Sashe 25
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hassan yayi ajjiyar zuciya yace "Baba ba zan so in ke ganin ka kana wahala ba, nafi so inke ganin ka kana hutawarka" Baba yace "amma zaka ji dadi in ka ganni ina neman halak dina ko? Hutu kuma ai da saura na tunda da karfi na ba wai shekaru na ne suka ja ba, in lokacin hutawar yayi zan huta ne".
Haka suka yi ta ja in ja, a karshe dai a dole Hassan ya buga offer ya bawa Baba ya sallame shi saboda wadanda suke kan layi suna jira. Amma a ransa ya kudurce abinda ya kamata yayi akan lamarin.
Baba yana zuwa gida da murnar sa ya fara bawa iyalinsa labari "alhamdulillah, aiki ya samu, aikin gadin nan dai da nake ta buri gashi nan Allah ya kawo shi" ya bude takardar yana nuna musu ita upside down. Inna ta karba tana dubawa duk da ba gane wa take yi ba fuskarta lullube da farin ciki. "Masha Allah baban biyu, Allahu ya sa albarka a ciki, Allah yasa ka fara a Sa'a. Amma na dauka ba yanzu za'a baku ba sai an gama tantancewa" ya zauna yana cewa "haka ya kamata, amma yaron nan Hassan kinsan shine mai abin, a take ya buga min takarda a matsayin mai gadi ya bani".
Ruqayyah data fito daga toilet da buta a hannunta ta saki butar "mai gadi?" Ta fada, fuskarta tana nuna bacin ranta "wanne irin maigadi kuma? Yanzu Hassan din ne da kansa ya baka aikin maigadi a kamfanin sa? Wannan ai cin fuska ne"
Inna Ade tace "haba Ruqayyah, in ba'a gode masa ba ai kuwa ba za'a zage shi ba. Aikin gadin bashi baban naku yake nema ba? Ba dan shi ba kuma aikin gadin ma zai iya rasawa ya koma ya cigaba da leburanci da dako" cikin bacin rai Ruqayyah tace "amma wannan lokacin ai ya wuce, wannan sabuwar rayuwa ce, a matsayin sa na wanda zai zama surikinsa ba kamata yayi ya bashi babban office a kamfaninsa ba?" Baba ya fara fada "bana son diban albarka Hassana, da wanne takardun zai bani aikin office din? Me zanyi a office din? Shi cewa yayi ma in hakura da aikin ya bani jari inyi sana'a nace a'a, saboda ni bana son dogara da wani. In ba zaki yi murna da abinda Allah ya bamu ba ki wuce ki bani guri".
Bata kuma cewa komai ba ta wuce daki tana kunan zuci. Tabbas sai ta takawa Hassan burki, in dai yana sonta sai ya chanja wannan aikin, wannan ai ita zai zubarwa da kima a idon yan'uwansa da sauran jama'ar sa, shikenan kuma sai ace babanta shine mai gadin kamfanin mijinta? Ina! Ai sam ba zata sabu ba.
Da daddare dan halak din yazo zance.
Yaune zuwansa zance officially na farko. Yayi mata kwalliya sosai ya kuma gama shiryo kalaman da zai yi mata. Yayi packing sannan ya aika kiranta. Ita ma kuma a nata bangaren ta saka ran zai zo kuma ta shirya nata kalaman. Dan haka ana cewa ana sallama da ita ta saka hijab ta fesa daya daga cikin turaren da suke cikin kayan Hussain. A bakin kofar gidan ta tsaya ta gyara expression din fuskarta zuwa irin wanda tasan yana so, na yarinya mai kunya da nutsuwa
A jikin mota ta ganshi a tsaye ya rungume hannunsa. Farin yadi ne a jikinsa mai taushi wanda ya karbi kafar jikinsa sosai ya kuma fito da kyawun gyararriyar sumar kansa wadda ta sha gyara kuma take a bude. Bakin takalmi, bakin agogo da bakin tabarau, sai kuma kyakkyawan murmushi a fuskarsa. Zuciyarsa kuma cike da soyayyar hassanar sa.
