Sashe 3
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ta tuna farkon sanda aka siyo musu kekuna, ana kawowa Hussain ya dauka ya hau ai kuwa ya fado ya kukkurje, amma bai hakura ba, yayi ta hawa keken nan yana faduwa har sai da ta dauke saboda tausayin sa sai babansu yace ta bar masa ai a haka ake girma. Hassan kuwa sai yayi ta studying keken nan yana gwada yadda komai nasa yake aiki har sai da ya fahimce shi sannan ya hau, shima kuma a hankali yadda ko ya fadi ba zaiji ciwo ba, kuma bai fadin ba, sai yake tukawa a hankali yadda in yaga zai fadi sai yayi sauri ya sauka, ko kuma yake bin jikin bango yana dafawa.
A karshe sai ya zamanto Hussain ya riga Hassan iya keke, amma kuma duk ya ci uban keken nasa ya babballashi. Sanda Hassan ya iya nasa keken, keken Hussain ya riga ya lalace.
Amma kuma akwai wani abu a dangane da Hussain tun yana yaro, yana balain, tsananin son sana'a. Duk wani abu indai ance abinda zai kawo kudi ne to Hussain ya sanshi kuma yana sonshi. Hussain har fruits din bishiyar umbrella din gidansu yake cira ya siyar wa da yaran unguwa. Hussain in yaje da abu makaranta wani yaron yace yana so yakan iya siyar masa ya kara riba sannan ya fito waje ya sai wani. Amma fa kudin in ya samu rabarwa mutane yake yi.
Ta tuna wata rana da ya dawo daga school da ulu da kwarashi, ta tambaye shi inda ya samu sai yace "Nanny din mu ta makaranta na gani tana saƙa, tace min ana samun kudi sosai in akayi saƙa, shine na bata kudi ta siyomin zan ringa yin saƙar hula ina bata tana siyar min" sai da baban su ya zane shi akan sakar nan sannan ya daina.
Babansu ya taba tambayar su abinda zasu zama in sun girma. Hassan yayi shiru yana tunani sannan yace "ban sani ba Abba, sai nan gaba in nayi tunani" ana tambayar Hussain sai ya washe baki yace "Dangote".
Ta dawo da tunaninta kansa da har yanzu yake durkushe a gabanta yana roko, ya kamata ta bashi dama, amma ya kamata tayi tunani, saboda kamar yadda Hassan ya fada wannan future dinsu ne basu kadai ba harda yan kananan yaranta mata. Dole zata yi tunani kafin tayi taking wannan risk din kuma dole zata yi shawara. Shawara da abokin shawarar ta sarkin tunani. Hassan.
Tace "shikenan Hussain ka bani lokaci inyi tunani, duk abinda na yanke kuma shine final babu jayayya"
Ba haka yaso ba, amma yadda take so dole hakan za'ayi.
Bayan ya fita sai ta juyo ta kalli Hassan, a take ya girgiza mata kai.
Ta sauke ajjiyar zuciya tace "bana son discouraging dinsa, ka bani shawara yaya zanyi?"
Ya gyara zama yana kallon carpet yace "dukiyar marayu ce aunty, ina ji masa tsoro, kinsan halin Hussain in ya kafa kasuwancin ma raba wa mutane zai tayi" Ta gyada kai cikin fahimta, ya cigaba da cewa "a shawarce ina ganin a raba, a fitar masa da kasonsa a bashi ya kafa kasuwancin dashi yadda ko sun rushe ba zai rusa mu gabaki daya ba, mu dashi zamu samu abinda zamu dogara dashi. Idan kuma ya zama successful sai a kara masa wata"
Aunty taji dadin wannan shawarar, amma kuma a ranta bata son rabon gadon nan saboda tana ganin kamar raba kan ƴaƴanta ne, taso a ce komai zasuyi tare zasuyi. Amma kuma shawarar abar dubawa ce.
Haka akayi, aka raba gado aka bawa Hussain nasa, sauran kuma suka ajiye suna amfani dashi gurin harkokin rayuwarsu. Hassan yayi amfani da wani kaso a cikin nasa gurin nema wa kansa makaranta.
