigowa suna tambayar ba'asi, Baba abun da Baba ya boye daga kan abubuwan da take saka shi yana yi har zuwa wanda take yi ma Falmata, sai a lokacin ne mutane suka san gaskiyar abun da yake faruwa, domin kowa yana mata kallon mutuniyar kirki saboda yadda take nunawa Falmata kauna a gaban idon mutane kamar zata hadeye ta, babu abun da ya bawa mutane mamaki kamar maganar auren Falmata, a nan wasu suka yarda domin kowa yayi mamakin jin Falmata zata auri tsoho yarinya kyakkyawa kuma mai kananan shekaru. Duk wanda ya shigo gidan ya ji abun da ya faru sai mamaki ya kama shi, gashi babu bakin bada hakuri domin mai faruwa ta faru Baba ya riga ya aikatawa Tumba mai gaba daya. Tumba kan kuka kawai take tana fadin ta shiga uku amana ta kamata, Falmata bata labarta musu wanda take aure ba balle su san fittacen mutum ne, sanin yaro ne yai shigar tsofi ma Baba ne ya fada, Naja kuma ana ciki kuka da jimamaki hakan yasa babu wanda ya san Sirleem ne, sai hakan be hanata zama abar kallo ba saboda tufafin jikinta da kuma gidan da aka kaita domin duk wanda yajr walimarta ya ga gida abun da ake kira da gida, har wadanda ba su je ba ma sun samu labarin irin gidan da aka kai Falmata.
Sai kusan goma na dare Falmata tai ma Baba sallama yana ta saka mata albarka, yana mata addu'a har da hawayensa har lokacin yana jin bakinciki da nadamar abun da ya aikata. Sai bayan da Falmata ta wuce ne ya duba kayan da Sirleem ya bashi ya ga turaruka masu tsada da kamshi gaske ga kuma kudin da za su haura 70k a ciki.

“Allahu Akbar Allah na gode maka da ka nuna min wannan ranar, Allah kai mata albarka�

Ya fada yana share hawayen idonsa. Falmata ta isa gurin da Sirleem ya aje motarsa tana hawaye, tana jin kamar ace mahaifiyarta tana raye ta ga wannan ranar, ta dayan bangaren kuma zuciyarta na cike da farincikin dawowar Baba a hayyacinsa, tana taba motar sai Sirleem ya mika hannunsa ya bude mata motar ta shiga ta zauna ta rufe. Sirleem na kallonta ya san akwai wani abu, hannunsa ya kai ya kama hannunsa ya dora a kirjinsa.

“Haba dai karki ce min tausayin matar can kike�

Ta kalleshi.

“Baba ya sake ta, ta rasa kafarta kuma hannunta yana ruwa�

“She get what she deserved�

“Rayuwa abar tsoro ce Baby, wani lokacin Allah yana kyale bawa yai ta abun da yake so, idan ya tashi taba shi kadan zai taba shi amman sai ya zama abun tsoro, duk da irin makircinta bata hana Allah yi min abun da ya kaddara min ba, kuma gashi ta fara riskar sakamakonta tun a yanzu bayan hukuncin da zata je ta tarar a lahira�

Ta lumshe ido hawaye na sauko mata.

“Daman duk wanda za ayi wa hassada ko kuma a cutar da shi, to zai yi ta samun cigaba ne, kuma zai ga riba hakuri a duniya kamin ya riski ladar lahira, I love you...�

Bude idon tai ta kalleshi sai ta ji wani irin farinciki ya lullubeta marar misaltuwa.

“Alhamdulillah�

Ta furta sai ya ari numfashinta.

“Yeah Alhamdulillah da Allah ya ba ni mata irinki�

Ta yi murmushi shi kuma ya tashi motar yana tukawa da hannun daya yayinda dayan hannunsa yakr rike da hannun babynsa, time to time yake kissing din hannun kamar wani abun da ya zame masa dole. A zatonta gida za su wuce kai tsaye sai ta ga sun dauki hanyar zuwa Family house din su Hajiya Babba wato inda take zaune a yanzu, this is the second time da zai kaita gidan bayan zuwansu na farko a lokacin da ake shirye shirye fitar da Hajiya Babba India, ya je tare da Falmata ya nemi yafiyarta Falmata kuma tai mata bankwana, a lokacin Falmata ta yi zaton Hajiya Babba zata mata wulakanci ne ko ta mata wani abun, sai dai babu ko daya ta kanta take ma, kana ganinta kasan tana cikin ciwo, a Lokacin kam Sirleem ya shiga cikin tashin hankali sosai wanda ya saka Falmata ita ma ta shiga damuwa ganin mijinta ma a cikin damuwar, kusan kullum idan ya taso daga aiki sai ya je gurin Hajiyar, kuma be fasa bacin rai ba saboda halin da ta koma, bata iya komai da sashenta daya, bakinta kuma yaki dawowa daidai, komai take ci sai ya zubo mata ta gefen bakin haka ma yawu ke sauko mata gwanin tausayi, gaba daya ta canja kamar ba ita ba, cikin kankanen lokaci jikinta ya koma kamar na tsofi, sau uku ana fitar da ita waje amman babu wani canji kuma idan sun auna basa ganin komai, Jurry kam sau daya aka fitar da ita saboda ciwon kan da ya saka ta gaba nan suka ce ba su ga komai ba, ana dawowa da ita sai abun ya kara kamar an takaloshi sai ya taba kwakwalwarta har ta kai tana yin wadansu dabi'u da halaye irin na masu tabin hankali, zata zauna ayi fira da ita cikin mutune sai dai da an fara zata fara barin zance tana dariya irin na masu fama da hauka, hakan ya saka komai na rayuwarta ya tsaya cak bata fita ko'ina daga gida sai gida.
Sirleem yayi bakin harabar katon gidan da ya kusa gida ukun wani mutum, sannan ya bude motarsa ya fita kamin ya zagayo har Falmata ta bude ta fito.

“Ba mu siya mata komai ba�

“Babu abun da babu a cikin gidan nan, babu abun da zata nema ta rasa, ni kaina wani lokacin sai na rasa abun da zan riko mata, saboda ba komai take iya ci ba�

Sirleem ya bata amsa sannan ya nufi kofar shiga Falmata na biye da shi a baya, suna shiga falon yan jikokin gidan suka fara musu sannu da zuwa, sai ya rika daga su yana saukewa, sannan ya shiga ciki ya gaisa da wadanda suke manyansa Falmata ma ta gaisa da su kana ya nufi bangaren da dakin Hajiya Babba yake, domin bangare aka ware mata mai komai a ciki har da yar aikinta ita ke mata komai har abinci hakan kuma idan akai na gida gaba daya za a dauko a kawo mata a falonta. Kausar da Karima dakinsu daya, Jurry ce kawai ke da daki dabam saboda yanayinta. Da sallama ya shiga Kausar din ta amsa masa tana murmushi kana ta kalli Falmata.

“Anty Fateema sannunku da zuwa�

Falmata ta washe mata hakora tana jin girman da ta bata har cikin ranta.

“Kauwa Kausar ya gida?�

“Lafiya Kalau�

Kai tsaye Sirleem ya wuce dakin Mahaifiyarsa, Falmata kuma ta zauna a falon tana kallon katon Plasma, Kausar taje ta dauko mata ruwa da lemu ta aje mata.
Chapter 161 · 0% Book details