← Book details Auren Wata Tara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 64 OF 92

Sashe 64

Auren Wata Tara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

shine kika dawo ki kashemun miji rufin asiri na uban ya ya na ,," sosai ta fara bugun Zarah iya k'arfin ta Cikin wani irin b'acin rai da Chuchu tajima bataji irinshi ba ta daga hannu da wanke Mama Rabi da mari"kafin ta d'ago ta k'ara kifa mata wani "Dagowa Mama Rabi tayi rik'e da kumcinta ta ce " kutumar uban nan ni kika Mara"An mareki d'in wlh kika kara yunkurin tab'ata abunda yafi mari ma zan miki ki fita kibar d'akin nan tunda ba Haihuwarta kikayi ba da zakizo kina jibgarta "Kururuwa Mama Rabi tayi cikin b'acin rai Ta nufi Chuchu da niyyar shakota Waigawa Chuchu tayi cikin Sauri K'arfen da ake sanyawa majinyata kafin ruwa ta janyo tare da Buga Mata shi da karfi aka ji kake tasss Ai Mama Rabi azabar da tajice batasan sanda ta k'walla Kara ba tare da Zamewa a wajen tuni goshinta ya fashe ya fara zubar da jini Chuchu na ganin haka hankalinta ya tashi Asmy ma dake gefen Zarah tana Rungume da ita saida ta zaro ido ta ce " Chuchu me.kikayi mata haka"Cikin rudu Chuchu ta ce "Kina gani yunkurin Kaimun Duka fa tayi kinsan dai karfi na da nata ba d'aya ba shiyasan ya na Buga mata " Innalillahi Zarah da Asmy suka shiga nanatawa ganin yanda Mama Rabi ta sume Zarah ta ce "Shikenan Chuchu kinjamun na shiga ukku"ta fada cikin muryar kuka Cikin Sauri Chuchu ta ce "Ki maza mu bar asibitin nan"ganin Mama Rabi na k'ok'arin farfadowa Dan sumar ma ta azaba ce ya sanya Chuchu saurin zuwa gadon da Zarah take ta kamo hannunta ta ce " ki maza mu tafi karta farka kinsan bazata kyaleni ba nikuma bazan juri ganin kin sake fad'awa cikin wani halin ba please ki taho mu tafi gidanmu Dan girman Allah "Zarah na kuka ta ce " Bazan biki ba Chuchu a halin yanzu mutuwa ita nafi buk'ata fiye da wannan bak'ar rayuwa meyasa baki barta ta kasheni ba ku tafi kawai na shirya amsar kowani irin hukunci koda kuwa hakan zaiyi sanadiyar mutuwa ta...rufe mata baki Asmy tayi tana kuka Itama kukan Chuchu take duk ta rude ta rasa yanda zatayi janyo Zarah tayi ta ce "Ki taho momcy karki zauna su illataki " daida nan sukaji muryar Mama Rabi tana cewa "wayyo Goshina zai balle Allah tsinewa yarinyar nan ta illatani wlh saikinsan kin tabo Rabi y'ar dangi a garin funtua yau d'innan ko baki mutu ba keda tsinanniya kawar taki saikunzama Abun tsoro Dan wlh kartin mazan gidanmu bazasu barku ba saina sanya sun sauya muku halittu ta fad'a tana Kokarin Mikewa amma azabar zafin da takeji yasa ta kasa" Cikin kuka Chuchu ta ce "Kinji abunda take fada ko Momcy Dan Allah ki taho mu tafi" Asmy ce itama data tsorata tace "ki tashi Mubar asibitin nan zahra kinsan sarai matar nan ta aika y'an dabar gidansu Sunkai biyar wlh zata iya sawa a illataki " Zahra na kuka ta ce "Baba Dan Allah ku bari ko ganinsa nayi" Janta sukayi dole suka tayar da ita cikin Sauri Suka nufi barin d'akin "Mama Rabi na ganin haka ta fara ihu tana cewa " Wlh baku isa ba zaku dawo saina illataku tsinannun asarar haihuwa "Basu saurareta ba in banda saurin da suke Allah ya taimakesu basu