Sashe 122
Fulani Psrt 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Tsaya ka ji�
“Babu abun da zan ji, bana jin komai a yanzu, na dade ina jiran zuwan wannan ranar, na y iya kokarina wajen hana kaina haram, yanzu kuma na samu halal sai na hana kaina? No way�
Ya fada yana kai bakinsa ajikinta, light kiss yake aika mata hannayensa duka biyu suna mika mata sakonsa, akwai tsoro sosai a tare da ita na sakon da jikinta ya kasa dauka balle ya sakewa kwakwalwarta, sai dai ta samu natsuwa sosai a lokacin da yatsunta da na shi suke tarayya...
Ya so ya saurareta, sai dai ko kadan zuciyarsa bata kusanto masa ta tausayinta ba ta wannan fannin, ko da wasa zuciyarsa bata raya masa yayi kusa ba, kamar yadda yake ganin safiyar ta yi masa saurin wayewa, a lokacin ne ya tabbatar lallai shi ango ne, kuma ya dade da barin abun da ya kamata ace ya san muhimmanci tun da dadewa, ita kanta Falmata ta san ba karamin jihadi tai ba na barin jikinta ya karbi bakon lamari da be taba ba, ta yi kuka sai dai kuka tai irin na masu hakuri da danne cuta a zuci, bata bar ihunta ya fito ya cika dakinta ba, babu abun da take ambato sai Allah zuci da baki. A daren ranar Falmata ta san me ake kira da aure, ta gane banbanci ta da da, ba kasanta kadai ba ko kirjinta da be gama nina ba ciwo yake mata sosai. Idonta biyu har akai sallah asuba tana jin lokacin da ya shiga bandakin yai wanka ya fito ya kabbarta sallah asuba, bayan ya gama sallah ya nufo inda take ya kai hannunsa ya shafa fuskarta. A zatonsa bachi take domin idonta a lumshe suke, bakinsa ya kai ya sumbanci goshinta yana jin kamar yaja bukatar kari, sai da ya san ba zata iya ba, shi kansa ya sha wahala kamin Falmata ta maida shi cikakakken namiji.
HAJIYA BABBA POV.
Suna zaune a gidan Hajiya Tatula har kusan magariba, sannan matar ta iso tare da bokanyar a cikin motar kasuwa. Kofar Kicin Hajiya Talatu ta bude musu suka shigo sannan ta shigar da su wani dakin da bata cika amfani da shi ba, kana ta shigo dakinta ta sanarwa Hajiya Talatu da Jurry isowar matar.
Kamin Hajiya Babba tai wani yunkuri Jurry har ta kai tsaye domin hankalinta a mugun tashe yake, ko da Hajiya ta isa dakin ta samu Jurry da Hajiya Talatu a zaune gaban matar sua gaisawa, kallo daya zaka mata ka san akwai manyan kuma gawurtattun aljanu a kanta. Idonta a tsaye yake ga tufafin jikinta ma ba irin na mata ba ne, wando da riga ne na maza sai hijabin da ta dora akai, tana tare da wata katuwar jaka a gafe sai warin turaren aljanu take.
Hajiya da kanta ta mika mata gaisuwa, ta amsa tana wani gyatsa kamar wanda ta sha lemu mai gas.
“Baiwar Allah, ina cikin matsala....�
Tun daga a har za sai da Hajiya Babba ta labarta mata komai na zuwan da sukai garin su Wasim da abubuwan da aka fada musu da kuma abubuwan da suke gani.
“Kudi ake ba ni ko naira biyar ce a miko min sai na dubo muku abun da kenan�
Hajiya Talatu ta tashi da sauri taje ta dauko dari biyu ta mika mata, sai ta karba tana gyatsa, ta bude jakarta ta dauko kwalbar turare ta madara ta kurba kadan ta shafa kadan a kudin ta mursa a hannunta sannan ta dauko goro ta tauna ta cire hijabin da ke jikinta, ta dauko wani abu mai kamar duba da wasu yan duwatsu a ciki tana kadawa.
