Sashe 38
Auren Wata Tara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kalleta Da har lokaci hawaye basubar zarya a idonta ba ya ce "Gobe zanshigo Garin Around 4 Idan na tafi saiki koma hostel din hakan yayi miki ai ko?saita samu kanta da daga masa kai " A hankali ta fita daga motar harta bace masa gani baibar kallonta ba kafin ya sauke ajiyar zuciya kanshi ya had'a da sitiyarin mota yayi minti goma batare da ya dago ba ya rasa abunda yake masa dadi Dak'yal ya iya tashi yayi driving ya juya Kd tun a hanya yakejin ringing wayarsa bai dagaba ganin missed call d'in yayi yawa ya sanyashi dubawa yana ganin Number Ammy ce saida gabanshi ya fad'i a sanyaye ya d'aga sabon kiran d'aya shigo "Duk Inda kake kazo ka sameni a gida yanzunnan " Yanayin yanda Ammy tayi maganar ya tabbatar masa da tana cikin fushi a sanyaye ya ce "Gani nan zuwa ammy'" Bata amsa ba ta katse kiran "numfashi mai zafi ya fesar kafin yaci gaba da driving cikin Rashin nutsuwa Koda ya isa kd kai tsaye gidansu ya nufa A palour ya tarar da Ammy sai Chuchu gefenta tana Danna waya Amera na Kan sopa itama ta hade kai da gwuiwa tana kuka girgiza kai kawai yayi Dan yanzu kam ya tabbatar da kishin Amera ya wuce yanda yake Tunani Kennan Ammy tazo ta sanarwa " waje ya samu a palourn ya zauna Ba yabo ba fallasa Ammy ta amsa gaisuwar da yayi mata sannan Chuchu ta gaisheshi kamar ko yaushe yanda take gaisheshi Ajiyar zuciya Ammy ta sauke tare da Kallon MD ta ce "Yanzu Amera take zomun da wata magana wacce ta kusan girman tunani na hakane gaske ne koko?Batare da nuna alamun damuwa ba ya ce " wace magana kenan Ammy"Kallon Amera Dake kuka har lokacin Ammy tayi ta ce "maimaita abunda kika fad'amun " Kamar mai jira cikin kuka Amera ta ce "da Mace na kama su a gida na " Da mamaki MD yake kallonta Cike da mamaki ya ce "Kika kamamu Amera fa kikace zaki iya rantsewa da Qur'an Akan kin kamani da wata mace " Tana kuka ta ce "ba kamawa na iskanci ba Ai kamawa na bahaushe kun fito tare kaida ita daga pournmu"Kallon mamaki Ammy da Chuchu suka dinga binta da su Chuchu ta ja dogon tsuka ta ce " Daman ba na fad'a maki ba Ammy saikace dai bakisan halin yaya ba nasan wallahi yaya bazai tab'a aikata abunda tazo ta fad'a ba sharri ne kawai take neman K'ulla masa dan munafurci Mtwsss "daga mata hannu Ammy tayi ta ce " Karna karajin bakinki a nan Auta Amera sa'arkice karna kumajin bakinki a maganar nan "Tana turo baki Chuchu ta tashi tare da gallawa Amera harara da itama Amerar hararartata ta ke Dan daman Chan basa jituwa tabar palourn tana Jan tsoka maida hankalinta wajen Amera ammy tayi ta ce " Fad'amun gaskiyar abunda ya faru"Har lokacin kuka ta ke....nan ta labartawa Ammy komai da ta gani iya gaskiyarta har tafiyar da yayi da ita da shakar da tayiwa yarinyar.Kallon MD Ammy tayi ta ce "Hakane babana" Batare da tsoro ko shakku ba ya ce "Hakane Ammy" Me ya hadaka da mace babana har cikin gidanka kuma Alhalin ba kowa a gidan"?Tambayar da tun farko ya kamata tayi Amma ta kasa"ya fad'a ya na Hararar Amera "To yanzu fad'a mana meye alakarta da ita "Numfashi