A lokacin da shekara ta zagayo Hussain ya kira su yana nuna musu lissafin abubuwan da yayi da kudin da ya samu sai su ka ga cewa kudin da yake dashi a yanzu ya ninka wanda yake dasu a waccan shekarar sau huɗu har da doriya. Suka rike baki suna mamaki, shi kuma ya gyara zama yana murmushi yace "na gaya muku ai, Dangote zan zama"
Ga masu son siya zasu iya turo kudinsu ₦300 ta account
GT Bank
Account Name : Nafisa Usman Tafida
Account Number : 0139433741
Sai su turo shaidar transaction din ta hanyar WhatsApp zuwa wannan layin
08067081020
Wadanda basu da account zasu turo katin MTN na ₦300 zuwa wannan layin
08067081020.
Dan girman Allah banda kira, WhatsApp only
Sai na jiku....👬🏻 TAGWAYE 👭🏻
By
Maman Maama
Free episode
Episode Four: Gimbiya Fatima
Hayin Rigasa,
Kaduna state
Yammata biyu na gani suna shigowa cikin gidan su wanda katangar sa ta kasa ta zube dan haka aka zagaye shi da tsohon langa langa, sai dakuna guda biyu a tsakiyar gidan suma dakunan na kasa ne amma anyi musu plaster da siminti, a gefe akwai bandaki shima rabinsa na langa langa ne kuma babu rufi, tsakar gidan gabaki dayansa kasa ne da bishiya a gefe a kasanta akwai murhu da tukwane da sauran kayayyakin da suke nuna anan ake girki, sai kofar dakunan da akayi yar karamar baranda, wadda simintin ta duk ya mutu yayi ramuka.
A gefen barandar akwai jerin alluna da gwangwanin tauwada.
Jikin yammatan sanye yake da uniform. Kansu daya, kamannin su daya, yanayin su daya dan sai ka kalla sosai, ko kuma wanda ya riga ya sansu sannan ake iya gane banbancinsu.
Dariya suke yi suma, karar dariyar su ta hade da karar kofar gidan da suka bude, wanda ko soro babu, hannayensu sarkafe dana juna suna tafiya ƙafafuwan su suna hardewa cikin na juna.
"Ruqayyah baki da kirki wallahi, hahhaha, kinga yadda kika ruda shi kuwa ya kasa gane ina ne kofar fita daga ajin?" Wadda aka kira da Ruqayyah ta rike ciki tana dariya, sannan tace "kinga ai gobe ma ya kuma dan kaniyar sa....., Ko waye ya gaya masa ni sa'ar sa ce? Harda wani "wallahi Rukee da gaske nake sonki nake yi, ni ban taba kula ko wacce mace ba sai ke" ta karashe maganar cikin kwaikwayon muryar maza.
Suka sake kwashewa da dariya, dayar tace "baki da tausayi wallahi, kika sani ko da gasken yake?" Ruqayyah tace "to ke Sumayya, wadda aka haifo da layar tausayi a wuyanta ba sai kije ki ce kina sonsa ba? Ai ba lallai ne ya gane bani bace ba. Ni wannan me zanyi dashi? Me na sama yaci ballantana ya bawa na kasa?" Sumayya ta tura baki tace "ai ba ce miki nayi ina sonsa ba, ni cika min hannu ke da ba'a fada miki gaskiya" Ruqayyah ta warce hannunta tare da hankada Sumayya gaba "in kina son Allah da annabin sa, daga yau kar ki kara gayamin gaskiya".
A lokacin mamansu ta fito daga daki, doguwar macece kyakykyawa, baka, daga ganinta kasan anyi kyakykyawa a zamanin yarintarta. Amma a yanzu fatarta duk ta yamushe tamkar tafi shekarun ta, bakinta a bushe, hannayenta rudu rudu da jijiyoyi. Gefen rigarta a yage. Ta tsaya da labule a hannunta tana kallonsu tace "to sarakan rigima, ku dai kamar masu ganin hanjin juna ba kwa minti biyar tare sai kun yi fada. Me ya faru kuma?" Ruqayyah tazo ta wuce ta kusa da ita tana kunkuni ta shige dakin da yake kusa da inda maman nasu ta fito, Sumayya ta karaso gabanta tace "Inna Ade barka da gida. Mun dawo. Akwai abinci?"
Inna Ade tayi ajjiyar zuciya, haka suke tunda ta haife su, sunfi shiri da junansu akan kowa kuma sunfi fada da junansu akan kowa, sannan ko wanene kai baka isa kaji sirrinsu ba. Ta amsa gaisuwar Sumayya Sannan ta nuna mata kwano a gefe wanda tun daga wajensa zaka ga ya farfashe, murfinsa daban.
