Sashe 3
Farrah Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Wani dogon saurayi ne yatashi tsaye fari kal dashi kana ganinshi zakasan shine Modibbo sabida yanda yabi Farrah da kallo kaman yaga abinci, abincin ma gangariya, yana sanye da manyan kaya kal kal dasu babu datti dan Baban shi ne mai gari so sunada kudi gashi shine Magajin mai gari dan shi kadaine dan Maigari namiji, karasowa inda suke aduke gaban rafin yayi yana zuba hannu a aljihu yana kallon Farrah dabama taganshi ba ahankali yace “Farrah” dawani irin sauri daga Farrah har Shafa suka juyo suna kallonshi, hannun Farrah Shafa takama ta iza kan tulun dake cikin rafin tace “rike tulun nan Kurma” sanan tamike tsaye takalli Modibbo tace “Hamma Modibbo kaga bamasan bala’i kuma bama neman fitina karabu da Farrah dan Allah, nasan sabida ita ka kafa majalisa agaban rafin nan dan kasan tana zuwa debo ruwa, inhar kanason Kurma dagaske bazaka dinga jazamata bala’i ba bayan kasan Rakiya sonka take, kumama Hamma Modibbo waye zai barka ka auri Kurma iyye, dan Allah kafita harkan yarinyar nan ka tausaya mata, ka tausayama maraicinta haka mutanen kwarai suke” tunda take maganan yake binta da kallo saida tagama yanuna kanshi cikeda isgilanci yace “wai dani kike Shafa’atu?” Kwashewa da dariya abokanen sukayi ganin rainin wayon da Modibbo yama Shafa, daya daga cikin su yace “Modibbo bakin ciki take ba ita kakeso ba kawarta kakeso” wani mugun kallo Shafa tamai shikuma Modibbo yabi ta gefen Shafan yay inda Farrah take datake kokarin daukan tulun ta daya cika da ruwa zata iza bisa ka ganinshi yasa atsorace tasaki tulun zatai baya dasauri Modibbo yasa hannu yadauki tulun yarike yana kallonta yace “zona iza miki” girgizamai kai tayi ahankali kanta akasa taki zuwa, ahankali yataka zuwa gabanta yana kallon yanda jikinta kerawa sanan yadaura mata tulun aka dawani bala’in sauri kaman mazari tajuya zata wuce yace “bansallameki ba ai” chak ta tsaya batare data juyoba, hannunshi yatura a aljihu sanan yaciro ledan biscuit na Oreo dazun nan aka kawoma Mai gari biscut din daga binni nashine amman yakici dan yabata wani murmushi yakarayi yasan zata fara sonshi dan babu wanda yataba ganin irin biscuit din akauyen nan zuwa yayi tagabanta yamika mata ledan ta kalla sanan ta girgixamai kai ahankali yace “biscuit ne daga binni ki karba kona kama hannunki nasamiki” Shafa tadan kalla kaman zata fashe da kuka ganin haka yasa cikin fushi yace “idan Shafa kesaki tai abu kotahanaki kiyi abu zansa akoresu daga garin nan” akufule Shafa na tattauna baki tace “mafashi” dasauri Farrah tamikamai hannunta jin zaisa akori su Shafa, gently yasamata biscuit din yana murmushi sosai dasauri tawuce Shafa ma ta watsama dukansu harara tawuce shikuma yabita da kallo saida suka bace sanan yakoma inda suke ya zauna yana murmushi abokanenshi sukace “wai kai mezakayi da kurman nan ga hadaddun matan kauyen nan dake mutum maka kanace ma kurman nan mara galihu” wani kalan murmushi yayi yana karban shayin da aka zubamai a kopi kaman mai tunani yace “kap matan kauyen nan babu mai baiwar da kurman nan kedashi” Muji yace “wanan gajeran gata kurma wani baiwa tafi matan garin nan dashi Haba Modibbo Kodai magani tamaka ne” murmushi yayi sosai yadan kurbi shayin sanan Ya hadiye yace “aradun Allah duka kauyen nan babu wanda yakai kurman nan kayan alatu ajiki, ahaka da wahalan da komi kaga kidirmon datake dashi kuwa balle ma nacigaba da bata dadi ina bata su kaza da biscuit’ din binni” yay dan dariya yana sake kurban shayi, tabe baki Muji yayi yace “kaima kasan kozaka mutu kanadai magajin gari baza’ataba barinka ka auri Kurman nan ba, babu wanda yasan ubanta, ance kanjamau yakashe uwarta ma, dataga tana shirin mutuwa ta tattaro da ita da yaran nata suka dawo nan kauye tazo tamutu anan” tabe baki Modibbo yayi yasake kurban shayin yajaye kofin daga bakinshi sanan yadagakai yakalli abokanan nashi daduk suke kallonshi suna jiran amsan shi dan dariya yayi yace “yo uban me kukeso nafadi muku? Kuda kunku kunsan ba aurenta zanba ai hakan yabaku amsan manufata akan kurman” wani kalan kwashewa dukansu sukayi da dariya suna tafi, Tanko yanunashi da yatsa yana kadakai yace “Modibbo, Modibbo anyi dan iska awajen nan wlh” suka kara kecewa da dariya, murmushi Modibbo yayi yace “gobe zaku kawomin ita dakina na gangare idan duhu yayi” tafi sukahau yi, Muji yace “kace kai Modibbo gobe Kwanan ango lahiya lau ne kaida Yar kurman ka” dariya Modibbo yayi yace “dasafe gobe zan kawo mata kwai da cinyan kaza da shayi, nabata dadi tabani kindirmo”.
Tofah jama’a ana wata gawata!
~Sai mun hadu mako nagaba dan jin yanda zata kaya tsakanin Modibbo da Farrah, shin Allah zai kubutar da ita daga hannun Magajin Maigari koko tana ruwa?? Kubiyoni danjin cigaban wanan kayataccen labarin na FARRAH wanda ni M Shakur ke kawo muku dahaka nace Bissalam😘~
💫FARRAH💫
✍🏻M Shakur
Tofah jama’a ana wata gawata!
~Sai mun hadu mako nagaba dan jin yanda zata kaya tsakanin Modibbo da Farrah, shin Allah zai kubutar da ita daga hannun Magajin Maigari koko tana ruwa?? Kubiyoni danjin cigaban wanan kayataccen labarin na FARRAH wanda ni M Shakur ke kawo muku dahaka nace Bissalam😘~
💫FARRAH💫
✍🏻M Shakur