yaja kamar bazai magana ba saikuma.ya d'ago ya ce " Kanwar Jaber ce Tare suka zo bata da lafiya ya dawo da ita daga Asibiti sai akayi mashi kiran gaggawa Compony kasancewar gidana ne Inda yafi kusa da Inda yake shine ya nufo gidana da ita ya tafi kasancewar bata lafiya Saiyace ta jirashi anan kafin ya dawo ganin ya jima ne ya sanya nace bari mu fito Kawai na sanya driver ya kaita gida shine fa "Salati Ammy tayi ta na kallon Amera ta ce " Tofa kinji Kike tada jijiyoyin wuya yanzu Dan Allah wannan dame yayi kama Wannan wani irin zafin kishi ne gareki Amera ba bincike ba komai kin kama y'ar mutane da Duka bama lafiya gareta ba yanzu Dan Allah iyayenta muna mutunci dasu sukaji zasuji dadi kuwa?Goge hawayenta Amera tayi ta ce "Kiyi hakuri ammy bankawo komai a raina bane sharrin shaidan ne " tab'e baki Ammy tayi ta ce Allah kiyaye "ta Mike tabar palourn cike da jin Haushi Matsowa tayi kusa da MD da ya lumshe idonshi tayi cikin sigar Ban hakuri ta ce " Kayi hakuri honey Dan Allah"Bai tanka mata ba haka bai bata amsa ba "Tana shirin fashewa da kuka ta ce " Please honey Dan Allah ka yafemun kasan kome nayi nayishine saboda sonda nake maka tsananin kishin Kane ya sa na aikata komai "Dagowa yayi lokaci guda d'aya Kalleta yaga irin yanda idonta yayi ja " girgiza kai yayi ya ce "kishi hauka ne Amera?haka ake kishi?yanxu da kin Kashe y'ar mutane ki ce me ?So kike ki ja mana bala'i ,sannan ji maganganun batancin da kika dinga fad'amun matsayina na mijinki hakan da kikayi tarbiya ce,Ko angaya maki haka ake kishi" kama hannunshi Tayi tana kuka ta ce "Kayi hakuri honey bana iya control d'in Kaine ne akan kishin da nake maka " tab'e baki yayi baice Mata komai ba "Kayi hakuri Dan Allah Karkayi fushi?Dagowa yayi yaga yanda tayi kalar tausayi lokaci guda saiya sakar mata murmushi ya ce " ya wuce my merah"Ajiyar zuciya ta sauke tare da kwancewa jikinshi ta Ce"Thnks mijin da yafi na kowa "a hankali ya zame jikinshi da nata Dan kar Ammy ta fito a tare sukaje sukayiwa Ammy bankwana sannan suka kama hanyar gidansa a hanya MD sai mamaki yake yanda ya iya shirya k'aryar wannan around 10pm suna zaune a palour ta narke masa a jiki ta ce " Honey baka tambayeni ya akayi na dawo yau ba"yana wasa da gashin kanta ya ce "saikin fad'a" Cikin farinciki ta ce "Gajiya nayi da zaman kadaici kuma bazan juri Rashin ka a kusa dani ba shiyasa na yanke shawarar biyo mijina ko na samu lada " Kin kyauta "ya fad'a " Nan suka Dan tab'a Hira Kad'an kafin suje su kwanta sosai Amera tayi mamakin yanda MD baiyi kokarin yi mata komai ba a ranta ta ce "huta roro Allah ya taimakeni" Dan tasan irin wahalar da takesha musamman idan suka jima basa tare da wannan tunanin har bacci ya d'auketa Wanda Bata kawo komai a ranta ba. <Zaria> Dariya Asmy ta kwashe da ita Bayan ta gama sauraran labarin da Zarah ta bata ta ce "Kam amma Matar nan anyi y'ar iska wlh tabarya fa da Adda kikace yo ko dai k'aura ce?Duk yanda Zarah ta hade rai Dan sosai maganganun Amera suka daki zuciyarta na ce mata karuwa da tayi Jin Abunda Asmy ta ce batasan lokacin da tayi