Sashe 42
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Su Hassan suna kai su Hussain gurin zamansu sai ya juyo ya dawo inda ya bar Ruqayyah, amma sai ya tarar bata nan sai Sumayya da bata ma san Ruqayyah ta tashi ba, ya zauna ya kira yawarta ta dauka ta gaya masa inda take, so take ya taso ya bar gurin bikin ya taho gurinta. Ai kuwa ko minti goma ba'a yi ba sai gashi a gabanta yana mata murmushi. "Shine kika gudu ko?" Tace "kida yayi kara da yawa, kaina kuma ciwo yake yi min" ya zauna a kusa da ita yana murmushi yace "wannan ciwon kai, ki gaya min yaya zanyi dashi ne" ta dafa kan tace "gajiya ce kawai, da ace ba'a taho dani ba kaga da yanzu ina can ina hutawa ta" ya gyada kai yana dada jin rashin dacewar tahowa da ita da Aunty ta dage sai anyi, sannan yace "kawo kan inyi miki addu'a" ta makale kafada yayi dariya "adduar ce ba kya so? Kin san dai adduar miji ga matarsa tana da saurin karbuwa inayi miki zaki ga kin warke" ita dai taki yadda, ta san wayon ya tabata ne babu wata addu'a da zai yi mata, wai ita zaiyi wa wayo bayan itama tana da wayon ta. Shi kuma yayi ta mata dariya, yasan abinda take gudu kuma abin yana kara masa sonta a zuciyarsa, yana kara nuna masa cewa she is pure, baya jin ta taba rike hannu da wani balagaggen namiji, dan haka tashi ce shi kadai babu wanda ya gutsira ya rage masa.
Ya saka hannu a aljihu ya zaro kudi, sababbin 200 notes bandir biyu ya ajiye a tsakiyar su, sannan yayi folding hannunsa yana kallonta yace "ga kudi nan, ban sani ba ko kina so ki shiga cikin gurin biki kiyi liƙi" ta kalli kudin sannan ya kalle shi, tana lura da yadda idanuwansa suke studying dinta tace "liƙi kuma? Dole ne sai anyi likin?" Ya girgiza kansa yace "ba dole bane ba, ra'ayi ne, ban sani ba ko kina da ra'ayin yi?" Ta dan yi murmushi tace "kai me yasa ba zaka je kayi musu likin ba" yace "ni bana yi" tace "saboda me?" Yace "saboda banga abinda hakan zai amfane ni dashi ba, a duniya da kuma a lahira. Banga amfanin in dauki kudin da zan iya yin wani abu dasu mai muhimmanci a duniya, ko kuma inyi sadakar su in samu ladan a lahira, sannan in ringa watsi dasu mutane suna rawa akai ba. I don't see the logic in that" ta harde hannayenta itama irin yadda yayi tace "kuma ni shine kake bani inje inyi?" Yayi murmushi bai ce komai ba, ta dauki kudin ta jujjuya su a hannun ta mentally tana calculating adadinsu, ba laifi, shima fa yana da kudin, ta mayar dasu ta ajiye tace "har na lissafo irin amfanin da za'a yi da wadannan kudin, ba zan zubar dasu a kasa ba" ya jima yana kallon ta, fuskarsa da sassanyan murmushi sannan yace "take it" tace "bazan yi likin ba fa" yace "na sani, ki saka su a jakarki ko zaku fita shopping dasu Nafisa, nasan babu abinda suke kauna irin shopping, maybe zaki ga abinda kike bukata kema" ta girgiza kai sai ya saka hannu ya dauki jakarta ya bude ya zuba mata kudin a ciki sannan ya rufe ya mika mata. Ta karba a hankali tace "Nagode" zuciyarta fal farin ciki, tabbas ta samo bakin zaren sa.
Hirar su suka kama yi, mostly labarin drama din da ake yi a gurin abokan su yake bata, yadda aka sako su a gaba ana ta tsokanar su shida Hussain akan aure, har zaunar dasu masu auren ciki sukayi wai suna koya musu yadda zasu yi wa matan su. Tun Ruqayyah tana dan basarwa har ta fara murmushi, daga baya sai gata tana kyalkyala dariya duk wani ciwon kanta ta bacin ranta ya tafi. Anan suka yi tasu dinner din, yayi waya aka aiko musu da abinci nan aka jera musu suka ci suka sha, yaji dadin zamansu a gurin sosai duk da yasan Hussain yana can ya kumbura in ya lura baya cikin gurin.
