Sashe 94
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wannan yasa a take ta dauko wayarta ta kira Hussain dan taji dalilin da zaisa ya bar Fatima ta bi bayansa da tsohon ciki. Sai dai Hussain din bai dauka ba sai Hassan, ta gaya masa abinda ake ciki sannan ta koma gida ta cigaba da zaman jiran dawowarsu.
Har magrib tayi, sai ta kuma dauko waya ta kira Hassan amma bai dauka ba, ta kira Fatima not reachable Ruqayyah switched off. Ta kira Hussain shima ba'a dauka ba. Hankalin ta yayi dubu ya tashi, ta shiga dakin Khadijah ta tarar da ita a kwance wai zazzaɓi takeyi, ta dafa jikin ta taji zafi sosai, sai ta koma dakinta ta dauko mata magani ta taho da niyyar zata bata sai taga kira daga Bauchi. Babban yayan su Alhaji Lukman, tayi gyaran murya ta dauka tana gaishe shi, sai taji yayi shiru kafin ya amsa sannan yace mata "duk kuna gida tare da yara?" Tace "eh" tana mamakin tambayarsa, sai yace "shikenan ku zauna a gidan gamu nan tahowa komai dare insha Allah" sai ya kashe wayar ya barta da sakakken baki. Me zai zo yayi komai dare? Koma menene a barwa gobe mana?
Ta samu gefen gado ta zauna kusa da kafafuwan Khadijah tana cigaba da kiran number din Hassan da Hussain amma duk babu wanda ya dauka. Ta gaji ta tashi ta daga window tana hangen titi ko zata hango tahowar su amma babu alamar su.
A lokacin ne taji an rusa ihun kuka da muryar Nafisa, taji wani abu ya tsirga mata tun daga kanta har tafin kafarta. Taji wani irin daci a makwogwaron ta. Sai taji sautin kukan Nafisa yayi mata kama da sautin kukanta a lokacin mutuwar Alhaji Aminu uban ƴaƴan ta.
Khadijah da take kwance ta mike da sauri ta tafi dakin Nafisa tana hardewa, a hanya suka hadu da Zulaihat itama tana dosar dakin Nafisa. A dai dai lokacin Aunty taga tsayawar ambulance a kofar gidan. Ta sandare a gurin tana kallo aka bude gate aka shigo da ambulance din sannan akayi packing aka bude baya, taga police sun fito, sannan taga Hassan ya fito amma bata ga Hussain ba sai taga an turo gado da wani abu da yayi kama da gawa akai. Ta saki labulen sannan a hankali ta zame ta zube a gaban tagar.
Hassan yabi gawar Hussain da kallo ya tabbatar an shiga da ita ciki sannan ya juya gurin limamin unguwar su da ya biyo bayan motar rasu. Ashe har sun samu labari sun zauna jira. Hussain mutumin kirki.
Liman yace "dare yayi yanzu, sai dai yayi kwanan keso sai da safe ayi masa sallah" Hassan ya gyada kai kawai. Liman din yace "da assuba zan tura aje makabarta a haka kabari, yanzu kuma zan sika a siyo likkafani, sai asa lokaci saboda yan uwanku su sami sallah" sai Hassan ya girgiza kansa yana kallon garden din gidan, inda tun suna raya suke yin shuke shuke shida Hussain har suyi rigima in wani ya tabata wani yace "anan za'a binne shi, a cikin garden din mu. Nayi masa alkawarin zanke zuwa kabarinsa kullum ina masa addu'a. Anan za'a binne shi a kusa dani"
Wannan littafin na siyarwa ne, idan kin ganshi a wani gurin na sata ne, in kina so ki karanta halaliyar ki kiyi min magana ta WhatsApp through wannan number 08067081020
Sorry about the typos please
Mai sharing littafi, bana ganin ki Amma *Allah* yana kallon ki kuma na barki da shi*Hidden Strength*
