← Book details Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 134

Sashe 23

Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sumayya tayi dariya tace "son kai yake yi fa da yace ta fini komai" Hussain yace "na yarda dake, ta dai fiki sunkuyar da kai. Kin fita fara'a kuma daga alama zaki fita son mutane" ya fada cikin sigar tsokana, Ruqayyah ta danyi murmushi tana wasa da bakin jihab dinta sannan tace "na gane niyyar ku, so kuke ku hade min kai dan kunga baya nan ballantana ya tare min" Hussain yace "ohhh ashe kina magana. Ni na dauka ai mu biyu zamuyi hirar mu ban da ke"

Yace "to Malama Hassana, nazo ne......." Ruqayyah ta katse shi "Ruqayyah" yace "what?" Tace "Ruqayyah shine sunan" yace "ohh, ni kuma Hassana ake ta gaya min a kunnuwa na" tace "wannan shi kadai yake fada ai. Special" yayi dariya sosai yana bayyana dimple dinsa, Sumayya ma ta taya shi dariyar tana cewa "Ruqayyah yaushe kika kile har haka?" Hussain yace "wallahi Hassan ya taro match. Kuma kamar kin fada a kunnuwan sa" ta dan rufe fuska alamun kunya "kar ka gaya masa dan Allah".

Yace "kinsan me? Naga alamar kamar zaku daidaita da Gimbiya ta, Fatima sunanta, ita ce wadda zan aura. Tunda taji labarin ki take addu'ar ku daidaita da Hassan sai a hada bikin mu nan da wata biyar" ya zaro wayarsa yana bude lock din yace "ki saka min number dinki sai in bata ta kira ki ku gaisa" ta karbi wayar tana kallon hoton da yake kan screen din. Hoton sa ne tare da wata kyakkyawar yarinya wadda kallo daya tayi mata ta san ta fita komai, taji wani abu ya tsaya mata a wuyanta yana so ya kawo hawaye cikin idonta

Ta yi sauri ta mika masa wayarsa tace "bani da waya ai ni" Sumayya tace "kasan yanzu ne muka gama secondary school, Baba kuma dama yace sai mun gama zai siya mana waya" ya dan bata rai yana tunani yace "ku ka gama ko zaku gama? ai ba'a gama exams ba an dai yi neco saura waec. Ba zakuyi waec din ba?" Suka yi shiru duk su biyun, sai ya fahimci bashi da amsa dan haka yayi saurin chanja topic din da cewa "amma dai zaku cigaba da karatu ko?" A tare suka ce "eh" yace "good, Allah ya taimaka".

A lokacin ne yaro yazo ya kawo masa lemo da ruwa a jere akan karamin faranti tare da kofi akai. Sumayya ta karba sai ta bude motar ta ajiye masa sannan ta rufe. Yace "Nagode sosai. Dama kishirwa nake ji. Bara inzo in tafi kar in gajiyar daku da magana, ni bana gajiya da magana. Sai dai kuma gashi ban kawo muku komai ba" da sauri Ruqayyah tace "lah, babu komai, ai zuwan shine mafi muhimmanci akan wani abu" Sumayya ta kalle ta da mamaki sai kuma tayi saurin gyara fuskarta tace "haka ne" yace "a'a ba haka bane ba, ita kyauta ai abu ne mai kyau saboda tana kara soyayya a zukatan mutane, ko mai kankantar abu in aka baka shi kyauta sai kaji wanda ya bakan ya kara samun daraja a gurinka. Nima kunga yanzu ruwan da kuka bani ai naji dadi har cikin raina. Koda mutum ya fika komai na duniya in kuka hadu samu wani abu ka bashi, zaka kara daraja a gurinsa"

Ya cigaba "wannan yasa duk wanda na hadu dashi ina kokari inga na bashi wani abu da zai ke tunawa dani kuma yaji yana son mu sake haduwa. Ku ma kuma ba zaku zama exceptional ba. Ban taho da leda ba amma na san a jikina ba za'a rasa wani abu ba, ko cash ne" sai ya fara laluben jikin sa, yayi tsaki "these days sai mutum ya duba jikinsa yaji wai bashi da kudi".

Ruqayyah ta sake cewa "ba wani abu fa, ka barshi kawai".

Sai ya bude motar ya bude aljihun mota, sai gashi ya dauko rafar farare bugun Abuja, ya fito ya miko wa Sumayya, ga wannan kwa sayi jambaki" Ruqayyah tayi saurin rike hannun Sumayya duk kuwa da cewa sumayyan ba wai miko hannun tayi ba tace "uhm uhm, ba zamu karba ba gaskiya." Da mamaki yace "saboda me?" Ta sunkuyar da kai still hannunta rike dana Sumayya Tace "kawai dai. Babu abinda zamuyi dashi. Mungode"

Yace "ban taba jin yammata sunce babu abinda zasuyi da kudi ba sai yau. Ni sisters dina kullum complain suke kudi yayi musu kadan, kullum suna cikin siyan kayan kwalliya, jaka takalmi, da sauransu" Ruqayyah tace "mu duk wannan basu dame mu ba"

Yayi ajjiyar zuciya sannan ya jefa kudin cikin mota, Ruqayyah taji tamkar zuciyarta ya ciro ya jefa a mota amma ta maze, yace "ban taba yin kyauta an dawo min da ita ba sai yau. Amma babu komai, nasan ta inda zan bullo muku" duk suka yi murmushi. Yayi musu sallama ya shiga mota suka matsa ya tafi.

