Sashe 131
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Basu jima da aure ba aka yi posting din ta a service, aka tura ta bayelsa, amma haka Hassan ya shige mata gaba har sai da aka dawo da ita nan Kaduna musamman saboda a lokacin tana fama da laulayin ciki. Sai ta fahimci cewa shi din tsayayyen mutum ne irin wanda zaka iya gayawa problem dinka ya tsaya maka har sai kun samu solution. And she wondered yadda akayi Ruqayyah take kiran sa da matsolo. A gurin Sumayya sam Hassan bashi da maƙon kudi kawai dai baya son almubazzaranci, baya son unnecessary spendings, irin mutum ya sayi abu ba tare da yana bukatar saba, ko ka sayi abu kawai dan kaga wani ya siya kai ma sai ka siya dan ace kana da shi, amma kuma duk abinda yake da amfani Hassan zai siya in abundance, dan kayan abinci drinks fruits kala kalan nama har sai tace sunyi yawa kar su lalace. Musamman duk abinda ya fahimci cewa tana so ko kuma yaran suna so to ya ringa siyowa kenan. Kuma ta lura haka yake yiwa su Aunty ma, kafin su nemi abu ya kai musu shi indai yasan suna bukatar sa. Baya sai ya Aunty gwala-gwalai, baya chanja wa kannensa waya duk wata irin yadda Hussain yayi musu but yana kula da dukkanin bukatun su yana tsayawa a duk kanin al'amuran su kamar yadda ya tsaya a auren Nafisa bayan ya tabbatar yayi mata securing aikin da zata mori ilimin ta dashi, babu wanda zai ce marainiya ce dan Hassan ya cike gurbin uba a gurin ta kuma a yanzu yana kan cike wa a wajen Zulaihat dan ya matsa mata number akan ta fito da miji haka nan tunda har sun gama service dinsu.
A bangaren Hassan kuma bayan abinda ya faru tsakanin sa da Ruqayyah bai taba tsammanin zai samu farin ciki a rayuwar aure ba amma sai gashi ya samu more than abinda yayi tunani ma. Sumayya ta kawo haske sosai cikin rayuwarsa shi yasa ya makala mata suna "Noorie". A yanzu ne kuma ya gaskata maganar Baba, a yanxu ne kuma ya fahimci mistake dinsa na danganta wani category na mutane da munanan halayya.
Tabbas auren sa da Ruqayyah tamkar lesson ne ubangiji ya koya masa kuma ya dauki darasi sosai, sannan kuma aurensa da Sumayya shi kuma sakayya ce Allah yayi masa saboda yadda ya bude hannayensa duk biyun ya karbi kaddarorin rayuwarsa tare da gode Allah a bisa niimomin sa.
Gasu dai Sumayya da Ruqayyah tagwaye ne, uwa daya uba daya, ciki daya mahaifa daya, sun kuma sha nono daya a lokaci daya, sun rayu a guri daya, an yi musu tarbiyya iri daya sun kuma samu ilimi iri daya, hatta cup da plate din da suka ci abinci sanda suna tasowa iri daya ne gashi kuma kamannin su daya amma banbancin halayyar tamkar banbancin dake tsakanin annabi da kafiri ne. Kamar ace positive and negative sides of a battery ne.
Shine zai bada wannan shaidar sama da kowa tunda shine wanda yasan in and out of them, shi yayi zaman aure da duk su biyun a mabanbanta lokuta.
Shekarar farko ta bayan aurensu Allah ya azurta su da haihuwar da namiji wanda suka saka wa Abdullahi.
Tabbas, a farkon auren su har zuwa yanzu ma da suke shekara uku da yin aure sukan fuskanci financial problems, saboda Hassan yanzu ba ya aikin da zai ke samun albashi duk wata, sannan auren da yayi da kuma auren da yayi wa kanensa har biyu Khadijah da Nafisa ya dakatar da harkar gine ginen sa, estate din nan ta farko dai har yanzu ita ce, har yanzu bai samu ya kammala ta biyun ba, kuma gidajen yearly suke biyan sa rent ba monthly ba dan haka dan ma dai shi mai kulawa ne da lissafi a komai shi yasa har suke samun condition din da suke ciki a yanzu.