Tayi masa murmushi itama. Sannan ta tako sannu a hankali tazo inda yake ta dan durkusa kadan ta gaishe shi. Ya amsa yana kara fadada murmushin sa. "Barka da fitowa uwar yayan Hassan" ta rufe fuska da hannunta. Yayi dariya yana karewa siraran dogayen yatsun hannunta kallo ya gyara tsayuwarsa yace "kinyi kyau sosai. Sai dai matsalar daya ce" ta bude fuskarta amma idanuwanta a kasa tace "wacce matsala kenan fa?" yace "wannan kunyar nake rokon alfarmar a rage ta ko yaya ne a bani dama inga cikin idanuwanki. Kullum su nake gani cikin baccina amma kuma a zahiri an hana mini ganin su" ta fara kokarin sake rufe fuskar ya hade hannayensa a guri daya yace "dan Allah, a tausayawa marayan Allah".
Tace "maraya?" Ya cire glass din idonsa Yace "eh. Baki sani bako?" Tace "Allah yaji kansa" yace "Allah yaji kansu zaki ce. Duk su biyun babu" tace "ohhh, ya Salam, na dauka ai....." Yace "Aunty? Ba ita ta haife mu ba, amma uwa ce a gare mu, haihuwar mu ne kawai baya yi ba".
Ko cikin abokan sa ba kowa ne yasan cewa ba Aunty ce ta haife su ba amma wannan ai Hassana ce, wannan aurenta zaiyi kuma aure akan gaskiya ake gina shi.
Tayi masa gaisuwa sai ya bata brief labarin asalinsu da kuma cikakkiyar dangantakar su da Aunty, ya kuma lissafa mata sunayen kannensa mata sannan ya gaya mata irin soyayyar da yake wa yan'uwansa.
Itama kuma sai ga bashi labarin nata asalin da sunayen nata family members din da stage din karatun kowanne. A lokacin ne ta ga time din shigar da maganar Baba yayi. Tace "ammm akan maganar Baba" sai ta dago kai kamar yadda tayi plan cewa zata saka idonta cikin nasa ta gaya masa ya chanja wa baban ta aiki. Amma the moment da suka hada ido sai komai nata ya ruguje, wannan mutumin ba wannan mutumin bane daya same ta a toilet yace mata "help me Please" wannan wani mutumin ne daban. Wannan is so strong and so sure of himself. Wannan mutumin will not be controlled, not by her, not by anyone.
Ta sauke idonta kasa tana jin komai yana rushe mata, plan dinta duk ya ruguje, yace "uhum, ina jinki, me zaki ce min a game da Baba?"cikin sanyin murya tace "cewa zanyi dama an gode madallah da aikin da ka bashi" yace "noo. Babu godiya ai a tsakanin mu. Baba ai babanane, tunda nawa baban ya mutu kinga ai yanzu na samu Baba ko?"
Ta kuma cewa "an kawo mana sako kuma, mungode" ya dan bata fuska yace "sako kuma? Tace "eh" a ranta tana tunanin bashi din bane ba kenan, sai ta kara da cewa "Hussain yazo jiya, da dare kuma sai ya aiko mana da wayoyi ni da Sumayya da kuma kaya"
Hassan yayi dariya yana bayyana farin cikin sa yace "ya kyauta sosai. Ko gaya min bai yi ba. Hussain yana da kirki sosai yana kuma da kyauta sosai. Kinga ya rigani, ina ta lissafin siyan wayar amma bana so inyi laifi a gurin Baba tunda ban sani ba ko ba ya son kuyi waya yanzu"
Ta harare shi ta gefe yadda ba zai gani ba sannan tace "ai kuwa yayi fadan, sai da kyar ya bari" yace "to Alhamdulillah tunda ya bari ɗin, yanzu an kunna ta kenan a bani number in samu ta rage dare? Kinsan abinka da gwauro" tace "bamu bude bama, sai mun siyo sim card" yace "gobe zan aiko, da sassafe ma kuwa"
Sun dan jima suna hira, ita kanta Ruqayyah tasan taji dadin hirar Hassan yadda yake komai a nitse, sai kuma yace "naga alamar akwai sauro, gwara in barki ki koma gida kar ya cizar min ke ko?" Da haka suka yi sallama ya raka ta bakin kofa ta shiga sannan ya juyo.