Sumayya ta juyo gurin Ruqayyah "what? Kece kika mayar da wannan kuɗin da kanki?" Tayi ajjiyar zuciya "kar ki kara min bakin ciki akan wanda nake ji already. Ke fa kika yi min wa'azin in chanja hali, to halin nake chanja wa" ta wuce ciki a ranta tana mitar yadda Hussain zai dauki wannan uban kudin a motar Hassan yayi kyauta dashi, Allah kadai yasan irin barnar kudin da yake yi masa.

Hussain yana kallonsu ta mirror har suka shiga gida sannan ya mayar da hankalinsa fully kan tukinsa, ya girgiza kansa, shi har yanzu bai ji tayi masa ba duk kuwa da cewa bashi da wani dalili na feeling like that. He test them with money kuma sunci jarabawar amma still.......

Ya dauki wayarsa ya kira Hassana (kanwarsu) "zan turo miki kudi yanzu kije ki fitar ki danyo min siyayya irin taku ta mata, kaya masu kyau, komai guda biyu iri daya. Zan kuma yi miki aike sai ki hada da kayan ki bawa drivern da yasan gidan su Hassana akai musu ita da yaruwata".

Bayan sun gama wayar ya kira wani dealer na waya da yake kawo masa wayoyi yace "ina son wayoyi guda biyu, latest. Ka aika min dasu gida".

Da daddare suna zaune a tsakar gida suna cin tuwon shinkafa miyar taushe har da nama, duk a cikin kudin da Hassan ya ajiye ranar nan ne. Gaba dayansu su hudu a tray daya Inna kuma da Baba suma suna ci tare, ga maganin sauro an kunna a gefe ga iska tana kada su. Baba yana basu labari "wato gobe akwai drama, an sake aiko mana fa mu koma wannan inta uku din nan. Gashi yaron nan Hassan naga alamar bai san dani a ciki ba sai dai kawai ya ganni" a lokacin suka ji tsayuwar mota sannan aka yi sallama. Sulaiman ne ya fita, an jima kadan sai gashi da bagco guda biyu da kuma karamar leda yana ta washe baki.

"Wato yammatan nan sai kun bani tukuici, wai wannan kayan sako ne inji Hussain yace ace muku "asha yammatanci lafiya".

Wannan littafin na siyarwa ne, in baki sani ba kika karanta a rashin sani to yanzu kin sani. In kina son cigaba ki nemi wannan number 08067081020.Episode Fourteen : The Gate man

Da sauri Ruqayyah ta mike, zuciyarta fara kal kamar takarda, it is about time daya kamata suma su fara shigowa gari. Wannan talauci haka har ina!

Ta tari Sulaiman a hanya tana karbar karamar ledar cikin zumudi tace "inji Hussain ko inji Hassan?" Ya dan dakata yana tunani sai kuma yace "kamar dai Hussain yace min, oga Hussain, haka yace. Amma bara in koma in sake tambayar sa" ya ajiye kayan zai juya Inna Ade tace "kai! Dawo nan. In Hassan in ma Hussain menene abin tambaya? Duk daya ne in daya ya bayar tamkar dayan ya bayar ne "

Ruqayyah ta bude ledar hannunta, jikinta har rawa yake yi, tayi arba sa kwalayen waya guda biyu "wayyo Allah na" ta fada tana rungume kwalin wayar a kirjinta "Sumayya wayoyi ne, handsets ne ta so ki gani!" Sumayya ta ajiye cokalin hannunta ta mike da sauri tana karbar guda daya a hannun Ruqayyah sannan suka saka ihun murna suna rungume juna. Samarin kuma suka bude jakankunan suka fara fito da kayan ciki. Kayan sawa ne da sauran kayan bukatu na mata. Zunnur yace "wannan duk sanda ya sake dawowa sai naje na gaishe shi nima na samu rabona".

Baba ya daga murya yace "lafiyar ku kuwa? Menene haka kuke yi? Menene wannan din?" Inna Ade ta karbe wayoyin hannunsu Ruqayyah sannan ta ja jakar zuwa gaban Baba, Ruqayyah ta biyo ta tamkar magnet, Inna tace "kaya ne baban biyu, Hussain ne dazu da bakanan ya zo yaga yaran nan shine yanzu ya aiko musu da kaya. Ta fada tana kokarin firfito masa da kayan, ya hade rai yace "kayan lefe ne?"

Ta yi dariya "kayan lefe kuma Baban biyu? Kayan lefen ne za'a aiko driver ya kawo?" Yace "to kayan menene?" Tace "kyauta ce kawai yayi musu" ya kuma hade rai "gaya masa sukayi suka ce basu da suttura? Ko kuma sutturar jikinsu ya raina" Inna ade tayi shiru, ya juya kan yammatan, "rokonsa kuka yi kuka ce ya siya muku?" Da sauri Ruqayyah, cikin rawar murya tace "wallahi Baba ba rokonsa muka yi ba, daya bamu kudi ma cewa muka yi bama so, shine kawai ya aiko mana" ya juya kan Inna Ade "to ba da ni za'a yi wannan abin ba. Yanzu me kike tunanin zai faru idan Hassan din yace ya fasa aurenta? Ya zamuyi mu biya su kayan su? Gidan nan zan saka a kasuwa?" A hankali Ruqayyah tace "ba zai ce ya fasa ba" ya juyo yana kallonta yace "to fitsararriya, ina magana kina mayar min ko? Ta yaya kika san ba zai ce ya fasa ba? Kin san abinda gobe zata zo dashi ne?"
Chapter 23 · 0% Book details