Sashe 133
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A lokacin suka jiyo maganar shamaki, "takawa sannu, zaki ɗaukawa sannu, sunkuye alher" Hakan yana nufin mai martaba sarki ne da kansa ya taho gurin, abinda baya taba yi, baya taba shigowa bangaren matansa sai dai in watace a cikin su bata da lafiya ko wata a cikin yayansa. Jin haka yasa ka Fatima ta saki Hajiya ta kuma fita a guje zuwa inda yake tahowa, ita dama can tun tana karama yar babanta ce, ma'ana tafi shakuwa da babanta akan kowa, yaga tahowar ta, yakuma gane ta, ba ko girgiza ba ballantana yaji tsoro sai ma farin ciki da ya cika zuciyar sa cewa labarin da aka kai masa gaskiya ne, Fatima bata mutu ba kuma ta dawo gida.
Tana zuwa ya shige jikin sa tana kuka, "wallahi ban mutu ba Takawa, ina imo, ina can an rufe ni an hana ni tahowa, ina can bani da lafiya Baba". Bai amsa mata ba sai ya rungume ta yana shafa kanta, a ransa yana tasbihi ga ubangiji daya dawo masa da Fatima duk da cewa bai taba addu'a akan hakan ba, bai taba yi ba saboda bai san cewa hakan zai iya kasance wa ba, bai san cewa tana da rai ba.
Sai kuma ta cika shi da sauri ta dago kai tana kallonsa sa, zuciyarta a karye, yana yin fuskarta kadai ya isa ya saka mai karyayyiyar zuciya yayi kuka, tace "Baba ina Hussain? Ina Hussain dina? Baba dan Allah ka gaya min ba gaskiya ba ne ba abinda naji, dan Allah ka gaya min bai neme ni ba saboda shima ya dauka na mutu, ka gaya min cewa yana nan yana kukan rashina ba wai ni ce zanyi kukan rashin sa ba".
Dauke kansa yayi gefe ya lasa hada ido da ita, hakan yana kara tabbatar mata da maganar da Adam ya gaya mata amma kullum take gayawa zuciyar ta cewaba haka bane ba, kullum take saka ran cewain ta dawo goda zata tarar cewa ba haka bane ba, amma expression din fuskar maimartaba sarki kadai ya saka ta fahimtar cewa yaudarar kanta take yi, Hussain ya mutu, shekaru biyar da suka wuce, ita da Hussain sai a Darussalam.
Sai ta sake shi sannan ta zame zuwa kan kafafuwan sa, idanuwan ta a kasa amma hawaye ya tsaya a cikin su, Kamar yadda duk tunani ya tsaya a zuciyarta fuskar Hussain kawai take gani.
Ta tuno da maganar sa
"wannan ciwon da yake damuna jarabawa ta ce, abinda zai same ni kuma jarabawar ki ne"
Ta girgiza kanta kamar ta girgiza lokacin daya gaya mata maganar "no, no, no, Hussain, babu abinda zai same ka, please babu abinda zai same ka, ba zan iya ba Hussain, ba zan iya rayuwa babu kai ba" Hajiya ta zo gurinta tana kuka ita ma, tana cewa "zaki iya Fatima, Allah ya san zaki iya shi yasa ya dora miki, sai ki karba kuma ki gode masa bisa ga sauran ni'imomin da yayi miki" ta dago tana kallon ta, her mind racing, sauran ni'imomin da Allah yayi mata? Hajiya tana nufin dan ta kenan? Danta da suka haifa ita da Hussain? Mai kama da Hussain?
Ta mike da sauri ta fara waige waige tana neman sa, tana neman yaro dan shekara biyar mai kama da Hussain ko da Hassan, yaron da tasan zata yi dedicating duk kan sauran rayuwarta a gun tabbatar da cewa ya samu kyakykyawar rayuwa ba tare da yayi kukan maraici ba, yaron da tasan zai goge mata dukkanin kewa da kadaicin Hussain.