Sumayya yau bata tashi daga school ba sai da akayi kusa kiran sallar magrib. Ta gaji likis saboda yau sun safe suke lectures babu kakkautawa, dan yau sau daya taga Adam shima briefly yazo wai zasuyi sallama zai je Abuja tare da oga Hussain. Tana murmushi tave masa "kwana nawa zakuyi?" Yace "yau zamu dawo" tace "yau zaku dawo din shine harda sallama?" Ya langwabe kai "kika sani ko kawai so nake yi in ganki shine na fake da sallama" ta dan rufe fuska da mayafi, ya kama mayafin yana leka fuskar. Ta rufe idonta "ka bari fa" yace "ni ba zan bari ba, kallon fuskarki ma yanzu na fara" ta kwace mayafinta tana kara rufe fuskar dashi, yayi murmushi yace "kinsan wani abu?" Ta girgiza kai, yace "so nake in mun gama semester din nan inyi wa oga Hussain maganar mu, so nake a fara maganar auren mu tun yanzu ba wai sai mun gam school ba tunda kinga ai ina da aikina kuma ina samun kudi ba laifi, tunda na fara aikin kuma nake tarawa ba wani abin nke yi dashi ba. In nayi masa Magana nasan zai yi min jagora a maganar auren insha Allah"
Sai taji ranta yayi mata dadi, zuciyarta tayi fari tas, yace "kin amince da hakan?" Ta gyada kai tana murmushi, still fuskarta a boye, ita da ace amimcewarta kadai ake bukata da zata iya auren Adam ko da bashi da wannan aikin, koda sadaki kadai zai bayar babu lefe babu komai, thats how much take son shi. Da zasu rabu ya jaddada mata "you know I love you right?" Ta danyi murmushi tana kallon cikin idonsa ta gyada kai, sannan kuma kamar ba zata yi magana ba sai tace "and I love you too".
Har yanzu, har bayan ta wuni sir a makaranta ta dawo gida a gajiye da yunwa da ƙishirwa amma bata daina jin kaifin kallon da yayi mata a jikinta ba. Tana cin abinci tana zuba murmushi ita kadai, tayi sallah tayi wanka ta fito tama shiryawa Inna Ade ta shigo tana kallon ta. "Ke kuma fa kike ta farin ciki kamar anyi miki albishir da kujerar makka? Au ashe ba kinje, dan haka ba lallai ne ma kiyi farin cikin da kike yi yanzu ba" samayya tayi dariya, "haba Inna, farin ciki ma kuwa ai har marar misaltuwa zanyi in za'a mayar dani in sake ganin Ka'aba. Amma dai duk son da nake yiwa komawar in dai aka bani a yanzu sai dai in baki ko Baba tunda ni na sauke farali" Inna ta zauna a gefen gado tace "to gaya min abind yake saka ki wannan farin ciki haka"Sumayya ta zauna a kusa da inna tana kare mata kallo. Cikin yan shekarun nan da suka dawo gidan nan baba kuma ya samu aiki duk Inna ta chanja, jikinta ya murmure sosai babu wannan muguwar ramar fatarta tayi kyau tayi haske, kyawunta ya sake fitowa sosai. Sai Sumayya tace "kawai dai ina duba rayuwa shine naji raina yayi dadi sosai. Ina duba halin da mutanen da nake tsananin so suke ciki misali ku Iyaye na, Ruqayyah, kannena da sauran su duk kowa yana cikin rayuwa mai kyau sai naji zuciya ta tayi dadi sosai" Inna tace "banji kin lissafa da Adam ba" Sumayya ta sunkuyar da kai, Inna tace "ko shine da sauransu din?" Sai Sumayya ta rufe fuskarta, a dai dai lokacin wayarta tayi kara, ta bude idon ta tana kallon bakuwar number din da bata sani ba sannan ta dauka a hankali tare da sallama "Assalamu alaikum" daga daya barin taji muryar Ruqayyah "Sumayya nice, yar uwarki Ruqayyah ce. Accident muka yi ni da m.......... nida Fatima, Allah ya musu rasuwa ita da driver. An tafi dani asibiti ni kuma"
Sumayya ta zaro ido cikin tashin hankali "accident? Mutuwa? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Ya kike Ruqayyah me ya same ki ke? Wanne asibitin?" Ta jera mata tambayoyin cikin tashin hankali. Ruqayyah tace "da sauki. Asibitin da nake haihuwa. Ki gaya wa su Inna" sai ta kashe.