Sumayya ta dauka ta shiga dakin da Ruqayyah ta shiga. "Rukee ga abincin mu. Za muci yanzu ko sai munyi sallah?" Ruqayyah ta ajiye hijab din da take ninkewa a gefen yamusashshiyar katifar su, ta bude kwanon abincin sannan ta saki murfin ya fadi a kan sumuntin dakin tace "again! Yau ma shinkafa da mai da yaji? Yau ko waken babu?" Ta karashe maganar kamar zata yi kuka. Sumayya takaraso tana kallon abincin sannan ta tabe baki tace "ni yunwa nake ji, damuwata shine ba lallai abincin ya ishe mu ba"
Ruqayyah ta cigaba da cire uniform dinta tace "ki haɗa da nawa ki cinye duka, ni ba zanci wannan abincin ba, ni na gaji da cin irin wadannan abincin. Ni na gaji da talauci, ni so nake muyi kudi, na gaji da gidan nan, na gaji da kayan da muke sakawa na gaji da inda muke kwanciya. Na gaji da rayuwa" ta saka kafa tana haurin katifar tasu, sannan ta zauna dabas a gefe ta hade kai da gwuiwa.
Sumayya ta bita da kallo da sakakken baki, sannan ta zauna a gefenta ta jawo kwanon ta juya abincin ta fara ci sannan tace "kinga, kin san dai in baki ci abincin nan ba babu abinda zaki ci ko? Kinsan tabbas da daddare tuwo za'a yi kuma nasan shima cewa zaki yi ba zaki ci ba, ƙin cin fara da mai ba zai saka gasassun kaji suyi fiffike su zo gabanki ba ko?" Jin bata ce komai ba ya saka ta kara cewa "In baki ci abinci ba kuma kinsan ba zaki samu karfin zuwa makaranta kiyi exams gobe ba"
Hakan yasa Ruqayyah ta miki hannu a hankali ta saka a cikin kwanon abincin, sannan ta debi loma ta saka a baki tana taunawa kamar mai cin kashi. Babu abinda bata so irin abinda zai kawo mata cikas a cikin ssce exams din da suke yi a yanzu, dan tana ganin zuwa makaranta shine kadai hanyarta na cikar burinta, burinta na zama mai kudi.
********************************
A bangaren samarin, bayan sunje warehouse din da suka tafi, sun gama duk abubuwan da zasu yi sun dauko hanyar dawowa sai suka biya ta gurin da ake ginin sabon companyn da za'a bude musamman saboda sarrafa rake a mayar dashi zuwa sukari. Wannan shine Company na uku da Hussain zai bude a cikin shekaru biyar da bude companyn sa na farko.
A karshe sai ya zamanto Hussain ya riga Hassan iya keke, amma kuma duk ya ci uban keken nasa ya babballashi. Sanda Hassan ya iya nasa keken, keken Hussain ya riga ya lalace.
Amma kuma akwai wani abu a dangane da Hussain tun yana yaro, yana balain, tsananin son sana'a. Duk wani abu indai ance abinda zai kawo kudi ne to Hussain ya sanshi kuma yana sonshi. Hussain har fruits din bishiyar umbrella din gidansu yake cira ya siyar wa da yaran unguwa. Hussain in yaje da abu makaranta wani yaron yace yana so yakan iya siyar masa ya kara riba sannan ya fito waje ya sai wani. Amma fa kudin in ya samu rabarwa mutane yake yi.
Ta tuna wata rana da ya dawo daga school da ulu da kwarashi, ta tambaye shi inda ya samu sai yace "Nanny din mu ta makaranta na gani tana saƙa, tace min ana samun kudi sosai in akayi saƙa, shine na bata kudi ta siyomin zan ringa yin saƙar hula ina bata tana siyar min" sai da baban su ya zane shi akan sakar nan sannan ya daina.
Babansu ya taba tambayar su abinda zasu zama in sun girma. Hassan yayi shiru yana tunani sannan yace "ban sani ba Abba, sai nan gaba in nayi tunani" ana tambayar Hussain sai ya washe baki yace "Dangote".
Ta dawo da tunaninta kansa da har yanzu yake durkushe a gabanta yana roko, ya kamata ta bashi dama, amma ya kamata tayi tunani, saboda kamar yadda Hassan ya fada wannan future dinsu ne basu kadai ba harda yan kananan yaranta mata. Dole zata yi tunani kafin tayi taking wannan risk din kuma dole zata yi shawara. Shawara da abokin shawarar ta sarkin tunani. Hassan.