Suna komawa masaukin su Aunty ta kama hannun Ruqayyah "Ruqayyah ina kika je? Ina ta nemanki ni da nake so in ganki a kusa dani?" Ruqayyah ta danyi murmushi tace "uhmm dama........" Sumayya tace "tare da yaya Hassan suka fita, nima bansan inda suka je ba" Aunty ta saki hannun Ruqayyah tana cewa " wannan yaro, zai zo ya same ni ne, wato shine shi bai zauna ba ita ma kuma ya hana ta zama? Menene amfanin tahowa da ita da nayi kenan?" Tayi ta fadan ta ita kadai su dai su Ruqayyah suka fara shirin kwanciya bacci.
Karfe goma na safe aka daura auren auren Hussain Aminu Abdullahi da Gimbiya Fatima. Daurin auren daya samu halarta manya manyan kusoshin kasarnan dan Hussain duk wanda yake fada aji sai daya gayyace shi daurin aurensa, kuma yawancin su sunzo wadanda basu samu zuwa ba kuma sun turo representatives dinsu. An dauta auren ne a masallacin juma'a na kofar kudu, duk girman masallacin sai da mutane suka cika shi taf wadansu ma a haraba suka tsatstsaya, daga nan aka tafi reception, cikin gida kuma aka fara shirye shiryen daukan amarya zuwa kaduna inda acan kuma za'a daura auren Hassana da karfe biyu na rana. Dan haka ba tare da bata lokaci ba duk aka gama shiri, sannan aka dunguma gabaki daya har gaban mai martaba sarkin Kano, yau sai ga Sumayya da Ruqayyah a gaban sarki. Inda yayi wa Fatima doguwar nasiha akan aure, sannan kuma ya danka amanar ta a hannun yan uwan mijinta ya kuma yi musu addu'ar samun zaman lafiya da kuma zuriya mai albarka, daga nan sai aka bi aka rarrabawa duk matan da suke gurin littafin da maimartaba da kansa ya rubutawa Fatima na nasihohi akan zaman aure wanda yayi wa tittle da "Nasiha gareki yata Fatima" saboda ta ringa karantawa a duk lokacin da taji ta shiga duhu a game da zaman aurenta. Aka bawa duk matan gurin suma su ringa karantawa albarkacin Fatima.
Sai da aka daga Fatima za'a fita da ita sai ta saka kuka ta ruga gurin mahaifinta ta rungume shi, aka je da niyyar a dauko ta amma sai ya dakatar da mutanen ya mike da kansa ya kamata ya fita da ita ya saka ta a motar da zata kaita airport sannan ya shiga shima tare da kishiyar mamanta suka raka ta har gaban jirgi. Anan kowa ya kuma tabbatar da son da mai martaba sarki yake yiwa yarsa Fatima.
Ana sauka a Kaduna a ka cigaba da hidima, ana ƙoƙarin shiga da Fatima gidan ta kuma ana shirye shiryen daurin auren Hassana. Ruqayyah duk jinta take out of place, duk kuwa da cewa duk juyi sai Aunty ta kira sunan ta, sai ta lallaba ta ja Sumayya suka koma part dinta, Hassan ma ko duriyarsa bata ji ba bata sani ba mako ya dawo daga Kanon ko yana can, ta shiga daki kawai ta cire kwalliyar ta tayi wanka tayi kwanciyar ta, sama sama take jin guda da hayaniya daga gidan Hussain, ta san yanuwan amarya ne suke ta bidirin su a ciki, ta tashi ta jawo window ta rufe ta rufe curtain sannan ta kwanta, sai dai zafi take ji gashi dakin babu fanka ita kuma bata iya kunna ac ba, a haka tayi kwanciyar ta tana hada gumi.