“Gaishe dai nake Inna kirarinki nake, inna mai uwa da da, inna mai cin uwa ta ci danta, jini na ki dan mutum na ki, idan kin ga dama ki cinye kafar yaro ko hannunsa, doguwa matar kure, jini na ki tsoka ta bayinki, inna gwarzuwa kowa yayi kira sai ya ganki...�
(Irin wannan aljanar ita wasu suke kira da Inna, wasu kuma su ce mata doguwa, wasu kuma su ce mata uwa, idan ana son kashe mutum ko yi masa wani mummunnan aiki ita ake kira, wasu mutanen ma da ita suke maita, ko kadan bata da tausayi ba bata da imani, idan tana tare da uwar yaro zata shanye kafarsa ko hannunsa ko ta juya kwakwalwarsa haka take yi ma yaran mace idan tana tare da uwar, kuma jini take sha, ko da wasa kai mata kirari ka kirata sai ta zo sai dai be zama lallai ka ganta ba, Allah ya tsare mu)
Bata gama kirarin ba jikinta ya fara rawa, ta fara gyatsa fiye da ta dazun, sai lausayar da kai take can kuma yawu ya fara mata zuba, muryarta ta canja.
“Ga ni ma iso, mai shiga kogo in hau tsani, in ci sha jinin mutum in bar tsaka, ga uwa mai ciwa ta ci danta, kashe ta kuke son ayi?�
Hajiya Talatu da Hajiya Babba sun kalli juna, sai jurry ta girgiza kai.
“Aa a dai mata wani abun dabam, ba kisa ba�
Ta furzar da goron da ke bakinta.
“Idan ba a kisa ba a rike hannu ko kafa, idan ba jini za a sha ba, ku bar kiran Inna Inna mai hadari ce, wannan aikin sai duna bakin iska...�
Gaba daya tsoro ne ya kama su, jurry ta ja baya. Cikin dakiya Hajiya Babba ta ce.
“Ina zamu ga duna?�
“Yanzu zan turo muku shi�
Ya fara wani rangaji tana birkice ido, sosai jikin matar yai tsami saboda fitar inna. Fita tai daga jikin matar sannan bokanyar ta farka ta dauko wani turare binta sudan tare da danduwala ta hada guri daya ta murza a hannunta tashaka, take muryata a sauka jikinta ya amsa kiran Duna wanda wasu suke ki kira da junnul ashiq, duna gawurtaccen aljanine ga sauri da karfi ta keta, ba ko wane aljani ke iya karawa da shi ba, hakan yasa idan ya shiga jikin mace kamin ayi mata maganinsa sai ta sha wahala sosai, ayoyi ne kadai abun da ke nisantar da shi daga jikin dan'adam, idan kuma akai aiki da shi yana da wahala mutum yayi saurin warwarewa sai an kira shi an bashi kwatankwacin abun da wadancan mutanen na farko suka ba shi sannan ya rabu da mutum, aikinsa kuma sha yanzu ne magani yanzu matukar an bashi abun da yake so, sai dai komai karfin aljani yana tsoron bakara da ayatul kursiyo, matukar mutum na karanta su basa kusantarsa idan ma suna tare da shi za su nisanci mutum indai har an dage, domin idan aka karanta baqara har kashe a gida sai gidan yayi wata daya aljani ko wani abun cutarwa be kusanci gidan ba, amman sai idan ba a shan waka ko wani abun da baya haduwa da kur'ane.
Sai da yai ma kansa kirari yai gyatsa yana kankance ido fuska babu annuri sannan yace.
“Za ku siye kwaryar zuma, ku siye bakaken zakaru guda ba bakwai, sannan ku siye bakin sa, kuma ku samo dutsen tsakar hanya�
“Ina zamu iya neman wannan abun, idan aka ga muna nema, ai sai asiri ya tonu ace wani abun muke shirin yi, ina laifin mu bada kudi a nemo idan zai yiyu�
Cewar Hajiya Talatu ta sigar roko, ya daga idonsa kadan ya kalleta.
“Zaku biya dubu dari uku har kudin aiki�
“Ba matsala, ni dai a ayi aiki kar asirinmu ya tonu�
Hajiya Babba ta dora da nata sai ya maida dubansa gurinta.
“An gama, gobe gobe aiki na babbatuwa in dai kun biya kudi�
“Yanzu nan zan saka aje a ciro kudi a bata da yardar Allah mun gode�
Ya rufe ido yana wani fisgar jiki, sai ta fadi kasa kwance baki na fitar da kumfa. After like 5 min ta bude ido ta tashi zaune.
“Sannu�
Duk suka ce mata sai ta amsa tana yamutsa fuska tana gyara. Jurry ta mike tsaye.