Dariya ba ta ce " Kai sis baki da dama wlh wai Kaura "Asmy na Dariya ta ce " to inba yar daba ko Kaura ba wazaiyi haka itadai wannan kishin nata na hauka ne Wlh Dan daga gani matarsa ce "tab'e baki Zarah tayi ta ce " oho dai koma me dinsa ce chanta matse musu"asmy ta ce"Ke matarsa ce ma Gaskiya tunda Kinga daman sunce akwai matarsa da ke karatu waje saura wata Tara ta gama kila Hutu ne tazo""Umm hakane na ganta da akwati kuma a zagin da tadinga mun ta ce mijinta dukda tashin hankali bai bari naji sauran abunda take fada ba Ni fa bama wannan yafi damu na ba yanzu Wai gobe Nakoma gidansa da kayana ni bansan yanda zanyi da wannan murdadden mutumin da kuka lakamunba wlh"Asmy na boye dariyarta ta ce "yazakiyi dole Kibi umarnin mijinki tunda haka ya ce " Dundu a baya Zarah ta kaimata ta ce "Bansan iskanci asmy Allah kiyaye wannan ya zama mijina " Asmy na Dariya ta ce "To yanzu me d'inkine inba mijinki ba "harara Zarah ta galla mata ta ce " Mijin wucin gadi dai harna k'agara 9 months d'innan yayi na huta wlh "Kedai fad'i Gaskiya Malama kemafa nasan harkar nan sonta kike har kiba kikayi irin kinsamu abunda kikeso " Asmy ta fad'a tana dariyar shak'iyanci saurin barin zancen Zarah tayi Dan karta b'allo mata ruwa...washe gari Zarah badan taso ba saidan Asmy ta karfafa mata akan taje karyazo makaranta ya jaza mata wani abun ya sanya Zarah shiryawa ta tafi gidan saida ta share gidan Tass lungu da sako tayi mooping dan taga yayi kura ta sanya tsintsiyar k'amshi da air freshener mai dad'in k'amshi kafin kace me gidan ya kaure da sanyin ni'ima ganin irin aikin da tayi ga zufa ya sanyata yin wanka a toilet din D'akin Bayan ta fito tayi Sallar Riga da sicket d'inta na atamfa da sukayi mugun amsar choculate colour din fatar ta ta mayar Sosai kayan suka kamata daman Chan Zarah Indai zata sanya kaya tofa saisun fito mata da shape d'inta Y'ar hoda da kwalli kawai ta zizara badan komai ba saidan sabo da intayi wanka saita shafa su sannan ta fesa daya daga cikin turarrukan da tagani a jikin mirror sosai ta feshe turaren hada mugunta taga bati Ganin bayanan ya sanyata sakin jiki ta fito palour ba hijab rasa abunda zatayi tayi hakan ya sanyata d'aukar wayarta ta fara chat sosai ta shagala da chat har batasan shigowar motarshi gidan ba saida taji karan shigowa ya sanyata saurin firgita ta kalli kofa Shigowa yake cikin shigar da ya saba ta turawa da suke mugun Yi masa kyau Kallo d'aya tayi masa tayi saurin kasa da kai MD sosai yaji dadi da ya iske gidan tsaf tsaf a rayuwarsa Ba abunda yakeso sama da tsafta har wani lumshe ido yake Dan sosai yakeji dad'in k'amshin na ratsa sa lokaci guda a rayuwarsa da yaji yarinyar ta burgesa Karasawa palourn yayi binta ya dingayi da Kallo da kayan jikinta da suka dameta Zarah dukda ba kallonsa take ba Amma saitaji kunyar shigar da tayi a fakaice ta d'ago tana Kallonshi Idanunsu suka sartse Cikin na juna samun kanshi yayi da sakar mata murmushinshi mai tsada gabanta na fad'uwa Tayi kasa da kanta jinta take duk a takure ta kasa koda magana daya lura da hakan ya sanyashi Zuwa kujerar