Cikin ikon Allah sai ga yan gidan su nan sun zo, har da su Sulaiman da Zunnur da yan uwan inna Ade dana Baba, duk wadanda Inna ta bawa card din dinner sannan kuma ta turo su suje suyi wa Aunty Allah ya sanya alkhairi na daurin auren Hussain da Hassana. Yan uwan Hassan din da basu shigo ganin dakin amarya ba ranar da aka kawo ta suma duk suka shigo, wasu daga cikin yan uwan gimbiya suma suka leko, sai ya zamanto kamar wani bikin ake sakewa amma babu amarya, amaryar tana can ta kulle kanta a daki tana baccin wahala. Sai laasar ta tashi, shima gwoggo Habibah ce ta aiko Sumayya akan lallai ta tashe ta tayi wanka ta shirya ta fito. Dole ta tashi ta shirya din sannan ta nemi doguwar riga a cikin kayan lefenta ta saka tunda dinkunan nata sun kare sai wanda ta ware saboda dinner din yau. Ta kalli kanta a mudubi taga cewa tayi kyau sai dai idanunta da suka fada ciki suka yi baki. Ta danyi tsaki tana kara shafa hoda akan idon sannan ta fita.
Yadda taga gidan ya bata mamaki, ga abinciccika nan an kawo kala kala kowa yana serving kansa, ga kuma yan aiki nan an ajiye yadda daga an bata guri zasu gyara dan haka duk da yawan mutanen gidan fes fes yake yana kamshi. Ta gaggaishe da wadanda ya kamata ta gaisar su kuma wadanda ya kamata su gaishe ta suka gaishe ta.
Ana cikin haka sai ga jama'a nan suna ta shigowa, wai an kawo gimbiya gurinta za'a bata amanar ta a matsayin ta na yayar miji. A ranta tace "iyayi iya reto, wai matar da ta kusan haifa ta ita za'a bani amanar ta" aka zaunar da gimbiya a kasa, itama Ruqayyah aka zaunar da ita a kusa da gimbiyar sannan Aunty da sauran manyan iyaye suka zauna akan kujeru. Akayi ta jero musu nasiha akan su rike junansu amana. Aunty tace "to Ruqayyah da Fatima, ga amanar Hassan da Hussaini na na baku. Na san cewa kun sani marayu ne basu da uwa basu da uba dan haka basu da wanda yafi junan su kusanci da kansu. Dan Allah ku zamo sanadiyyar sake karfafa musu zumuncin su kar ku zamo sanadiyyar rushewar sa. Na san cewa Hassan da Hussain basa minti talatin a zaune tare ba tare da sunyi rigima ba amma hakan baya nufin cewa basa kaunar junan su dan ni ban taba ganin yan uwan da suke kaunar junan su ba kamar su. Dan Allah ku zamanto sanadiyyar karfafa wannan kauna a tsakanin su kar ku zama sanadiyyar haddasa gaba kiyayyar junan su a zukatan su". Daga nan sauran iyaye kowa ya kara da tasa. Duk sai da jikin kowa yayi sanyi a gurin harda Ruqayyah
Ya saka hannu a aljihu ya zaro kudi, sababbin 200 notes bandir biyu ya ajiye a tsakiyar su, sannan yayi folding hannunsa yana kallonta yace "ga kudi nan, ban sani ba ko kina so ki shiga cikin gurin biki kiyi liƙi" ta kalli kudin sannan ya kalle shi, tana lura da yadda idanuwansa suke studying dinta tace "liƙi kuma? Dole ne sai anyi likin?" Ya girgiza kansa yace "ba dole bane ba, ra'ayi ne, ban sani ba ko kina da ra'ayin yi?" Ta dan yi murmushi tace "kai me yasa ba zaka je kayi musu likin ba" yace "ni bana yi" tace "saboda me?" Yace "saboda banga abinda hakan zai amfane ni dashi ba, a duniya da kuma a lahira. Banga amfanin in dauki kudin da zan iya yin wani abu dasu mai muhimmanci a duniya, ko kuma inyi sadakar su in samu ladan a lahira, sannan in ringa watsi dasu mutane suna rawa akai ba. I don't see the logic in that" ta harde hannayenta itama irin yadda yayi tace "kuma ni shine kake bani inje inyi?" Yayi murmushi bai ce komai ba, ta dauki kudin ta jujjuya su a hannun ta mentally tana calculating adadinsu, ba laifi, shima fa yana da kudin, ta mayar dasu ta ajiye tace "har na lissafo irin amfanin da za'a yi da wadannan kudin, ba zan zubar dasu a kasa ba" ya jima yana kallon ta, fuskarsa da sassanyan murmushi sannan yace "take it" tace "bazan yi likin ba fa" yace "na sani, ki saka su a jakarki ko zaku fita shopping dasu Nafisa, nasan babu abinda suke kauna irin shopping, maybe zaki ga abinda kike bukata kema" ta girgiza kai sai ya saka hannu ya dauki jakarta ya bude ya zuba mata kudin a ciki sannan ya rufe ya mika mata. Ta karba a hankali tace "Nagode" zuciyarta fal farin ciki, tabbas ta samo bakin zaren sa.
