← Book details Auren Wata Tara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 87 OF 92

Sashe 87

Auren Wata Tara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ce "Yaya Kaine Daman Ashe da raban xamu sake ganawa kenan karyace akayi Mana akace an kasheka "Baba na hawaye ya ce"nine da kaina tukur"kafin Kace me Yan uwan baba sun cika Gidan kowa yazo sai yayi kukan farinciki mutumin da daukarsu ya mutu kasa da shekara ashirin da biyar su ganshi yanzu dole suka girgiza Kuma cikin ikon Allah y'an uwan baba duka suna Nan da ransu Basu mutu ba"nanfa Kuma aka Fara yiwa Zahra kallon Mamanta Saida baba yace musu ba ita bace zaiyi musu bayani"A katoton parlourn Gidan aka saukesu Dan ba laifi k'annan baba dukansu a da chanma da halin su bare yanzu da cigaba yazo Shima babban gidane Nan mutane akayi ta kawo gaisuwa mutane duk sun cika Gidan Bayan ankawo musu Abun tarbar Baki daya daga cikin K'annan baba alh Habu ya ce"Yaya muna jinka kayi Mana bayanin Ina ka shige kaida Zahra tsawon Shekaru"Nan baba ya kwashe labarin komai ya Basu ciki har da haduwarshi dajikarshi da Kuma rasuwar y'arsa da irin taimakon da MD yayi masa "Salati kowa keyi masu kuka nayimasu tsinewa mudan nayi Ya"Yan Yan uwa ko Mata da iyaye sai rungumar Zahra suke Sosai kowa yayi mamakin Jin mudan shine ya kashe Hajiya saratu(kakar zaha?)Sannan yayi kokarin kashe Dan uwansa godiya Sosai aka shiga yiwa Ammy da MD Alh tukur ne ya Ce "Haba biri yayi Kama da mutum Amma Abun Nan yazo da mamaki mudan fa dashi akayi suturar Hajiya saratu ya dinga kukan munafurci a fuska yafi kowa shiga tashin hankalin ance Mana y'an fashin da suka kasheka Suka tafi da gawarka da Zahra har adduar ukku da sadakar bakwai data arba'in Saida Akayi muku Ashe dai da sauran kwananku a gaba gaskiya mudan bazai gama da duniya lafiya ba Haba kenan shiyasa da aka tambayesa dukiyarka ya Ce Babu abunda naka Dake hannunshi duka ka amsa sannan barayin sunkwashe komai haka kawai muka kyalesa saboda mu Kai ka fiye Mana komai bamu kuma waiwayarsa Akan dukiyarka ba saboda a ganinmu Fatima maringanyiya itace magajiyarka fiye damu to Bata Nan da Tana Raye ne ma a lokacin zamuce saimun kwatar Mata hakkinta ba ayi shekara biyu da faruwar Haka ba Mudan ya kwashe komai nasa Dake Nan har Gidan daka saya Masa ya sayar tare da matarsa da y'arsa sadiya da tun kana Nan aka haifeta suka tashi ya Ce wai ya samu wani babban aiki a kaduna Babu Wanda ya kawo komai akai mukayi mishi fatan alkhairi Tunda ya komai kaduna mudan mudashi ko a waya Sosai hankalinmu ya tashi kasan d'an uwa da d'an uwa bamu k'ara samun labarin mudan ba sai kwanaki Nanda shekara ba ayi goma ba Alh Habu yaje garin wani taronsu na professional suka hadu dashi dakyal ya barshi ya kaishi gidanshi Yana mishi fada Akan meyasa ya baro Yan uwanshi bai Kara waiwayaba Yana hawayen munafurci ya Ce "wai bazai iya Zama garin bane zuciyarsa ji yake Kamar zata tarwatse saboda rashinka da yayi yasa yaji garin ya fita a ransa haka dai habu yayi Masa fada ya Ce "Zai dinga zuwa"Koda habu yazo ya fada Mana Sosai mukayi hamdala Jin lafiya yake Dan a tunaninmu ma ko wani Abun ya samesa takanas sati na zagayowa mu biyar din muka shirya