“Bari na je na ciro kudin na kawo�
Kamin hajiya ta amsa ta ta nufi kofar ta bude ta fita da sauri, sai da ta kawo kudin sannan matar ta tafi, Hajiya da Jurry kam ba su bar gidan ba sai da aka kira sallah isha'i.
TUMBA POV.
A daren ranar kasa bachi tai, tunani kala kala ya zo mata a rai, tsohon ne da gaske ko kuma wani ne yai siffar tsofin? Idan na tsohon ne indai har arzikinsa yayi yawa be kamata Falmata ta aure shi ba, Naja ta dace da shi duk da kasancewarsa tsoho. Abun ta tarar da kuma abun da ta gani be mata dadi sam. Idan har akwai wanda ta cancanci wannan uban dukiyar to yarta ne, miyasa ya boye cewar yana da arziki shi ne abun da yafi tsaya mata a rai. Wanene shi ma ai ya kamata a sani tun farko.
Kusan bachinta rabi ne, rabin duk tunani ne da nazari, washe ta kasa karyawa da komai, sai samun Baba tai a can gefe tana tsegunta masa.
“Maganar gaskiya Malam a kara bincike a kan yarinyar nan, kar ya zama mun aurar da ita ga mutumen banza, tsakani da Allah ni dai zuciyata bata kwanta da shi ba, ka ga irin dukiyar da na gani a gidan nan? Da Wahala idan ba yankan kai mutumen yake ba, idan ba haka ba miyasa tun farko be kai mu gidansa na gaskiya ba ya ka mu wani shegen gida, kuma jiya ina jin su Ramatu na fadin wai har 200k ya abokansa suka ba su na siyen baki duba ka gani har fa dubu dari biyu Malam�
Baba yayi shiru yana nazarin maganar ta, tana da gaskiya in dan gaskiya domin mai gaskiya baya boyo, be kamata ya boye komai.
“Ni kaina na yi wannan tunani, amman wai gidan babba ne sosai�
“Malam kasan gidan tsohon ciyaman? To wane shi wannan ya ci ubansa, ga haske ko'ina kuma kare da karau wannan ma fa gidan sama ne, ga wasu manyan kujeru, anya mutumen kwarai mai tarin dukiya kamar wannan sai yarda ya auri yar talakawa irin Falmata? Ai sai dai yar manyan mutane�
“Babu abun da zan ji, bana jin komai a yanzu, na dade ina jiran zuwan wannan ranar, na y iya kokarina wajen hana kaina haram, yanzu kuma na samu halal sai na hana kaina? No way�
Ya fada yana kai bakinsa ajikinta, light kiss yake aika mata hannayensa duka biyu suna mika mata sakonsa, akwai tsoro sosai a tare da ita na sakon da jikinta ya kasa dauka balle ya sakewa kwakwalwarta, sai dai ta samu natsuwa sosai a lokacin da yatsunta da na shi suke tarayya...
Ya so ya saurareta, sai dai ko kadan zuciyarsa bata kusanto masa ta tausayinta ba ta wannan fannin, ko da wasa zuciyarsa bata raya masa yayi kusa ba, kamar yadda yake ganin safiyar ta yi masa saurin wayewa, a lokacin ne ya tabbatar lallai shi ango ne, kuma ya dade da barin abun da ya kamata ace ya san muhimmanci tun da dadewa, ita kanta Falmata ta san ba karamin jihadi tai ba na barin jikinta ya karbi bakon lamari da be taba ba, ta yi kuka sai dai kuka tai irin na masu hakuri da danne cuta a zuci, bata bar ihunta ya fito ya cika dakinta ba, babu abun da take ambato sai Allah zuci da baki. A daren ranar Falmata ta san me ake kira da aure, ta gane banbanci ta da da, ba kasanta kadai ba ko kirjinta da be gama nina ba ciwo yake mata sosai. Idonta biyu har akai sallah asuba tana jin lokacin da ya shiga bandakin yai wanka ya fito ya kabbarta sallah asuba, bayan ya gama sallah ya nufo inda take ya kai hannunsa ya shafa fuskarta. A zatonsa bachi take domin idonta a lumshe suke, bakinsa ya kai ya sumbanci goshinta yana jin kamar yaja bukatar kari, sai da ya san ba zata iya ba, shi kansa ya sha wahala kamin Falmata ta maida shi cikakakken namiji.
HAJIYA BABBA POV.