gamu da na gida ba a wajen asibitin kai tsaye bakin get d'in suka nufa saida suka fita hankalin Chuchu ya d'an kwanta Ajiyar zuciya ta sauke Tare da zaunar da zahra da takejin layi akan wani dakali har lokacin kuka take " itada Asmy "matsawa kusa dasu Chuchu tayi cikin Sauri ta bud'e wayarta kai tsaye contact din Yayanta ta kira tanajin ta fara ringing ta fara zirga zirga har ta katse bai d'auka ba oh my god ta fad'a kafin ta k'ara kira cikin Sauri ta ce " yaya d'auka yaya d'auka kai kad'ai ne zaka iya fuskanta ta kai tsaye ka taimakemu saida ta kusa katsewa kafin ya d'auka tana jin ya d'auka ta fashe masa da kuka "Cikin tsananin tashin hankali ya ce " Innalillahi what happened Chuchu me akayi kike kuka waye ya mutu"Cikin kuka ta ce "Yaya ba mutuwa bace Zadai a kashemu Dan Allah kazo ko katuro a taimaka mana Allah muna cikin wani hali" Cikin tashin hankali ya ce "Innalillahi wa inna ilaihiraji'un shiyasa banason barinki barin gida daidai da second fad'amun me yake faruwa karki tarwatsarmun zuciya "cikin kuka ta ce " yaya nasan kai mai fahimta ne zaka fahimcemu momcy ce ta shiga wani hali yanzu haka muna cikin tsananin tashin hankali Dan Matar ubanta ke son kasheta yanzu ma dak'yal muka samu muka kubuta yaya ka taimakemu ka turo mota azo a d'auke mu kartayi mana illah"ta k'arasa fad'a tana kuka"Ai MD daga zaunen da yake baisan lokacin d'aya zabura ya Mike ba ya ce "what takeson kasheta Innalillahi wa inna ilaihiraji'un wani tashin hankaline ya ziyarci zuciyarsa jin ana son kashe Zarah a matuk'ar d'imauce ya ce " Yanzu kuna ina "Kallon Sunan Asibitin tayi ta ce " Muna general hospital funtua"Okay to gani nan kusamu waje ku b'uya Karku bar wajen "to yaya Dan Allah ka turo a taimakemu" katse wayar yayi batare da ya saurari abunda take cewa ba Dan hankalinshi a matuk'ar dage yake jin ana farautar rayuwar Zahra waje yayi daga palourn shi cikin Sauri Duk ya rud'e d'aya daga cikin driver d'inshi da bai tafi ba ya kwalawa kira yana zuwa ya ce "yi maza ka dauko mota yanzu wacce ba Suna na jiki kuma wacce ba asanni da ita ba yanzunnan " Driver najin haka cikin Sauri yaje ya d'auko motar MD na shiga yace "Yi gudu sosai kayi gudun da baka tabayi ba ina son kafin nan kafin 30 minutes ka kaini Funtua " Angama ranka ya dad'e ya fad'a yana karawa motar gudu "Duk kanshi ya kulle Jabir ya kira yana d'auka ya ce " kana ina yanzu"Ina gida "Idan baka komai ka fito da Mota yanzu na kama hanyar funtua mu hadu a Chan" Funtua da Daren nan Jabir ya fad'a cikin mamaki "eh yanzu Chuchu ta kirani cikin tashin hankali wai ana harin rayuwar Mai Sunan Ammy Yanzuma dak'yal suka sha" Cikin tsananin tashin hankali Jabir ya ce "Subhanallahi gani nan yanzunnan" anyi gudu ma awa guda ya kamata ya kaisu shine cikin minti 35 suka isa garin funtua Wanda kai tsaye general hospital din suka nufa Saida sukaje gab kafin Suyi parking ta nesa MD.ya hangosu su Ukku sai sannan hankalinsa ya tuno masa Tabbas ya tunkaresu kai tsaye asmy da Zahra zasu ganesa su tona masa asiri gaban Kanwarsa "dafe kanshi dake tsananin sara masa yayi kiran jaber yayi ya ce " kana ina "na kusa yanzu " naga Inda suke amma Kasan Bazaiyu