A mota mukaje domin mu ziyarcesa muyi mashi fada Akan ya dinga ziyartarmu ko hankalinmu ya kwanta saidai me Koda muka je saimuka tarar ya sayar da Gidan Harma wanda suka saya sunshiga Sosai mukayi mamaki da Al"ajabi mun tambaya inda suka koma Amma ba Wanda ya sani Daga lokacin muka Fara zargin mudan Akwai rashin gaskiyar da yake boyewa Ashe dai Haka dinne gaskiya mudan yacika Maci Amana Yayi Mana bazata"MD ya dago sai lokacin yayi magana ya na kallon alh tukur ya ce "Baba Shi Alh Habun Zai iya gane Gidan"Alh habu Dake gefe ya Ce "Kwarai kuwa Har Gidan Zan iya ganewa a Nan ne unguwar dosa saidai fa ya tashi Dan sau biyu muna komawa Amma ya tashi Babu Wanda Kuma yasan inda ya koma"ba matsala baba Indai ka gane Gidan Abun Mai sauki ne bazai wahalar kamuwa ba Indai har Yana garin kaduna Zai kamu "Malam sani ya ce"Tabbas hakane saidai ayi plane din ylda wuri saboda kar labarin bayyanuwarka yasanya ya gudu ko yayi maka wani Abun"Murmushi MD yayi yace "ba abunda Zai faru Insha Allah yanzu kawai yanda za ayi mu koma kd sai muje a nunamun Gidan"Alh tukur ya ce "a a a fa saikun kwana Taya zakusha doguwar tafiya haka Baku kwana ba "tarba ta musamman da girmamawa sunshata a garin Nan Zahra ko Yan uwa sai zuwa ganinta ake Wannan ya dauki Yaran wancen ya dauka cousine din Mamanta da diyansu Sai zuwa suke ana kulla zumunci duk sunyi musayar number da su kwana biyu sukayi a jigawa suka dawo kd Wanda MD duk jinshi yayi Kamar a Kaya saboda baby zahrar sa a tare dashi Koda suka Isa kd kafinma su wuce gida unguwar dosa suka nufa har bakin get din Gidan dukda an Kara sabunta Gidan ya kaisu suna Isa ya ce ayi parking Nan ne Gidan"Mamaki ya gama cika MD ya ce "Baba ka tabbatar kuwa ba batar Kai kayi ba"Comfirm Wannan shine Gidan bazan taba Manta sa ba "Kallon ammy MD yayi ya ce "Ammy wannan Ai Gidan su Amera ne kin Manta lokacin Dana aureta ma Anan Gidan ne kafin Daga baya su koma kawo"Ammy na sake sake a ranta ta ce"Tabbas Nan ne "Baba habu ne ya ce "Wace Amera kake magana yaron Nan"Matata ce baba kilan ko mistake kayi"Sunanta na gaskiya fa "baba habu ya tambaya"Sadiya"Md ya basa amsa gabansa na faduwa"Innallahi Aiko idan ba sa'a ba y'ar mudan ce sunanta sadiya ita daya garesa"Gaban Ammy na tsananta faduwa ta Ce "innalillahi wa inna ilaihiraji'un juyar dakan motar MD yayi "ya ce "Bari muje na kaiku Indai shine kuga fuskarsa idan Kuma bashi bane to"Kai tsaye Gidan su amira suka nufa sunyi mamaki matuka Ganin tundaga farkon layin har karshensa cike da motocin jami'an tsaro Koda suka karasa bakin get din Gidan cike yake da motocin Yan sanda Yan unguwa duk anfito anyone curgo curgo hankali tashe MD ya fito Ganin shine ya Sanya jami'an tsaro basu ce mashi komai ba tambayar days Daga cikinau yayi ya ce "ka shiga dai ciki manyan na ciki ranka ya Dade Daman Abun yashafeka gears da Allah ya kawokama kafin a kiraka"abunda ya shafeni Kuma "Md ya fada Ganin su ammy da baba da baba habu sun fito Dan Zahra k'in fitowa tayi "a tare suka shiga cikin gidan Sosai hankalin MD ya tashi ganin daddyn Amera hannayensa biyu cikin handcuffs sojoji da y'an sanda sun zagayesa amera da Mamanta sun biyosu sai kuka suke amera na Ganin