Inna Ade da dama tun da taji Maganar accident ta mike tsaye tana kallon Sumayya tace "me ya samu Ruqayyah? Hatsari suka yi?" Sumayya ta gyada mata kai already hawaye yana zuba a idonta tace "hatsari sukayi wai Fatima ta mutu. Allah sarki Fatima. Innalillahi wa inna ilaihir rajiun" ta fada tana neman hijab dinta. Sannan suka fito palo tare da Inna ita kuma tana nemna waya ta kira Baba ta gaya masa zasu tafi asibiti gurin Ruqayyah, a lokacin ne shi kuma baban suka shigo sun dawo daga masallaci tare da Suleiman. Sulaiman yana goge hawaye, Sumayya tace "kunji labarin kuma ko? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Allah yaji kan Fatima" Baba yace "wacce Fatima ce kuma ta rasu? Mu yanzu ake gaya mana mutuwar yaron nan dan uwan Hassan. Hussain. Yanzu aka kawo gawarsa daga Abuja"
Sumayya ta dora hannu aka Baba ya daga mata hannu, "kar kiyi, ba da haka zaki nuna wa Ubangiji godiyar ki daya baki rai shima ya bashi rai sannan ya ƙaddara saduwar ku a duniya ba" Sumayya ta sauke hannnun tana sheshshekar kuka, Inna Ade tana tayata. Sannan Inna ta gaya musu kiran da Ruqayyah tayi musu da sakon data sanar dasu. Nan take suka shirya gabaki dayan su suka hau Napep din Sulaiman suka tafi asibitin.
Asibitin da aka kai Ruqayyah dana shine asibitin da suke zuwa, dan hka suna zuwa ba tare da wani matsala ba aka karbe ta aka bata taimakon gaggawa kafin karasowar likita. Kafin likitan yazo su Baba sunzo, sun kuma ji dadin yadda suka ganta complete ba tare da ta rasa wani abu na jikinta ba a hatsarin da ita kadai ta fita da rai. Wannan babban abin godiya ga Allah ne. Bayan likitan yazo yayi mata complete check up sai ya fahimci ko karaya bata dashi sai tarkade a hannun ta na hagu wanda ita Ruqayyan ma bata san dashi ba sai kuma ciwon da taji a cinyarta, wanda karfe ne ya soke ta a gurin. Amma problem din shine complain da take yi cewa kafar ta makale, ta kuma fadi cewa farkon data tashi tana iya motsa ta amma yanzu ta kasa. Sai doctor din ya rubuta mata hoto da za'a yi mata a kafar da safe yadda za'a fi ganin komai. Daga nan ya barta aga yanuwanta.
Har magrib tayi, sai ta kuma dauko waya ta kira Hassan amma bai dauka ba, ta kira Fatima not reachable Ruqayyah switched off. Ta kira Hussain shima ba'a dauka ba. Hankalin ta yayi dubu ya tashi, ta shiga dakin Khadijah ta tarar da ita a kwance wai zazzaɓi takeyi, ta dafa jikin ta taji zafi sosai, sai ta koma dakinta ta dauko mata magani ta taho da niyyar zata bata sai taga kira daga Bauchi. Babban yayan su Alhaji Lukman, tayi gyaran murya ta dauka tana gaishe shi, sai taji yayi shiru kafin ya amsa sannan yace mata "duk kuna gida tare da yara?" Tace "eh" tana mamakin tambayarsa, sai yace "shikenan ku zauna a gidan gamu nan tahowa komai dare insha Allah" sai ya kashe wayar ya barta da sakakken baki. Me zai zo yayi komai dare? Koma menene a barwa gobe mana?
Ta samu gefen gado ta zauna kusa da kafafuwan Khadijah tana cigaba da kiran number din Hassan da Hussain amma duk babu wanda ya dauka. Ta gaji ta tashi ta daga window tana hangen titi ko zata hango tahowar su amma babu alamar su.
A lokacin ne taji an rusa ihun kuka da muryar Nafisa, taji wani abu ya tsirga mata tun daga kanta har tafin kafarta. Taji wani irin daci a makwogwaron ta. Sai taji sautin kukan Nafisa yayi mata kama da sautin kukanta a lokacin mutuwar Alhaji Aminu uban ƴaƴan ta.
Khadijah da take kwance ta mike da sauri ta tafi dakin Nafisa tana hardewa, a hanya suka hadu da Zulaihat itama tana dosar dakin Nafisa. A dai dai lokacin Aunty taga tsayawar ambulance a kofar gidan. Ta sandare a gurin tana kallo aka bude gate aka shigo da ambulance din sannan akayi packing aka bude baya, taga police sun fito, sannan taga Hassan ya fito amma bata ga Hussain ba sai taga an turo gado da wani abu da yayi kama da gawa akai. Ta saki labulen sannan a hankali ta zame ta zube a gaban tagar.