Suna zaune a gidan Hajiya Tatula har kusan magariba, sannan matar ta iso tare da bokanyar a cikin motar kasuwa. Kofar Kicin Hajiya Talatu ta bude musu suka shigo sannan ta shigar da su wani dakin da bata cika amfani da shi ba, kana ta shigo dakinta ta sanarwa Hajiya Talatu da Jurry isowar matar.
Kamin Hajiya Babba tai wani yunkuri Jurry har ta kai tsaye domin hankalinta a mugun tashe yake, ko da Hajiya ta isa dakin ta samu Jurry da Hajiya Talatu a zaune gaban matar sua gaisawa, kallo daya zaka mata ka san akwai manyan kuma gawurtattun aljanu a kanta. Idonta a tsaye yake ga tufafin jikinta ma ba irin na mata ba ne, wando da riga ne na maza sai hijabin da ta dora akai, tana tare da wata katuwar jaka a gafe sai warin turaren aljanu take.
Hajiya da kanta ta mika mata gaisuwa, ta amsa tana wani gyatsa kamar wanda ta sha lemu mai gas.
“Baiwar Allah, ina cikin matsala....�
Tun daga a har za sai da Hajiya Babba ta labarta mata komai na zuwan da sukai garin su Wasim da abubuwan da aka fada musu da kuma abubuwan da suke gani.
“Kudi ake ba ni ko naira biyar ce a miko min sai na dubo muku abun da kenan�
Hajiya Talatu ta tashi da sauri taje ta dauko dari biyu ta mika mata, sai ta karba tana gyatsa, ta bude jakarta ta dauko kwalbar turare ta madara ta kurba kadan ta shafa kadan a kudin ta mursa a hannunta sannan ta dauko goro ta tauna ta cire hijabin da ke jikinta, ta dauko wani abu mai kamar duba da wasu yan duwatsu a ciki tana kadawa.
“Gaishe dai nake Inna kirarinki nake, inna mai uwa da da, inna mai cin uwa ta ci danta, jini na ki dan mutum na ki, idan kin ga dama ki cinye kafar yaro ko hannunsa, doguwa matar kure, jini na ki tsoka ta bayinki, inna gwarzuwa kowa yayi kira sai ya ganki...�
(Irin wannan aljanar ita wasu suke kira da Inna, wasu kuma su ce mata doguwa, wasu kuma su ce mata uwa, idan ana son kashe mutum ko yi masa wani mummunnan aiki ita ake kira, wasu mutanen ma da ita suke maita, ko kadan bata da tausayi ba bata da imani, idan tana tare da uwar yaro zata shanye kafarsa ko hannunsa ko ta juya kwakwalwarsa haka take yi ma yaran mace idan tana tare da uwar, kuma jini take sha, ko da wasa kai mata kirari ka kirata sai ta zo sai dai be zama lallai ka ganta ba, Allah ya tsare mu)
Bata gama kirarin ba jikinta ya fara rawa, ta fara gyatsa fiye da ta dazun, sai lausayar da kai take can kuma yawu ya fara mata zuba, muryarta ta canja.
“Ga ni ma iso, mai shiga kogo in hau tsani, in ci sha jinin mutum in bar tsaka, ga uwa mai ciwa ta ci danta, kashe ta kuke son ayi?�
Hajiya Talatu da Hajiya Babba sun kalli juna, sai jurry ta girgiza kai.
“Aa a dai mata wani abun dabam, ba kisa ba�
Ta furzar da goron da ke bakinta.
“Idan ba a kisa ba a rike hannu ko kafa, idan ba jini za a sha ba, ku bar kiran Inna Inna mai hadari ce, wannan aikin sai duna bakin iska...�
Gaba daya tsoro ne ya kama su, jurry ta ja baya. Cikin dakiya Hajiya Babba ta ce.