A lokacin ne wata taxi ta shigo layin, mai taxin ya dan wuce motar Hassan kadan sannan yayi packing. Ya fito a dai dai lokacin da Hassan yake kokarin bude kofar motar sa. Ya mika masa hannu, sai da Hassan ya kare masa kallo ya ganshi dan karamin saurayi da ba zai wuce ashirin zuwa ashirin da biyar ba, ya mika masa nasa hannun suka gaisasai ya nuna gidan su Ruqayyah yace "dan Allah nan ne gidan su wasu twins masu kama daya?" Hassan ya gyara tsayuwarsa yana studying saurayin yace "eh nan ne ya akayi?" Saurayin yace "Okay dama gidan nake nema shikenan na gode" Hassan ya kuma cewa "me yasa kake neman gidan su?" Saurayin yace "ohhh, dama muna haduwa ne dasu yawanci a school dinsu, to kwana biyu ban gansu ba shine nazo in duba su kuma mu gaisa" Hassan yace "really? Da wa zaka gaisa a cikin su?" Saurayin yace "Ruqayyah nasan ba zata kula ni bama, so.....da Sumayya zamu gaisa" Hassan yayi murmushi ya nuna masa kofar gidan yace "bismillah" sannan ya shiga motarsa ya bar unguwar zuciyarsa fara kal. Hassanar sa mai kamun kai ce ita, Hassanar sa mutuniyar kirki ce.
Wannan littafi na siyarwa ne, in kina son siya ki nemi wannan number din 08067081020
Episode Fifteen : The New Driver
Adam ya bi motar da kallo har ta kule, shi dai bai ga alamar wannan mutumin daga wannan gidan ya fito ba dan bai ma yi kama da unguwar ba ballantana gidan. Waye shi? Kwalliyar da yayi da kamshin da yake yafi kama dana wanda yazo zance, amma zance gurin wa? Ya kalli nashi kayan jikin, basu mutu ba amma kuma ba zasu tsaya a jere dana wanda ya bar gurin ba.
Ya dan tsafa kansa yana kallon gidan, shi bai taba zuwa zance ba, sai kuma ya tambayi kansa in da gaske zancen yazo. Shi dai yasan yaran sun tsaya masa a rai, kamannin halittar su da bambancin halayyar su yana bashi mamaki kuma yana kara sawa yaji tsoron Allah a zuciyarsa. Wannan ya sa ya kasa cire su a ransa, sai ya mayar da makarantar su gurin zuwan sa kullum idan lokacin daukan dalibai yayi, a haka watarana ya gansu wata rana kuma sai dai yayi ta rarraba ido ba tare daya gansu ba, haka zai hakura ya koma gida.
Haka suka yi ta ja in ja, a karshe dai a dole Hassan ya buga offer ya bawa Baba ya sallame shi saboda wadanda suke kan layi suna jira. Amma a ransa ya kudurce abinda ya kamata yayi akan lamarin.
Baba yana zuwa gida da murnar sa ya fara bawa iyalinsa labari "alhamdulillah, aiki ya samu, aikin gadin nan dai da nake ta buri gashi nan Allah ya kawo shi" ya bude takardar yana nuna musu ita upside down. Inna ta karba tana dubawa duk da ba gane wa take yi ba fuskarta lullube da farin ciki. "Masha Allah baban biyu, Allahu ya sa albarka a ciki, Allah yasa ka fara a Sa'a. Amma na dauka ba yanzu za'a baku ba sai an gama tantancewa" ya zauna yana cewa "haka ya kamata, amma yaron nan Hassan kinsan shine mai abin, a take ya buga min takarda a matsayin mai gadi ya bani".
Ruqayyah data fito daga toilet da buta a hannunta ta saki butar "mai gadi?" Ta fada, fuskarta tana nuna bacin ranta "wanne irin maigadi kuma? Yanzu Hassan din ne da kansa ya baka aikin maigadi a kamfanin sa? Wannan ai cin fuska ne"
Inna Ade tace "haba Ruqayyah, in ba'a gode masa ba ai kuwa ba za'a zage shi ba. Aikin gadin bashi baban naku yake nema ba? Ba dan shi ba kuma aikin gadin ma zai iya rasawa ya koma ya cigaba da leburanci da dako" cikin bacin rai Ruqayyah tace "amma wannan lokacin ai ya wuce, wannan sabuwar rayuwa ce, a matsayin sa na wanda zai zama surikinsa ba kamata yayi ya bashi babban office a kamfaninsa ba?" Baba ya fara fada "bana son diban albarka Hassana, da wanne takardun zai bani aikin office din? Me zanyi a office din? Shi cewa yayi ma in hakura da aikin ya bani jari inyi sana'a nace a'a, saboda ni bana son dogara da wani. In ba zaki yi murna da abinda Allah ya bamu ba ki wuce ki bani guri".