Hirar su suka kama yi, mostly labarin drama din da ake yi a gurin abokan su yake bata, yadda aka sako su a gaba ana ta tsokanar su shida Hussain akan aure, har zaunar dasu masu auren ciki sukayi wai suna koya musu yadda zasu yi wa matan su. Tun Ruqayyah tana dan basarwa har ta fara murmushi, daga baya sai gata tana kyalkyala dariya duk wani ciwon kanta ta bacin ranta ya tafi. Anan suka yi tasu dinner din, yayi waya aka aiko musu da abinci nan aka jera musu suka ci suka sha, yaji dadin zamansu a gurin sosai duk da yasan Hussain yana can ya kumbura in ya lura baya cikin gurin.
Suna komawa masaukin su Aunty ta kama hannun Ruqayyah "Ruqayyah ina kika je? Ina ta nemanki ni da nake so in ganki a kusa dani?" Ruqayyah ta danyi murmushi tace "uhmm dama........" Sumayya tace "tare da yaya Hassan suka fita, nima bansan inda suka je ba" Aunty ta saki hannun Ruqayyah tana cewa " wannan yaro, zai zo ya same ni ne, wato shine shi bai zauna ba ita ma kuma ya hana ta zama? Menene amfanin tahowa da ita da nayi kenan?" Tayi ta fadan ta ita kadai su dai su Ruqayyah suka fara shirin kwanciya bacci.
Karfe goma na safe aka daura auren auren Hussain Aminu Abdullahi da Gimbiya Fatima. Daurin auren daya samu halarta manya manyan kusoshin kasarnan dan Hussain duk wanda yake fada aji sai daya gayyace shi daurin aurensa, kuma yawancin su sunzo wadanda basu samu zuwa ba kuma sun turo representatives dinsu. An dauta auren ne a masallacin juma'a na kofar kudu, duk girman masallacin sai da mutane suka cika shi taf wadansu ma a haraba suka tsatstsaya, daga nan aka tafi reception, cikin gida kuma aka fara shirye shiryen daukan amarya zuwa kaduna inda acan kuma za'a daura auren Hassana da karfe biyu na rana. Dan haka ba tare da bata lokaci ba duk aka gama shiri, sannan aka dunguma gabaki daya har gaban mai martaba sarkin Kano, yau sai ga Sumayya da Ruqayyah a gaban sarki. Inda yayi wa Fatima doguwar nasiha akan aure, sannan kuma ya danka amanar ta a hannun yan uwan mijinta ya kuma yi musu addu'ar samun zaman lafiya da kuma zuriya mai albarka, daga nan sai aka bi aka rarrabawa duk matan da suke gurin littafin da maimartaba da kansa ya rubutawa Fatima na nasihohi akan zaman aure wanda yayi wa tittle da "Nasiha gareki yata Fatima" saboda ta ringa karantawa a duk lokacin da taji ta shiga duhu a game da zaman aurenta. Aka bawa duk matan gurin suma su ringa karantawa albarkacin Fatima.
Sai da aka daga Fatima za'a fita da ita sai ta saka kuka ta ruga gurin mahaifinta ta rungume shi, aka je da niyyar a dauko ta amma sai ya dakatar da mutanen ya mike da kansa ya kamata ya fita da ita ya saka ta a motar da zata kaita airport sannan ya shiga shima tare da kishiyar mamanta suka raka ta har gaban jirgi. Anan kowa ya kuma tabbatar da son da mai martaba sarki yake yiwa yarsa Fatima.