Hassan yabi gawar Hussain da kallo ya tabbatar an shiga da ita ciki sannan ya juya gurin limamin unguwar su da ya biyo bayan motar rasu. Ashe har sun samu labari sun zauna jira. Hussain mutumin kirki.
Liman yace "dare yayi yanzu, sai dai yayi kwanan keso sai da safe ayi masa sallah" Hassan ya gyada kai kawai. Liman din yace "da assuba zan tura aje makabarta a haka kabari, yanzu kuma zan sika a siyo likkafani, sai asa lokaci saboda yan uwanku su sami sallah" sai Hassan ya girgiza kansa yana kallon garden din gidan, inda tun suna raya suke yin shuke shuke shida Hussain har suyi rigima in wani ya tabata wani yace "anan za'a binne shi, a cikin garden din mu. Nayi masa alkawarin zanke zuwa kabarinsa kullum ina masa addu'a. Anan za'a binne shi a kusa dani"
Wannan littafin na siyarwa ne, idan kin ganshi a wani gurin na sata ne, in kina so ki karanta halaliyar ki kiyi min magana ta WhatsApp through wannan number 08067081020
Sorry about the typos please
Mai sharing littafi, bana ganin ki Amma *Allah* yana kallon ki kuma na barki da shi*Hidden Strength*
Sumayya yau bata tashi daga school ba sai da akayi kusa kiran sallar magrib. Ta gaji likis saboda yau sun safe suke lectures babu kakkautawa, dan yau sau daya taga Adam shima briefly yazo wai zasuyi sallama zai je Abuja tare da oga Hussain. Tana murmushi tave masa "kwana nawa zakuyi?" Yace "yau zamu dawo" tace "yau zaku dawo din shine harda sallama?" Ya langwabe kai "kika sani ko kawai so nake yi in ganki shine na fake da sallama" ta dan rufe fuska da mayafi, ya kama mayafin yana leka fuskar. Ta rufe idonta "ka bari fa" yace "ni ba zan bari ba, kallon fuskarki ma yanzu na fara" ta kwace mayafinta tana kara rufe fuskar dashi, yayi murmushi yace "kinsan wani abu?" Ta girgiza kai, yace "so nake in mun gama semester din nan inyi wa oga Hussain maganar mu, so nake a fara maganar auren mu tun yanzu ba wai sai mun gam school ba tunda kinga ai ina da aikina kuma ina samun kudi ba laifi, tunda na fara aikin kuma nake tarawa ba wani abin nke yi dashi ba. In nayi masa Magana nasan zai yi min jagora a maganar auren insha Allah"
Sai taji ranta yayi mata dadi, zuciyarta tayi fari tas, yace "kin amince da hakan?" Ta gyada kai tana murmushi, still fuskarta a boye, ita da ace amimcewarta kadai ake bukata da zata iya auren Adam ko da bashi da wannan aikin, koda sadaki kadai zai bayar babu lefe babu komai, thats how much take son shi. Da zasu rabu ya jaddada mata "you know I love you right?" Ta danyi murmushi tana kallon cikin idonsa ta gyada kai, sannan kuma kamar ba zata yi magana ba sai tace "and I love you too".