"Ina yake?" Tace tana bin mutanen gurin da kallo, "Allah sarki, ya dauka bashi da uwa bashi da uba ko?" Ta share hawayen ta "it must have been so hard on him, it must have been so hard on all of you" amma sai ta ga duk suna binta da kallon rashin fahimta, wa take nema? Wa take nufin ya tashi ba uwa ba uba?
Ganin kallon da suke yi mata ya sake tsinka zuciyarta, God please no, not her son please. Bata son tayi musu tambayar dan bata shirya jin amsar da zasu bata ba, zuciyarta ba zata iya dauka ba. Sai ta tambayi kanta "me ya saka ta dawo gida, me nene yayi mata saura a gida? Ina ma dai da gaske ne abinda suke tunani, ina ma dai ta mutu a ranar nan kamar yadda suka yi zargi.
Duk da haka tana so taji me ya faru da dan nata, ta kama hannun umma "ina Da na?" Ta tambaya da wata irin murya data huda zuciyoyin duk wadanda suke gurin "ko yana gurin Hassan ne? Ku kawo min mota in tafi Kaduna in ganshi, ku gaya min inda yake don Allah".
Ummah tace "Fatima ke zamu tambaya ai inda yake, mu gawar da aka bamu muka binne da ciki a jikinta dan haka bamu nemi inda abinda yake cikin ki yake ba, mu duk mun dauka tare muka binne ku. Kin haihu ne dama kafin kuyi accident din? A ina kika haihu? A ina kika bar babyn?" Fatima ta dafe kanta da hannayenta biyu tana jin yadda kan ta yake juyawa, "innalillahi wa inna ilaihir rajiun" ta ringa fada cikin muryar ban tausayi. Duk iyayenta suka yi kanta kowa yana kokarin rarrashin ta
Maman Adam ce tazo itama tace "ku barta dan Allah ta huta, kar ku gaya mata abinda zai bata ranta Please" duk suka juyo suna kallonta, suna lissafin inda zasuyi placing dinta. An enamy or a friend? Amma sai aka dauki shawarar ta aka shigar da Fatima cikin gida, nan da nan kuma aka guda da shewa da murnar dawowar Fatima gida, labari ya bazu ko'ina cewa gawar da aka binne ba ta Fatima bace ba. Sai dai kowa aka gayawa labarin sai ya tambaya "how comes?" Lallai akwai zare cikin nadi.
Duk wannan murnar da ake yi Fatima bata tare da murna, bata kuka kuma bata dariya, tana dai zaune kawai tana kuma yin duk abinda aka umarce ta tayi batare da musu ko doki ba.
Kafin wani lokaci maganar ta zagaye ko ina, duk yan uwan Fatima sun samu labari kuma da yawadaga cikin su wadanda basa gida sun kamo hanyar gida, hatta wadanda basa kasar sun nemi next flight to Nigeria sun yi booking, Asma'u kuma da take gida already ta dauki hotunan Fatima ta tura wa yan uwadan su tabbatar da gaskiyar magana.
An sauki Adam a gurin saukar baki maza a waje, an kuma sauki Mama a kebantaccen guri a cikin gida har sai anji labari daga bakin Fatima tukunna kafin ayi tunanin matsayin ta a cikin maganar, sai dai ba Fatima ba kadai duk wanda aka gaya wa dawowar Fatima sai ya tambaya "har babyn suka dawo tare?" Amsar, ita take saka su cikin jimami da kuma tunanin ya akayi aka kwana a ragaya?
Bayan anyi sallar magrib ne maimaita sarki ya kira iyalinsa gabaki daya, immediate family dinsa, wadanda da yawa daga cikin su sun iso gidan kuma duk suna son suji inda maganar ta kwana.
Bayan sun zauna ne, fuskokin su dauke da mixed feelings na farin ciki da kuma jimami, Fatima a kusa da baban ta, fuskarta unreadable, sai aka gabatar da addu'a tare da godiya ga ubangiji akan wannan abin farin cikin daya same su tare da kuma neman jagorar sa akan duk hukuncin da zasu yanke.