Tace "shikenan Hussain ka bani lokaci inyi tunani, duk abinda na yanke kuma shine final babu jayayya"
Ba haka yaso ba, amma yadda take so dole hakan za'ayi.
Bayan ya fita sai ta juyo ta kalli Hassan, a take ya girgiza mata kai.
Ta sauke ajjiyar zuciya tace "bana son discouraging dinsa, ka bani shawara yaya zanyi?"
Ya gyara zama yana kallon carpet yace "dukiyar marayu ce aunty, ina ji masa tsoro, kinsan halin Hussain in ya kafa kasuwancin ma raba wa mutane zai tayi" Ta gyada kai cikin fahimta, ya cigaba da cewa "a shawarce ina ganin a raba, a fitar masa da kasonsa a bashi ya kafa kasuwancin dashi yadda ko sun rushe ba zai rusa mu gabaki daya ba, mu dashi zamu samu abinda zamu dogara dashi. Idan kuma ya zama successful sai a kara masa wata"
Aunty taji dadin wannan shawarar, amma kuma a ranta bata son rabon gadon nan saboda tana ganin kamar raba kan ƴaƴanta ne, taso a ce komai zasuyi tare zasuyi. Amma kuma shawarar abar dubawa ce.
Haka akayi, aka raba gado aka bawa Hussain nasa, sauran kuma suka ajiye suna amfani dashi gurin harkokin rayuwarsu. Hassan yayi amfani da wani kaso a cikin nasa gurin nema wa kansa makaranta.
A lokacin da shekara ta zagayo Hussain ya kira su yana nuna musu lissafin abubuwan da yayi da kudin da ya samu sai su ka ga cewa kudin da yake dashi a yanzu ya ninka wanda yake dasu a waccan shekarar sau huɗu har da doriya. Suka rike baki suna mamaki, shi kuma ya gyara zama yana murmushi yace "na gaya muku ai, Dangote zan zama"
Ga masu son siya zasu iya turo kudinsu ₦300 ta account
GT Bank
Account Name : Nafisa Usman Tafida
Account Number : 0139433741
Sai su turo shaidar transaction din ta hanyar WhatsApp zuwa wannan layin
08067081020
Wadanda basu da account zasu turo katin MTN na ₦300 zuwa wannan layin
08067081020.
Dan girman Allah banda kira, WhatsApp only
Sai na jiku....👬🏻 TAGWAYE 👭🏻
By
Maman Maama
Free episode
Episode Four: Gimbiya Fatima
Hayin Rigasa,
Kaduna state
Yammata biyu na gani suna shigowa cikin gidan su wanda katangar sa ta kasa ta zube dan haka aka zagaye shi da tsohon langa langa, sai dakuna guda biyu a tsakiyar gidan suma dakunan na kasa ne amma anyi musu plaster da siminti, a gefe akwai bandaki shima rabinsa na langa langa ne kuma babu rufi, tsakar gidan gabaki dayansa kasa ne da bishiya a gefe a kasanta akwai murhu da tukwane da sauran kayayyakin da suke nuna anan ake girki, sai kofar dakunan da akayi yar karamar baranda, wadda simintin ta duk ya mutu yayi ramuka.
A gefen barandar akwai jerin alluna da gwangwanin tauwada.
Jikin yammatan sanye yake da uniform. Kansu daya, kamannin su daya, yanayin su daya dan sai ka kalla sosai, ko kuma wanda ya riga ya sansu sannan ake iya gane banbancinsu.
Dariya suke yi suma, karar dariyar su ta hade da karar kofar gidan da suka bude, wanda ko soro babu, hannayensu sarkafe dana juna suna tafiya ƙafafuwan su suna hardewa cikin na juna.
"Ruqayyah baki da kirki wallahi, hahhaha, kinga yadda kika ruda shi kuwa ya kasa gane ina ne kofar fita daga ajin?" Wadda aka kira da Ruqayyah ta rike ciki tana dariya, sannan tace "kinga ai gobe ma ya kuma dan kaniyar sa....., Ko waye ya gaya masa ni sa'ar sa ce? Harda wani "wallahi Rukee da gaske nake sonki nake yi, ni ban taba kula ko wacce mace ba sai ke" ta karashe maganar cikin kwaikwayon muryar maza.