Bata kuma cewa komai ba ta wuce daki tana kunan zuci. Tabbas sai ta takawa Hassan burki, in dai yana sonta sai ya chanja wannan aikin, wannan ai ita zai zubarwa da kima a idon yan'uwansa da sauran jama'ar sa, shikenan kuma sai ace babanta shine mai gadin kamfanin mijinta? Ina! Ai sam ba zata sabu ba.
Da daddare dan halak din yazo zance.
Yaune zuwansa zance officially na farko. Yayi mata kwalliya sosai ya kuma gama shiryo kalaman da zai yi mata. Yayi packing sannan ya aika kiranta. Ita ma kuma a nata bangaren ta saka ran zai zo kuma ta shirya nata kalaman. Dan haka ana cewa ana sallama da ita ta saka hijab ta fesa daya daga cikin turaren da suke cikin kayan Hussain. A bakin kofar gidan ta tsaya ta gyara expression din fuskarta zuwa irin wanda tasan yana so, na yarinya mai kunya da nutsuwa
A jikin mota ta ganshi a tsaye ya rungume hannunsa. Farin yadi ne a jikinsa mai taushi wanda ya karbi kafar jikinsa sosai ya kuma fito da kyawun gyararriyar sumar kansa wadda ta sha gyara kuma take a bude. Bakin takalmi, bakin agogo da bakin tabarau, sai kuma kyakkyawan murmushi a fuskarsa. Zuciyarsa kuma cike da soyayyar hassanar sa.
Tayi masa murmushi itama. Sannan ta tako sannu a hankali tazo inda yake ta dan durkusa kadan ta gaishe shi. Ya amsa yana kara fadada murmushin sa. "Barka da fitowa uwar yayan Hassan" ta rufe fuska da hannunta. Yayi dariya yana karewa siraran dogayen yatsun hannunta kallo ya gyara tsayuwarsa yace "kinyi kyau sosai. Sai dai matsalar daya ce" ta bude fuskarta amma idanuwanta a kasa tace "wacce matsala kenan fa?" yace "wannan kunyar nake rokon alfarmar a rage ta ko yaya ne a bani dama inga cikin idanuwanki. Kullum su nake gani cikin baccina amma kuma a zahiri an hana mini ganin su" ta fara kokarin sake rufe fuskar ya hade hannayensa a guri daya yace "dan Allah, a tausayawa marayan Allah".
Tace "maraya?" Ya cire glass din idonsa Yace "eh. Baki sani bako?" Tace "Allah yaji kansa" yace "Allah yaji kansu zaki ce. Duk su biyun babu" tace "ohhh, ya Salam, na dauka ai....." Yace "Aunty? Ba ita ta haife mu ba, amma uwa ce a gare mu, haihuwar mu ne kawai baya yi ba".
Ko cikin abokan sa ba kowa ne yasan cewa ba Aunty ce ta haife su ba amma wannan ai Hassana ce, wannan aurenta zaiyi kuma aure akan gaskiya ake gina shi.
Tayi masa gaisuwa sai ya bata brief labarin asalinsu da kuma cikakkiyar dangantakar su da Aunty, ya kuma lissafa mata sunayen kannensa mata sannan ya gaya mata irin soyayyar da yake wa yan'uwansa.
Itama kuma sai ga bashi labarin nata asalin da sunayen nata family members din da stage din karatun kowanne. A lokacin ne ta ga time din shigar da maganar Baba yayi. Tace "ammm akan maganar Baba" sai ta dago kai kamar yadda tayi plan cewa zata saka idonta cikin nasa ta gaya masa ya chanja wa baban ta aiki. Amma the moment da suka hada ido sai komai nata ya ruguje, wannan mutumin ba wannan mutumin bane daya same ta a toilet yace mata "help me Please" wannan wani mutumin ne daban. Wannan is so strong and so sure of himself. Wannan mutumin will not be controlled, not by her, not by anyone.
Ta sauke idonta kasa tana jin komai yana rushe mata, plan dinta duk ya ruguje, yace "uhum, ina jinki, me zaki ce min a game da Baba?"cikin sanyin murya tace "cewa zanyi dama an gode madallah da aikin da ka bashi" yace "noo. Babu godiya ai a tsakanin mu. Baba ai babanane, tunda nawa baban ya mutu kinga ai yanzu na samu Baba ko?"