Tambayar da tafi damun kowa a gurin ita Takawa ya fara yiwa Fatima. "Fatima Zahra, ina kike tsahon shekarun nan kuma mai ya hanaki dawowa gida? Ko kuma neman munki sanar mana a inda kike mu muje mu taho dake?" Ta dago kanta tana kallon sa, sannan cikin karamar murya tace "ina imo, bani da lafiya, kuma an rufe ni ba'a barina na fito ko da kofar gida, ban san yadda zanyi in neme ku ba" suka fara kallon juna cikin mamaki sannan Hajiya Ummah tace "imo? Ya akayi kika je imo?" Duk suka dawo da hankalin su kanta suna jiran amsa, amma ga mamakin su sai suka ga ta juya hannayenta, alamun bata sani ba.
Umar ya gyara zamansa yace "Fatima abinda ke cikin ki a lokacin fa? Kin san yadda akayi kika rabu dashi?" Idonta ya ciko da kwalla, ta dora hannunta akan cikinta sannan tace "ban sani ba Yaya, ni bansan komai ba, ni dai na ganni acan baninda lafiya, Adam ya gaya min accident mukayi ni bansan ma munyi accident din ba, ya gaya min tsinta ta yayi a daji sai kuma babansa ya hada mu gaba daya ya tafi damu can, ya gaya min shima bai ganni da ciki ba, yace sanda ya ganni babu ciki a jikina amma da alamar na haihu ne a lokacin, ni na dauka a inda muka yi hatsarin na haihu, na dauka an kawo muku babyn kuma kuna ta nemana, na dauka...." Muryarta ta makale saboda kukan da ya ci karfin ta, Hajiya, Ummah tare da yan uwan Fatima mata suna taya ta kukan.
Mazan kuma suna ta kokarin amfani da kwakwalwar su wajen ganin sun fahimci menene ya faru. Abubakar yace "tunda ga Fatima anan a gaban mu, wacece kenan muka binne da tsohon ciki? Menene dalilin da yasa aka faya mana cewa Fatimah ce bayan ba ita bace ba?" Umar ya juya gurin Fatima yana tausayin yadda take kuka na rashin sanin inda danta yake ga kuma mikin mutuwar mijinta, yace "Fatima Zahra, ki daure, ki tuna, ranar da kuka yi accident din menene ya faru? Dake da waye a cikin motar? Shin kunyi accident din ma ko ba kuyi ba? Ko wani cover up aka shirya dan a salwantar da ke da kuma abinda yake cikin ki? Ki tuna Fatima, ki bamu labarin menene ya faru, wannan ne zai taimaka mana gurin gano inda yaron yake".
Tana zuwa ya shige jikin sa tana kuka, "wallahi ban mutu ba Takawa, ina imo, ina can an rufe ni an hana ni tahowa, ina can bani da lafiya Baba". Bai amsa mata ba sai ya rungume ta yana shafa kanta, a ransa yana tasbihi ga ubangiji daya dawo masa da Fatima duk da cewa bai taba addu'a akan hakan ba, bai taba yi ba saboda bai san cewa hakan zai iya kasance wa ba, bai san cewa tana da rai ba.
Sai kuma ta cika shi da sauri ta dago kai tana kallonsa sa, zuciyarta a karye, yana yin fuskarta kadai ya isa ya saka mai karyayyiyar zuciya yayi kuka, tace "Baba ina Hussain? Ina Hussain dina? Baba dan Allah ka gaya min ba gaskiya ba ne ba abinda naji, dan Allah ka gaya min bai neme ni ba saboda shima ya dauka na mutu, ka gaya min cewa yana nan yana kukan rashina ba wai ni ce zanyi kukan rashin sa ba".
Dauke kansa yayi gefe ya lasa hada ido da ita, hakan yana kara tabbatar mata da maganar da Adam ya gaya mata amma kullum take gayawa zuciyar ta cewaba haka bane ba, kullum take saka ran cewain ta dawo goda zata tarar cewa ba haka bane ba, amma expression din fuskar maimartaba sarki kadai ya saka ta fahimtar cewa yaudarar kanta take yi, Hussain ya mutu, shekaru biyar da suka wuce, ita da Hussain sai a Darussalam.