Akwai lokacin da har sai da ya siyar da motar sa yake hawa ta haya saboda rashin kuɗi, amma fa iyalinsa basu taba zamada yunwa ba. Sai Sumayya ta bashi shawarar kafin ya kammala wannan ginin ya yi shaguna a gaban estate din sai ya saka musu monthly rents yadda duk wata zai ke karbar wani abu, sannan itama kuma ta nemi ya amince mata ya nema mata aiki amma sai yaki yadda da maganar aikin duk da cewa ya ji dadin waccan shawarar data bashi ta shaguna, dan haka sai yace mata ya bata aiki a karkashin sa a matsayin personal adviser dinsa, zai ke bata salary duk wata, ita kuma taki yarda tunda already yana bata kudin da suke isarta yin duk bukatun ta.
Shi kuma sai yaji babu dadi, dan yasan yadda Baba yasha wahala akan karatun ta ya kamata ace iyayenta sun mori ilimin ta amma sai dai shi baya son ace matarsa kullum sai ta fita gurin aiki, baya son abar tarbiyyar yayansa a hannun yan aikin gidadan haka sai ya mayar mata da matsayin ta zuwa secretary dinsa sannan yayi mata office dinta anan cikin gidan su inda anan ne suke ajjiyar duk wasu takardu da duk wasu bayanai da suka shafi business dinsa, ta ce mai kula da komai. Sai ta karba saboda tana ganin aikin zata yi ai ba wai bada shawara kadai ba, kuma tasan idan ma bata karba ba dole zai dauki wani ko wata a wannan matsayin.
Kiri kiri Hassan ya hana ake kai su Aminu gidan Ruqayyah, yace "I don't want them getting confused su kasa gane wacece mommy din a cikin ku. In sun girma sun fahimta da kansu zasu je but not now" a dole Sumayya ta amince da hakan ba dan zuciyarta tana so ba sai dan bata taba yi masa musu, ko abu taga yayi va dai dai ba bata musa masa directly sai dai indirectly ta kawo masa shawarar da zata rushe waccan maganar ba tare da ya fahimci abinda tayi ba.
Wannan kenan...............
Bara mu leka Kano. Shekaru biyar bayan mai martaba Sarkin Kano tare da yayansa sunje sun binne konanniyar gawar mace da ciki, wadda suka yi tunanin ta yarsu kuma yaruwarsu gimbiya Fatima ce. Experience din da har yanzu yake fresh a zuciyoyin al'ummar gidan musamman mahaifanta.
Ana tsakiya da hidimomin yau da kullum kamar yadda aka saba, sai ga baki sunzo a airport taxi, tun daga bakin gate aka tsayar dasu ana tuhumar su da su fadi daga inda suke kuma wa suke nema. Hakan ya faru ne saboda lura da akayi da cewa ba hausawa bane ba, duk da cewa ba za'a iya fadin direct wanne addini suke bi ba.
Na mijin da yake gaba tare da driver ne yayi Magana
"Sunana Adam, ina son ganin maimartaba sarki"
Kallon da dogarin ya watsa masa ne yasa yayi saurin chanja maganar sa "ko kuma wani a cikin manyan gidan wanda yake kusa"
Dogarin ya kuma bata rai, gashi dai hausa yake yi amma yafi kama da inyamuri. "Me zaka yi musu in ka gansu?" Adam ya dauke kai, dama yasan haka zata kasance, shi yasa ya nemi da su fara aiko da sakon zuwansu kafin suzo dan shi baya ciki da wulakanci, zai iya fita yanzu ya wanke dogarin nan da mari. Ya hadiye bacin ransa, wai me yasa kananan ma'aikata suke da wulakanta mutane ne bayan su kuma manyan nasu ba haka suke ba.