na tunkaresu ba su Ukku Chuchu zata gane halin da ake ciki"Daga bangaren jabir ya ce"yanda za ayi ka.kira Chuchu Kad'an ja hankalinta da kwatancen gaba Kad'an Inda kake data bar wajen saika shammaceta kaje kawai ka daukota amma karka saki kabarta "Ajiyar zuciya MD ya sauke ya ce " To ita kawar tata fa"Karka damu da ita kota ganka ba matsala hankalinta ma zaifi kwanciya akan tayi tunanin ko Sace ta akayi "yanda Jabir ya basa shawara haka yayi ya kira Chuchu ya d'auke hankalinta tayi wani wajen yana ganin ta danyi nesa dasu ya sauka daga motar Inda suke ya nufa har lokacin kuka zahra take tanajin takaici da bak'inciki a cikin zuciyarta Asmy ma tayi tagumi hawaye kawai take " kamar daga sama zahra taji an ruko hannunta Duka biyun tare da daukarta gaba d'aya tana shirin fasa ihu Yayi saurin rufe bakinta da hannunsa Asmy dake shirin itama kwala ihun ya Kalla tare haska mata kansa da hasken screen din wayarsa"ya mata nuni da tayi shiru da hannu" gwalo idanu tayi ganin Wanda Bata tab'a tsammani ba ta ce "me ya kawoka nan " Karki damu ina tare da ita bazata cutu ba "Asmy duk ta rude waige ta fara ta ce " To to to "Saurin barin Wajen yayi bai dire Zarah ko ina ba sai mota Ya bi Shima ya shiga ya rufe yacewa " Driver ka juya damu"Zahra Najin muryarsa ta gene cikin tsananin tashin hankali ta bud'e idonta ta sauke a kansa cikin tsananin b'acin rai da bakin ciki ta ce "Ubanme kazo kamun ka sauke ni Na rantse da Allah kafin na Tara maka mutane Bayan Lalatamun rayuwa da kayi da ruguzamun rayuwa dakayi bai isheka shine har saika biyo Inda nake zuwane kayi ka k'arasa kasheni Allah ya isa tsakani na dakai mugu azzalumi macuci ka cuceni ka yaudareni kaci Amanata daman Kasan da cikinka jikina shiyasa kaki Sanar dani kak'i Sakina ka barni na taho da kadarraren cikinka gidan iyayena ka lalata Aure na da Wanda yayimun halicci ya soni tsakani da Allah yayi dakon soyayyata shekara da shekaru sannan ka ruguza mu'amula ta da mahaifina da y'an uwa na ka cuceni Ka zalunceni Allah ya isa tsakani na dakai" ta k'arasa fad'a cikin wani irin kuka mai tab'a zuciyar mai sauraro rumtse idonsa MD yayi yanajin kalaman nata na dakar masa zuciya jin ta ambaci ciki ya sanyashi Sauri Dagowa cike da mamaki ya ce "Ciki ?Kina nufin Kina da ciki " Hawaye cike da fuskarta ta ce "Bansaniba mugu azzalumi wlh saina zubar da kadaddararan cikin nan kamar yanda na tsaneka haka na tsani cikin ta fad'a tana Kokarin bud'e kofa ta fita dukda Gudun da motar take MD na ganin haka yayi Saurin ruk'ota tana fusgewa dak'yal ya samu ya rungumota jikinsa " Bugunshi ta fara da hannu iya karfinta ta ce "Ka sakeni nace Wlh baka isa ba ka gudu dani Ka maidani Inda Ka daukoni ko kuma kayi Dana sanin tab'a sani na ma da kayi a rayuwa"ta fad'a tana kokarin fusgewa daga jikinsa" Meye haka Mamy ki nutsu "Bazan nutsu dinba ku saukeni na rantse da Allah ko na yi muku ihun y'an kidnapping"Innalillahi" MD ya fad'a "Hankalinsa a matuk'ar tashe yake baima lura da Kiran Jabir da Chuchu suke masa ba Sosai zahra ta chaza masa kai ganin tana Kokarin fusgewa daga ruk'on da yayi mata ya sanyashi kallon driver ya ce "
Chapter 64 · 0% Book details