Sai ta sake shi sannan ta zame zuwa kan kafafuwan sa, idanuwan ta a kasa amma hawaye ya tsaya a cikin su, Kamar yadda duk tunani ya tsaya a zuciyarta fuskar Hussain kawai take gani.
Ta tuno da maganar sa
"wannan ciwon da yake damuna jarabawa ta ce, abinda zai same ni kuma jarabawar ki ne"
Ta girgiza kanta kamar ta girgiza lokacin daya gaya mata maganar "no, no, no, Hussain, babu abinda zai same ka, please babu abinda zai same ka, ba zan iya ba Hussain, ba zan iya rayuwa babu kai ba" Hajiya ta zo gurinta tana kuka ita ma, tana cewa "zaki iya Fatima, Allah ya san zaki iya shi yasa ya dora miki, sai ki karba kuma ki gode masa bisa ga sauran ni'imomin da yayi miki" ta dago tana kallon ta, her mind racing, sauran ni'imomin da Allah yayi mata? Hajiya tana nufin dan ta kenan? Danta da suka haifa ita da Hussain? Mai kama da Hussain?
Ta mike da sauri ta fara waige waige tana neman sa, tana neman yaro dan shekara biyar mai kama da Hussain ko da Hassan, yaron da tasan zata yi dedicating duk kan sauran rayuwarta a gun tabbatar da cewa ya samu kyakykyawar rayuwa ba tare da yayi kukan maraici ba, yaron da tasan zai goge mata dukkanin kewa da kadaicin Hussain.
"Ina yake?" Tace tana bin mutanen gurin da kallo, "Allah sarki, ya dauka bashi da uwa bashi da uba ko?" Ta share hawayen ta "it must have been so hard on him, it must have been so hard on all of you" amma sai ta ga duk suna binta da kallon rashin fahimta, wa take nema? Wa take nufin ya tashi ba uwa ba uba?
Ganin kallon da suke yi mata ya sake tsinka zuciyarta, God please no, not her son please. Bata son tayi musu tambayar dan bata shirya jin amsar da zasu bata ba, zuciyarta ba zata iya dauka ba. Sai ta tambayi kanta "me ya saka ta dawo gida, me nene yayi mata saura a gida? Ina ma dai da gaske ne abinda suke tunani, ina ma dai ta mutu a ranar nan kamar yadda suka yi zargi.
Duk da haka tana so taji me ya faru da dan nata, ta kama hannun umma "ina Da na?" Ta tambaya da wata irin murya data huda zuciyoyin duk wadanda suke gurin "ko yana gurin Hassan ne? Ku kawo min mota in tafi Kaduna in ganshi, ku gaya min inda yake don Allah".
Ummah tace "Fatima ke zamu tambaya ai inda yake, mu gawar da aka bamu muka binne da ciki a jikinta dan haka bamu nemi inda abinda yake cikin ki yake ba, mu duk mun dauka tare muka binne ku. Kin haihu ne dama kafin kuyi accident din? A ina kika haihu? A ina kika bar babyn?" Fatima ta dafe kanta da hannayenta biyu tana jin yadda kan ta yake juyawa, "innalillahi wa inna ilaihir rajiun" ta ringa fada cikin muryar ban tausayi. Duk iyayenta suka yi kanta kowa yana kokarin rarrashin ta
Maman Adam ce tazo itama tace "ku barta dan Allah ta huta, kar ku gaya mata abinda zai bata ranta Please" duk suka juyo suna kallonta, suna lissafin inda zasuyi placing dinta. An enamy or a friend? Amma sai aka dauki shawarar ta aka shigar da Fatima cikin gida, nan da nan kuma aka guda da shewa da murnar dawowar Fatima gida, labari ya bazu ko'ina cewa gawar da aka binne ba ta Fatima bace ba. Sai dai kowa aka gayawa labarin sai ya tambaya "how comes?" Lallai akwai zare cikin nadi.
Duk wannan murnar da ake yi Fatima bata tare da murna, bata kuka kuma bata dariya, tana dai zaune kawai tana kuma yin duk abinda aka umarce ta tayi batare da musu ko doki ba.