Cikin bacin ra yace "kwadon su zanyi in cinye. Ina ruwanka da abinda zanyi musu, ji nake kai aikinka shine isar da sako kuma na baka sako ka tsaya kana bata min lokaci da tambayoyi marasa amfani" shima dogarin ya kufula "an bata maka lokacin, aikina ba isar da sako bane ba tunda ni ba masinja bane ba, aikina shine kula da lafiya da dukiyar mai martaba tare da iyalinsa, kai kuma kayi kama da marasa gaskiya shi yasa na tsare ka na hana ka shiga, kuma ko duk garin nan zasu taru wallahi ba zan barka ka shiga gidan nan ba"
Adam ya dube kofa ya fita "amma lallai zaka shirya yin azumi uku kenan na rantsuwar da kayi dan shiga gidan nan kamar nayi ne na gama ko kana so ko ba ka so, ko zaka bude kofa ko ba zaka bude ba ni dai sai na shiga, and I will be talking to the emir while you will be fasting saboda rantsuwar da kayi" dogari ya daga kafada yace "kai ka san me kace a karshe. In ma zagi na kayi to kai ma haka. Ni dai kofa ce ba zan bude ba sai dai ka fadi abinda zaka fada anan, in naji mai ma'ana ne in aika a fada a ciki, in marar ma'ana ne kuma in koma ciki in barka anan kayi ta maganganun ka kai kadai"
Adam yace "Ni ai da masu gidan nazo inyi magana, ma'ana mamallaka gidan ba masu saka ja da koren kaya suna tsayawa a kofar gida ba" dogari yace "in ma baki da fari ne mun saka din, gida ne dai ba zaka shiga ba"
A hankali aka sauke glass din tagar baya na motar, sannan kyakykyawar fuskar Fatima ta bayyana. Tana nan babu abinda ya ragu daga kyawunta sai ma fari data yi saboda chanjin weather, sai kuma rama da tayi sosai, ga wanda ya santa zai iya cewa ta kankance ta koma kamar sanda take secondary school, yanayin takuma yayi kama da yanayin marar lafiya. A tare da ita akwai wata mata wadda kana ganin ta kasan ita ta haifi Adam. Ta kare wa dogarin da suke cacar baki da Adam kallo, ta gane shi tsaf dan rayuwarta a gidan su bata daga cikin abubuwan data manta. For years, shine dogarin da yake gadin gate din farko na gidan, sannan tace "Auwal dogari" ya juyo da sauri jin an ambaci sunansa, suka hada ido sai ya makale a yadda yake, baki a bude yana kokarin mayar wa da Adam magana, tace "dan Allah ka bude mana kofa mu shiga" ya rufe bakin sannan ya mitstsika idonsa da sauri sannan ya sake kallonta, anya tsufa bai fara kama shi ba kuwa? Wannan kamar gimbiya Fatima fa. Gimbiya Fatima data mutu shekaru biyar da suka wuce.
A bangaren Hassan kuma bayan abinda ya faru tsakanin sa da Ruqayyah bai taba tsammanin zai samu farin ciki a rayuwar aure ba amma sai gashi ya samu more than abinda yayi tunani ma. Sumayya ta kawo haske sosai cikin rayuwarsa shi yasa ya makala mata suna "Noorie". A yanzu ne kuma ya gaskata maganar Baba, a yanxu ne kuma ya fahimci mistake dinsa na danganta wani category na mutane da munanan halayya.
Tabbas auren sa da Ruqayyah tamkar lesson ne ubangiji ya koya masa kuma ya dauki darasi sosai, sannan kuma aurensa da Sumayya shi kuma sakayya ce Allah yayi masa saboda yadda ya bude hannayensa duk biyun ya karbi kaddarorin rayuwarsa tare da gode Allah a bisa niimomin sa.