Suka sake kwashewa da dariya, dayar tace "baki da tausayi wallahi, kika sani ko da gasken yake?" Ruqayyah tace "to ke Sumayya, wadda aka haifo da layar tausayi a wuyanta ba sai kije ki ce kina sonsa ba? Ai ba lallai ne ya gane bani bace ba. Ni wannan me zanyi dashi? Me na sama yaci ballantana ya bawa na kasa?" Sumayya ta tura baki tace "ai ba ce miki nayi ina sonsa ba, ni cika min hannu ke da ba'a fada miki gaskiya" Ruqayyah ta warce hannunta tare da hankada Sumayya gaba "in kina son Allah da annabin sa, daga yau kar ki kara gayamin gaskiya".
A lokacin mamansu ta fito daga daki, doguwar macece kyakykyawa, baka, daga ganinta kasan anyi kyakykyawa a zamanin yarintarta. Amma a yanzu fatarta duk ta yamushe tamkar tafi shekarun ta, bakinta a bushe, hannayenta rudu rudu da jijiyoyi. Gefen rigarta a yage. Ta tsaya da labule a hannunta tana kallonsu tace "to sarakan rigima, ku dai kamar masu ganin hanjin juna ba kwa minti biyar tare sai kun yi fada. Me ya faru kuma?" Ruqayyah tazo ta wuce ta kusa da ita tana kunkuni ta shige dakin da yake kusa da inda maman nasu ta fito, Sumayya ta karaso gabanta tace "Inna Ade barka da gida. Mun dawo. Akwai abinci?"
Inna Ade tayi ajjiyar zuciya, haka suke tunda ta haife su, sunfi shiri da junansu akan kowa kuma sunfi fada da junansu akan kowa, sannan ko wanene kai baka isa kaji sirrinsu ba. Ta amsa gaisuwar Sumayya Sannan ta nuna mata kwano a gefe wanda tun daga wajensa zaka ga ya farfashe, murfinsa daban.
Sumayya ta dauka ta shiga dakin da Ruqayyah ta shiga. "Rukee ga abincin mu. Za muci yanzu ko sai munyi sallah?" Ruqayyah ta ajiye hijab din da take ninkewa a gefen yamusashshiyar katifar su, ta bude kwanon abincin sannan ta saki murfin ya fadi a kan sumuntin dakin tace "again! Yau ma shinkafa da mai da yaji? Yau ko waken babu?" Ta karashe maganar kamar zata yi kuka. Sumayya takaraso tana kallon abincin sannan ta tabe baki tace "ni yunwa nake ji, damuwata shine ba lallai abincin ya ishe mu ba"
Ruqayyah ta cigaba da cire uniform dinta tace "ki haɗa da nawa ki cinye duka, ni ba zanci wannan abincin ba, ni na gaji da cin irin wadannan abincin. Ni na gaji da talauci, ni so nake muyi kudi, na gaji da gidan nan, na gaji da kayan da muke sakawa na gaji da inda muke kwanciya. Na gaji da rayuwa" ta saka kafa tana haurin katifar tasu, sannan ta zauna dabas a gefe ta hade kai da gwuiwa.
Sumayya ta bita da kallo da sakakken baki, sannan ta zauna a gefenta ta jawo kwanon ta juya abincin ta fara ci sannan tace "kinga, kin san dai in baki ci abincin nan ba babu abinda zaki ci ko? Kinsan tabbas da daddare tuwo za'a yi kuma nasan shima cewa zaki yi ba zaki ci ba, ƙin cin fara da mai ba zai saka gasassun kaji suyi fiffike su zo gabanki ba ko?" Jin bata ce komai ba ya saka ta kara cewa "In baki ci abinci ba kuma kinsan ba zaki samu karfin zuwa makaranta kiyi exams gobe ba"
Hakan yasa Ruqayyah ta miki hannu a hankali ta saka a cikin kwanon abincin, sannan ta debi loma ta saka a baki tana taunawa kamar mai cin kashi. Babu abinda bata so irin abinda zai kawo mata cikas a cikin ssce exams din da suke yi a yanzu, dan tana ganin zuwa makaranta shine kadai hanyarta na cikar burinta, burinta na zama mai kudi.
********************************
A bangaren samarin, bayan sunje warehouse din da suka tafi, sun gama duk abubuwan da zasu yi sun dauko hanyar dawowa sai suka biya ta gurin da ake ginin sabon companyn da za'a bude musamman saboda sarrafa rake a mayar dashi zuwa sukari. Wannan shine Company na uku da Hussain zai bude a cikin shekaru biyar da bude companyn sa na farko.