Har yanzu, har bayan ta wuni sir a makaranta ta dawo gida a gajiye da yunwa da ƙishirwa amma bata daina jin kaifin kallon da yayi mata a jikinta ba. Tana cin abinci tana zuba murmushi ita kadai, tayi sallah tayi wanka ta fito tama shiryawa Inna Ade ta shigo tana kallon ta. "Ke kuma fa kike ta farin ciki kamar anyi miki albishir da kujerar makka? Au ashe ba kinje, dan haka ba lallai ne ma kiyi farin cikin da kike yi yanzu ba" samayya tayi dariya, "haba Inna, farin ciki ma kuwa ai har marar misaltuwa zanyi in za'a mayar dani in sake ganin Ka'aba. Amma dai duk son da nake yiwa komawar in dai aka bani a yanzu sai dai in baki ko Baba tunda ni na sauke farali" Inna ta zauna a gefen gado tace "to gaya min abind yake saka ki wannan farin ciki haka"Sumayya ta zauna a kusa da inna tana kare mata kallo. Cikin yan shekarun nan da suka dawo gidan nan baba kuma ya samu aiki duk Inna ta chanja, jikinta ya murmure sosai babu wannan muguwar ramar fatarta tayi kyau tayi haske, kyawunta ya sake fitowa sosai. Sai Sumayya tace "kawai dai ina duba rayuwa shine naji raina yayi dadi sosai. Ina duba halin da mutanen da nake tsananin so suke ciki misali ku Iyaye na, Ruqayyah, kannena da sauran su duk kowa yana cikin rayuwa mai kyau sai naji zuciya ta tayi dadi sosai" Inna tace "banji kin lissafa da Adam ba" Sumayya ta sunkuyar da kai, Inna tace "ko shine da sauransu din?" Sai Sumayya ta rufe fuskarta, a dai dai lokacin wayarta tayi kara, ta bude idon ta tana kallon bakuwar number din da bata sani ba sannan ta dauka a hankali tare da sallama "Assalamu alaikum" daga daya barin taji muryar Ruqayyah "Sumayya nice, yar uwarki Ruqayyah ce. Accident muka yi ni da m.......... nida Fatima, Allah ya musu rasuwa ita da driver. An tafi dani asibiti ni kuma"
Sumayya ta zaro ido cikin tashin hankali "accident? Mutuwa? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Ya kike Ruqayyah me ya same ki ke? Wanne asibitin?" Ta jera mata tambayoyin cikin tashin hankali. Ruqayyah tace "da sauki. Asibitin da nake haihuwa. Ki gaya wa su Inna" sai ta kashe.
Inna Ade da dama tun da taji Maganar accident ta mike tsaye tana kallon Sumayya tace "me ya samu Ruqayyah? Hatsari suka yi?" Sumayya ta gyada mata kai already hawaye yana zuba a idonta tace "hatsari sukayi wai Fatima ta mutu. Allah sarki Fatima. Innalillahi wa inna ilaihir rajiun" ta fada tana neman hijab dinta. Sannan suka fito palo tare da Inna ita kuma tana nemna waya ta kira Baba ta gaya masa zasu tafi asibiti gurin Ruqayyah, a lokacin ne shi kuma baban suka shigo sun dawo daga masallaci tare da Suleiman. Sulaiman yana goge hawaye, Sumayya tace "kunji labarin kuma ko? Innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Allah yaji kan Fatima" Baba yace "wacce Fatima ce kuma ta rasu? Mu yanzu ake gaya mana mutuwar yaron nan dan uwan Hassan. Hussain. Yanzu aka kawo gawarsa daga Abuja"
Sumayya ta dora hannu aka Baba ya daga mata hannu, "kar kiyi, ba da haka zaki nuna wa Ubangiji godiyar ki daya baki rai shima ya bashi rai sannan ya ƙaddara saduwar ku a duniya ba" Sumayya ta sauke hannnun tana sheshshekar kuka, Inna Ade tana tayata. Sannan Inna ta gaya musu kiran da Ruqayyah tayi musu da sakon data sanar dasu. Nan take suka shirya gabaki dayan su suka hau Napep din Sulaiman suka tafi asibitin.
Asibitin da aka kai Ruqayyah dana shine asibitin da suke zuwa, dan hka suna zuwa ba tare da wani matsala ba aka karbe ta aka bata taimakon gaggawa kafin karasowar likita. Kafin likitan yazo su Baba sunzo, sun kuma ji dadin yadda suka ganta complete ba tare da ta rasa wani abu na jikinta ba a hatsarin da ita kadai ta fita da rai. Wannan babban abin godiya ga Allah ne. Bayan likitan yazo yayi mata complete check up sai ya fahimci ko karaya bata dashi sai tarkade a hannun ta na hagu wanda ita Ruqayyan ma bata san dashi ba sai kuma ciwon da taji a cinyarta, wanda karfe ne ya soke ta a gurin. Amma problem din shine complain da take yi cewa kafar ta makale, ta kuma fadi cewa farkon data tashi tana iya motsa ta amma yanzu ta kasa. Sai doctor din ya rubuta mata hoto da za'a yi mata a kafar da safe yadda za'a fi ganin komai. Daga nan ya barta aga yanuwanta.