Gasu dai Sumayya da Ruqayyah tagwaye ne, uwa daya uba daya, ciki daya mahaifa daya, sun kuma sha nono daya a lokaci daya, sun rayu a guri daya, an yi musu tarbiyya iri daya sun kuma samu ilimi iri daya, hatta cup da plate din da suka ci abinci sanda suna tasowa iri daya ne gashi kuma kamannin su daya amma banbancin halayyar tamkar banbancin dake tsakanin annabi da kafiri ne. Kamar ace positive and negative sides of a battery ne.
Shine zai bada wannan shaidar sama da kowa tunda shine wanda yasan in and out of them, shi yayi zaman aure da duk su biyun a mabanbanta lokuta.
Shekarar farko ta bayan aurensu Allah ya azurta su da haihuwar da namiji wanda suka saka wa Abdullahi.
Tabbas, a farkon auren su har zuwa yanzu ma da suke shekara uku da yin aure sukan fuskanci financial problems, saboda Hassan yanzu ba ya aikin da zai ke samun albashi duk wata, sannan auren da yayi da kuma auren da yayi wa kanensa har biyu Khadijah da Nafisa ya dakatar da harkar gine ginen sa, estate din nan ta farko dai har yanzu ita ce, har yanzu bai samu ya kammala ta biyun ba, kuma gidajen yearly suke biyan sa rent ba monthly ba dan haka dan ma dai shi mai kulawa ne da lissafi a komai shi yasa har suke samun condition din da suke ciki a yanzu.
Akwai lokacin da har sai da ya siyar da motar sa yake hawa ta haya saboda rashin kuɗi, amma fa iyalinsa basu taba zamada yunwa ba. Sai Sumayya ta bashi shawarar kafin ya kammala wannan ginin ya yi shaguna a gaban estate din sai ya saka musu monthly rents yadda duk wata zai ke karbar wani abu, sannan itama kuma ta nemi ya amince mata ya nema mata aiki amma sai yaki yadda da maganar aikin duk da cewa ya ji dadin waccan shawarar data bashi ta shaguna, dan haka sai yace mata ya bata aiki a karkashin sa a matsayin personal adviser dinsa, zai ke bata salary duk wata, ita kuma taki yarda tunda already yana bata kudin da suke isarta yin duk bukatun ta.
Shi kuma sai yaji babu dadi, dan yasan yadda Baba yasha wahala akan karatun ta ya kamata ace iyayenta sun mori ilimin ta amma sai dai shi baya son ace matarsa kullum sai ta fita gurin aiki, baya son abar tarbiyyar yayansa a hannun yan aikin gidadan haka sai ya mayar mata da matsayin ta zuwa secretary dinsa sannan yayi mata office dinta anan cikin gidan su inda anan ne suke ajjiyar duk wasu takardu da duk wasu bayanai da suka shafi business dinsa, ta ce mai kula da komai. Sai ta karba saboda tana ganin aikin zata yi ai ba wai bada shawara kadai ba, kuma tasan idan ma bata karba ba dole zai dauki wani ko wata a wannan matsayin.
Kiri kiri Hassan ya hana ake kai su Aminu gidan Ruqayyah, yace "I don't want them getting confused su kasa gane wacece mommy din a cikin ku. In sun girma sun fahimta da kansu zasu je but not now" a dole Sumayya ta amince da hakan ba dan zuciyarta tana so ba sai dan bata taba yi masa musu, ko abu taga yayi va dai dai ba bata musa masa directly sai dai indirectly ta kawo masa shawarar da zata rushe waccan maganar ba tare da ya fahimci abinda tayi ba.
Wannan kenan...............
Bara mu leka Kano. Shekaru biyar bayan mai martaba Sarkin Kano tare da yayansa sunje sun binne konanniyar gawar mace da ciki, wadda suka yi tunanin ta yarsu kuma yaruwarsu gimbiya Fatima ce. Experience din da har yanzu yake fresh a zuciyoyin al'ummar gidan musamman mahaifanta.