MD ta ruga da gudu wajensa tare da ruko hannunsa a matukar rude ta Ce "Honey kaje Kayi musu magana zasu tafar mun da dad Dan Allah honey karka Bari su tafar mun dashi ba abunda yayi musu"ta fada cikin wani irin kuka Mai tashin Hankali"Kallon kallon aka tsaayayi tsakanin baba da baba habu da Kuma Baban amera da yake hawayen nadama a tare baba habu da kakan Zahra suka ce "Mudan " motsa hannunshi mudan yake Dake rike da handcuffs a matukar rude ya ce "Yaya Daman baka mutu ba "Baba Yana hawaye ya ce "Ban mutu ba mudan kaga ikon Allah a tunaninka ka kasheni saikuma ka Manta da Allah shine Mai iko Akan komai bakayi tunanin Zan rayu ba mudan Me nayi maka da na chanchancin Wannan danyen hukuncin Daga gareka mudan ka Manta cewar Ni jininka ne saboda son Abun duniya yayi maka yawa ka Manta koba hisabin duniya akwai na lahira"Mudan na kuka da idonsa ya ce "Hakika na cutar dakai Dan uwa na hakkinka kadai ya Isa ya Hana Ni zaman lafiya nasan ban chanchanci yafiya Daga gareka ba saboda ban chanchanci a yafemun ba Yaya Ina kunyar hada Ido kadai a yanzu"Ya karasa fada cikin wani irin kuka "salati ammy tayi ta salamce MD kanshi Saida yayi mutuwar tsaye Banda amera da Mamanta da sukaji wata sabuwar maganar ta bullo jami'an tsaronma tsaye sukayi suna sauraron wani case din sabo baba habu ne cikin muryar bacin Rai ya ce "Ai baka ga komai ba mudan na tabbatar bazakayi kyakyawan karshe ba Ina son ka fadamun Kaine Wanda ka kwantar da d'an uwa na tsawon shekaru kwance ka mantar dashi komai "Kauda Kai mudan yayi ya ce "Yau Rana ce ta tonon asiri a gareni Tabbas Nina kwantar dashi tare da y'arsa da tun sanda muka Kai musu Hari ta tsira muka neme ta muka rasa Wanda ba Wanda yasan yanda akayi ta tsira na rufe musu bakine dalilin dodon tsafinmu daye ke nuna Mana Kuna raye dukda ban gaskata kana rayen ba saboda Harbin da nayi maka banyi tunanin zaka Tashi ba "Hankali tashe Baba Habu,da baba ,da maman amera sukace tsafi Kuma Mudan kana nufin har tsafi make bamu sani ba innalillahi wa inna ilaihiraji'un"Banda kuka ba abunda Baban amera yake kukan nadama ya ce "na Fara tsafine tun kafin dawowata kaduna na hadu da wani abokina Wanda sanadiyarsa na fada harkar tsafi Ni mutum ne Mai tsananin son Abun duniya tun Ina yaro hakan yasa nake iya komai Akan Indai Zan samu kudi kisa a wajena ba wani abu bane ,na kashe mutane da Dama.....kasa karasa abunda yakeson fada yayi sakamakon kukan da yaci karfinsa salati kawai kowa yake Jin abunda Baban amera ke fadada bakinsa har Zahra da ta shigo Daga baya Saida ta tsorata you tayi Kamar zata ruga MD Dake kusa da ita ya ruko ta "dukta tsorata ,"tashin hankalinta da MD yake jiki baya musaltuwa dakyal ya iya Daga Baki ya kalli daya Daga cikin jami'an tsaron ya ce "Wan laifin ne yayi Wanda har aka zagaye Gidan. Da jami'an tsaro"Daya Daga cikin dpo din da MD yasa Akan binciken kisan babanshi da Kuma na Alh sammani aminin babanshi ya ce"Case din Akan aikin ka ne MD Kasan tun lokacin kisan mahaifinka Da na Alh sammani bamu bar bincike Akan wadanda sukayi Wannan aikin ba to a jiya ne bincike yagano Mana wasu Daga cikin manyan y'an fashin garin Nan Wanda muka gana musu
Chapter 87 · 0% Book details