“Ina zamu ga duna?�
“Yanzu zan turo muku shi�
Ya fara wani rangaji tana birkice ido, sosai jikin matar yai tsami saboda fitar inna. Fita tai daga jikin matar sannan bokanyar ta farka ta dauko wani turare binta sudan tare da danduwala ta hada guri daya ta murza a hannunta tashaka, take muryata a sauka jikinta ya amsa kiran Duna wanda wasu suke ki kira da junnul ashiq, duna gawurtaccen aljanine ga sauri da karfi ta keta, ba ko wane aljani ke iya karawa da shi ba, hakan yasa idan ya shiga jikin mace kamin ayi mata maganinsa sai ta sha wahala sosai, ayoyi ne kadai abun da ke nisantar da shi daga jikin dan'adam, idan kuma akai aiki da shi yana da wahala mutum yayi saurin warwarewa sai an kira shi an bashi kwatankwacin abun da wadancan mutanen na farko suka ba shi sannan ya rabu da mutum, aikinsa kuma sha yanzu ne magani yanzu matukar an bashi abun da yake so, sai dai komai karfin aljani yana tsoron bakara da ayatul kursiyo, matukar mutum na karanta su basa kusantarsa idan ma suna tare da shi za su nisanci mutum indai har an dage, domin idan aka karanta baqara har kashe a gida sai gidan yayi wata daya aljani ko wani abun cutarwa be kusanci gidan ba, amman sai idan ba a shan waka ko wani abun da baya haduwa da kur'ane.
Sai da yai ma kansa kirari yai gyatsa yana kankance ido fuska babu annuri sannan yace.
“Za ku siye kwaryar zuma, ku siye bakaken zakaru guda ba bakwai, sannan ku siye bakin sa, kuma ku samo dutsen tsakar hanya�
“Ina zamu iya neman wannan abun, idan aka ga muna nema, ai sai asiri ya tonu ace wani abun muke shirin yi, ina laifin mu bada kudi a nemo idan zai yiyu�
Cewar Hajiya Talatu ta sigar roko, ya daga idonsa kadan ya kalleta.
“Zaku biya dubu dari uku har kudin aiki�
“Ba matsala, ni dai a ayi aiki kar asirinmu ya tonu�
Hajiya Babba ta dora da nata sai ya maida dubansa gurinta.
“An gama, gobe gobe aiki na babbatuwa in dai kun biya kudi�
“Yanzu nan zan saka aje a ciro kudi a bata da yardar Allah mun gode�
Ya rufe ido yana wani fisgar jiki, sai ta fadi kasa kwance baki na fitar da kumfa. After like 5 min ta bude ido ta tashi zaune.
“Sannu�
Duk suka ce mata sai ta amsa tana yamutsa fuska tana gyara. Jurry ta mike tsaye.
“Bari na je na ciro kudin na kawo�
Kamin hajiya ta amsa ta ta nufi kofar ta bude ta fita da sauri, sai da ta kawo kudin sannan matar ta tafi, Hajiya da Jurry kam ba su bar gidan ba sai da aka kira sallah isha'i.
TUMBA POV.
A daren ranar kasa bachi tai, tunani kala kala ya zo mata a rai, tsohon ne da gaske ko kuma wani ne yai siffar tsofin? Idan na tsohon ne indai har arzikinsa yayi yawa be kamata Falmata ta aure shi ba, Naja ta dace da shi duk da kasancewarsa tsoho. Abun ta tarar da kuma abun da ta gani be mata dadi sam. Idan har akwai wanda ta cancanci wannan uban dukiyar to yarta ne, miyasa ya boye cewar yana da arziki shi ne abun da yafi tsaya mata a rai. Wanene shi ma ai ya kamata a sani tun farko.
Kusan bachinta rabi ne, rabin duk tunani ne da nazari, washe ta kasa karyawa da komai, sai samun Baba tai a can gefe tana tsegunta masa.
“Maganar gaskiya Malam a kara bincike a kan yarinyar nan, kar ya zama mun aurar da ita ga mutumen banza, tsakani da Allah ni dai zuciyata bata kwanta da shi ba, ka ga irin dukiyar da na gani a gidan nan? Da Wahala idan ba yankan kai mutumen yake ba, idan ba haka ba miyasa tun farko be kai mu gidansa na gaskiya ba ya ka mu wani shegen gida, kuma jiya ina jin su Ramatu na fadin wai har 200k ya abokansa suka ba su na siyen baki duba ka gani har fa dubu dari biyu Malam�
Baba yayi shiru yana nazarin maganar ta, tana da gaskiya in dan gaskiya domin mai gaskiya baya boyo, be kamata ya boye komai.
“Ni kaina na yi wannan tunani, amman wai gidan babba ne sosai�
“Malam kasan gidan tsohon ciyaman? To wane shi wannan ya ci ubansa, ga haske ko'ina kuma kare da karau wannan ma fa gidan sama ne, ga wasu manyan kujeru, anya mutumen kwarai mai tarin dukiya kamar wannan sai yarda ya auri yar talakawa irin Falmata? Ai sai dai yar manyan mutane