Ta kuma cewa "an kawo mana sako kuma, mungode" ya dan bata fuska yace "sako kuma? Tace "eh" a ranta tana tunanin bashi din bane ba kenan, sai ta kara da cewa "Hussain yazo jiya, da dare kuma sai ya aiko mana da wayoyi ni da Sumayya da kuma kaya"
Hassan yayi dariya yana bayyana farin cikin sa yace "ya kyauta sosai. Ko gaya min bai yi ba. Hussain yana da kirki sosai yana kuma da kyauta sosai. Kinga ya rigani, ina ta lissafin siyan wayar amma bana so inyi laifi a gurin Baba tunda ban sani ba ko ba ya son kuyi waya yanzu"
Ta harare shi ta gefe yadda ba zai gani ba sannan tace "ai kuwa yayi fadan, sai da kyar ya bari" yace "to Alhamdulillah tunda ya bari ɗin, yanzu an kunna ta kenan a bani number in samu ta rage dare? Kinsan abinka da gwauro" tace "bamu bude bama, sai mun siyo sim card" yace "gobe zan aiko, da sassafe ma kuwa"
Sun dan jima suna hira, ita kanta Ruqayyah tasan taji dadin hirar Hassan yadda yake komai a nitse, sai kuma yace "naga alamar akwai sauro, gwara in barki ki koma gida kar ya cizar min ke ko?" Da haka suka yi sallama ya raka ta bakin kofa ta shiga sannan ya juyo.
A lokacin ne wata taxi ta shigo layin, mai taxin ya dan wuce motar Hassan kadan sannan yayi packing. Ya fito a dai dai lokacin da Hassan yake kokarin bude kofar motar sa. Ya mika masa hannu, sai da Hassan ya kare masa kallo ya ganshi dan karamin saurayi da ba zai wuce ashirin zuwa ashirin da biyar ba, ya mika masa nasa hannun suka gaisasai ya nuna gidan su Ruqayyah yace "dan Allah nan ne gidan su wasu twins masu kama daya?" Hassan ya gyara tsayuwarsa yana studying saurayin yace "eh nan ne ya akayi?" Saurayin yace "Okay dama gidan nake nema shikenan na gode" Hassan ya kuma cewa "me yasa kake neman gidan su?" Saurayin yace "ohhh, dama muna haduwa ne dasu yawanci a school dinsu, to kwana biyu ban gansu ba shine nazo in duba su kuma mu gaisa" Hassan yace "really? Da wa zaka gaisa a cikin su?" Saurayin yace "Ruqayyah nasan ba zata kula ni bama, so.....da Sumayya zamu gaisa" Hassan yayi murmushi ya nuna masa kofar gidan yace "bismillah" sannan ya shiga motarsa ya bar unguwar zuciyarsa fara kal. Hassanar sa mai kamun kai ce ita, Hassanar sa mutuniyar kirki ce.
Wannan littafi na siyarwa ne, in kina son siya ki nemi wannan number din 08067081020
Episode Fifteen : The New Driver
Adam ya bi motar da kallo har ta kule, shi dai bai ga alamar wannan mutumin daga wannan gidan ya fito ba dan bai ma yi kama da unguwar ba ballantana gidan. Waye shi? Kwalliyar da yayi da kamshin da yake yafi kama dana wanda yazo zance, amma zance gurin wa? Ya kalli nashi kayan jikin, basu mutu ba amma kuma ba zasu tsaya a jere dana wanda ya bar gurin ba.
Ya dan tsafa kansa yana kallon gidan, shi bai taba zuwa zance ba, sai kuma ya tambayi kansa in da gaske zancen yazo. Shi dai yasan yaran sun tsaya masa a rai, kamannin halittar su da bambancin halayyar su yana bashi mamaki kuma yana kara sawa yaji tsoron Allah a zuciyarsa. Wannan ya sa ya kasa cire su a ransa, sai ya mayar da makarantar su gurin zuwan sa kullum idan lokacin daukan dalibai yayi, a haka watarana ya gansu wata rana kuma sai dai yayi ta rarraba ido ba tare daya gansu ba, haka zai hakura ya koma gida.