Ana tsakiya da hidimomin yau da kullum kamar yadda aka saba, sai ga baki sunzo a airport taxi, tun daga bakin gate aka tsayar dasu ana tuhumar su da su fadi daga inda suke kuma wa suke nema. Hakan ya faru ne saboda lura da akayi da cewa ba hausawa bane ba, duk da cewa ba za'a iya fadin direct wanne addini suke bi ba.
Na mijin da yake gaba tare da driver ne yayi Magana
"Sunana Adam, ina son ganin maimartaba sarki"
Kallon da dogarin ya watsa masa ne yasa yayi saurin chanja maganar sa "ko kuma wani a cikin manyan gidan wanda yake kusa"
Dogarin ya kuma bata rai, gashi dai hausa yake yi amma yafi kama da inyamuri. "Me zaka yi musu in ka gansu?" Adam ya dauke kai, dama yasan haka zata kasance, shi yasa ya nemi da su fara aiko da sakon zuwansu kafin suzo dan shi baya ciki da wulakanci, zai iya fita yanzu ya wanke dogarin nan da mari. Ya hadiye bacin ransa, wai me yasa kananan ma'aikata suke da wulakanta mutane ne bayan su kuma manyan nasu ba haka suke ba.
Cikin bacin ra yace "kwadon su zanyi in cinye. Ina ruwanka da abinda zanyi musu, ji nake kai aikinka shine isar da sako kuma na baka sako ka tsaya kana bata min lokaci da tambayoyi marasa amfani" shima dogarin ya kufula "an bata maka lokacin, aikina ba isar da sako bane ba tunda ni ba masinja bane ba, aikina shine kula da lafiya da dukiyar mai martaba tare da iyalinsa, kai kuma kayi kama da marasa gaskiya shi yasa na tsare ka na hana ka shiga, kuma ko duk garin nan zasu taru wallahi ba zan barka ka shiga gidan nan ba"
Adam ya dube kofa ya fita "amma lallai zaka shirya yin azumi uku kenan na rantsuwar da kayi dan shiga gidan nan kamar nayi ne na gama ko kana so ko ba ka so, ko zaka bude kofa ko ba zaka bude ba ni dai sai na shiga, and I will be talking to the emir while you will be fasting saboda rantsuwar da kayi" dogari ya daga kafada yace "kai ka san me kace a karshe. In ma zagi na kayi to kai ma haka. Ni dai kofa ce ba zan bude ba sai dai ka fadi abinda zaka fada anan, in naji mai ma'ana ne in aika a fada a ciki, in marar ma'ana ne kuma in koma ciki in barka anan kayi ta maganganun ka kai kadai"
Adam yace "Ni ai da masu gidan nazo inyi magana, ma'ana mamallaka gidan ba masu saka ja da koren kaya suna tsayawa a kofar gida ba" dogari yace "in ma baki da fari ne mun saka din, gida ne dai ba zaka shiga ba"
A hankali aka sauke glass din tagar baya na motar, sannan kyakykyawar fuskar Fatima ta bayyana. Tana nan babu abinda ya ragu daga kyawunta sai ma fari data yi saboda chanjin weather, sai kuma rama da tayi sosai, ga wanda ya santa zai iya cewa ta kankance ta koma kamar sanda take secondary school, yanayin takuma yayi kama da yanayin marar lafiya. A tare da ita akwai wata mata wadda kana ganin ta kasan ita ta haifi Adam. Ta kare wa dogarin da suke cacar baki da Adam kallo, ta gane shi tsaf dan rayuwarta a gidan su bata daga cikin abubuwan data manta. For years, shine dogarin da yake gadin gate din farko na gidan, sannan tace "Auwal dogari" ya juyo da sauri jin an ambaci sunansa, suka hada ido sai ya makale a yadda yake, baki a bude yana kokarin mayar wa da Adam magana, tace "dan Allah ka bude mana kofa mu shiga" ya rufe bakin sannan ya mitstsika idonsa da sauri sannan ya sake kallonta, anya tsufa bai fara kama shi ba kuwa? Wannan kamar gimbiya Fatima fa. Gimbiya Fatima data mutu shekaru biyar da suka wuce.