Kafin wani lokaci maganar ta zagaye ko ina, duk yan uwan Fatima sun samu labari kuma da yawadaga cikin su wadanda basa gida sun kamo hanyar gida, hatta wadanda basa kasar sun nemi next flight to Nigeria sun yi booking, Asma'u kuma da take gida already ta dauki hotunan Fatima ta tura wa yan uwadan su tabbatar da gaskiyar magana.
An sauki Adam a gurin saukar baki maza a waje, an kuma sauki Mama a kebantaccen guri a cikin gida har sai anji labari daga bakin Fatima tukunna kafin ayi tunanin matsayin ta a cikin maganar, sai dai ba Fatima ba kadai duk wanda aka gaya wa dawowar Fatima sai ya tambaya "har babyn suka dawo tare?" Amsar, ita take saka su cikin jimami da kuma tunanin ya akayi aka kwana a ragaya?
Bayan anyi sallar magrib ne maimaita sarki ya kira iyalinsa gabaki daya, immediate family dinsa, wadanda da yawa daga cikin su sun iso gidan kuma duk suna son suji inda maganar ta kwana.
Bayan sun zauna ne, fuskokin su dauke da mixed feelings na farin ciki da kuma jimami, Fatima a kusa da baban ta, fuskarta unreadable, sai aka gabatar da addu'a tare da godiya ga ubangiji akan wannan abin farin cikin daya same su tare da kuma neman jagorar sa akan duk hukuncin da zasu yanke.
Tambayar da tafi damun kowa a gurin ita Takawa ya fara yiwa Fatima. "Fatima Zahra, ina kike tsahon shekarun nan kuma mai ya hanaki dawowa gida? Ko kuma neman munki sanar mana a inda kike mu muje mu taho dake?" Ta dago kanta tana kallon sa, sannan cikin karamar murya tace "ina imo, bani da lafiya, kuma an rufe ni ba'a barina na fito ko da kofar gida, ban san yadda zanyi in neme ku ba" suka fara kallon juna cikin mamaki sannan Hajiya Ummah tace "imo? Ya akayi kika je imo?" Duk suka dawo da hankalin su kanta suna jiran amsa, amma ga mamakin su sai suka ga ta juya hannayenta, alamun bata sani ba.
Umar ya gyara zamansa yace "Fatima abinda ke cikin ki a lokacin fa? Kin san yadda akayi kika rabu dashi?" Idonta ya ciko da kwalla, ta dora hannunta akan cikinta sannan tace "ban sani ba Yaya, ni bansan komai ba, ni dai na ganni acan baninda lafiya, Adam ya gaya min accident mukayi ni bansan ma munyi accident din ba, ya gaya min tsinta ta yayi a daji sai kuma babansa ya hada mu gaba daya ya tafi damu can, ya gaya min shima bai ganni da ciki ba, yace sanda ya ganni babu ciki a jikina amma da alamar na haihu ne a lokacin, ni na dauka a inda muka yi hatsarin na haihu, na dauka an kawo muku babyn kuma kuna ta nemana, na dauka...." Muryarta ta makale saboda kukan da ya ci karfin ta, Hajiya, Ummah tare da yan uwan Fatima mata suna taya ta kukan.
Mazan kuma suna ta kokarin amfani da kwakwalwar su wajen ganin sun fahimci menene ya faru. Abubakar yace "tunda ga Fatima anan a gaban mu, wacece kenan muka binne da tsohon ciki? Menene dalilin da yasa aka faya mana cewa Fatimah ce bayan ba ita bace ba?" Umar ya juya gurin Fatima yana tausayin yadda take kuka na rashin sanin inda danta yake ga kuma mikin mutuwar mijinta, yace "Fatima Zahra, ki daure, ki tuna, ranar da kuka yi accident din menene ya faru? Dake da waye a cikin motar? Shin kunyi accident din ma ko ba kuyi ba? Ko wani cover up aka shirya dan a salwantar da ke da kuma abinda yake cikin ki? Ki tuna Fatima, ki bamu labarin menene ya faru, wannan ne zai taimaka mana gurin gano inda yaron yake".