Ana sauka a Kaduna a ka cigaba da hidima, ana ƙoƙarin shiga da Fatima gidan ta kuma ana shirye shiryen daurin auren Hassana. Ruqayyah duk jinta take out of place, duk kuwa da cewa duk juyi sai Aunty ta kira sunan ta, sai ta lallaba ta ja Sumayya suka koma part dinta, Hassan ma ko duriyarsa bata ji ba bata sani ba mako ya dawo daga Kanon ko yana can, ta shiga daki kawai ta cire kwalliyar ta tayi wanka tayi kwanciyar ta, sama sama take jin guda da hayaniya daga gidan Hussain, ta san yanuwan amarya ne suke ta bidirin su a ciki, ta tashi ta jawo window ta rufe ta rufe curtain sannan ta kwanta, sai dai zafi take ji gashi dakin babu fanka ita kuma bata iya kunna ac ba, a haka tayi kwanciyar ta tana hada gumi.
Cikin ikon Allah sai ga yan gidan su nan sun zo, har da su Sulaiman da Zunnur da yan uwan inna Ade dana Baba, duk wadanda Inna ta bawa card din dinner sannan kuma ta turo su suje suyi wa Aunty Allah ya sanya alkhairi na daurin auren Hussain da Hassana. Yan uwan Hassan din da basu shigo ganin dakin amarya ba ranar da aka kawo ta suma duk suka shigo, wasu daga cikin yan uwan gimbiya suma suka leko, sai ya zamanto kamar wani bikin ake sakewa amma babu amarya, amaryar tana can ta kulle kanta a daki tana baccin wahala. Sai laasar ta tashi, shima gwoggo Habibah ce ta aiko Sumayya akan lallai ta tashe ta tayi wanka ta shirya ta fito. Dole ta tashi ta shirya din sannan ta nemi doguwar riga a cikin kayan lefenta ta saka tunda dinkunan nata sun kare sai wanda ta ware saboda dinner din yau. Ta kalli kanta a mudubi taga cewa tayi kyau sai dai idanunta da suka fada ciki suka yi baki. Ta danyi tsaki tana kara shafa hoda akan idon sannan ta fita.
Yadda taga gidan ya bata mamaki, ga abinciccika nan an kawo kala kala kowa yana serving kansa, ga kuma yan aiki nan an ajiye yadda daga an bata guri zasu gyara dan haka duk da yawan mutanen gidan fes fes yake yana kamshi. Ta gaggaishe da wadanda ya kamata ta gaisar su kuma wadanda ya kamata su gaishe ta suka gaishe ta.
Ana cikin haka sai ga jama'a nan suna ta shigowa, wai an kawo gimbiya gurinta za'a bata amanar ta a matsayin ta na yayar miji. A ranta tace "iyayi iya reto, wai matar da ta kusan haifa ta ita za'a bani amanar ta" aka zaunar da gimbiya a kasa, itama Ruqayyah aka zaunar da ita a kusa da gimbiyar sannan Aunty da sauran manyan iyaye suka zauna akan kujeru. Akayi ta jero musu nasiha akan su rike junansu amana. Aunty tace "to Ruqayyah da Fatima, ga amanar Hassan da Hussaini na na baku. Na san cewa kun sani marayu ne basu da uwa basu da uba dan haka basu da wanda yafi junan su kusanci da kansu. Dan Allah ku zamo sanadiyyar sake karfafa musu zumuncin su kar ku zamo sanadiyyar rushewar sa. Na san cewa Hassan da Hussain basa minti talatin a zaune tare ba tare da sunyi rigima ba amma hakan baya nufin cewa basa kaunar junan su dan ni ban taba ganin yan uwan da suke kaunar junan su ba kamar su. Dan Allah ku zamanto sanadiyyar karfafa wannan kauna a tsakanin su kar ku zama sanadiyyar haddasa gaba kiyayyar junan su a zukatan su". Daga nan sauran iyaye kowa ya kara da tasa. Duk sai da jikin kowa yayi sanyi a gurin harda Ruqayyah