Sashe 19
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Duk suka yi shiru suna kallon sa, Hassan cikin sanyin jiki yace "saboda me Baba?" Baba yace "Saboda kamar yadda na fada ina sonka, duk su biyun yaya na ne basu da banbanci a guri na kuma suma duk ina son su, dan haka nake fatan idan sunyi aure auren nasu zai zauna har mutuwa, bana fatan ka auri yata kuma ka rabu da ita saboda wani hali nata da zaka ga baiyi maka ba, wannan shi yasa nake ganin alakar ku zata fi tafiya daidai da Sumayya, saboda a yadda na fahimta kamar halin ku yafi zama daya akan ita Ruqayyah"
Jabir yayi gyaran murya yace "Baba ita Ruqayyah tana da wani aibu ne? Wani hali da ya kamata a sani kafin a aure ta? Ko tana da wata cuta ce?" Baba ya girgiza kai, Ruqayyah yarsa ce kuma yana sonta, kuma son da yake mata ne ya saka shi wannan batu, aure ba abin wasa bane ba, ba kuma a gina shi a kan ƙarya da rufa rufa in dai har ana so ya dore. Yana son auren Ruqayyah da Hassan ya dore in dai ya kasance, shi yasa zai gaya masa in zai aure ta a haka shikenan in kuma ba zai iya ba sai ya karbi Sumayya in ita ma baya so shikenan.
Yace "Ruqayyah tana da zafin zuciya sosai, taurin zuciya da kafiya, ko mu iyayenta muna fama da ita a kan hakan. Bata da son mutane sosai saboda tana da fada, bata da tsoro sam. Kai kuma na fahimci mutum ne mai jama'a dan haka nake ganin kamar tafiyar ku ba zata zo daya ba"
Hassan ya shafa kansa yana sauke ajjiyar zuciya, shi baiga aibu a duk abinda Baba ya fada ba, dama ai ya riga yasan da rashin tsoron da taurin zuciyar tun sanda ta taimaka masa, rashin son mutane kuma shi zai iya cewa abin dadi yayi masa dan shi din ma ba mai son mutanen bane ba dan haka kullum yake fatan kar ya samu mace mai kwashe kwashen mutane yadda zasu ji dadin zamansu su kadai.
Yayi murmushi yana kallon Jabir shima da yake murmushi, sun dai fahimci cewa Baba mutum ne mai karanci da yawa yadda har zai fada musu abinda yake ganin aibu ne akan yar da ya haifa a cikinsa saboda ya kyautata dangantakar sa da su. Hassan yace "Baba ni ina ganin wannan ai duk ba wani abu bane ba, wannan ba abinda zai hana ayi aure bane ba, kuma ni itan dai Baba in za'a bani ita nake so Sumayya kuma sai ta zama kanwata" Jabir yace "wannan haka ne, kuma kusan duk halin daka lissafa irin na Hassan ne" ya fada cikin tsokana, "haka muke ta fama dashi, baya daukan raini ga kafiya, ina jin abin nasu a sunan ne" suka yi dariya su biyu banda Baba, shi gani yake yi kamar basu fahimce shi bane ba, amma zama da Ruqayyah su kansu da suka haife ta dauke kai kawai suke yi a lokuta da dama, suna ta yi mata addu'a kuma suna saka ran idan ta kara girma zata rage, sai dai baiyi tsammanin za'a zo neman aurenta haka da wuri ba. Yayi wa Hassan tayin auren Sumayya ne saboda yana ganin Hassan da Ruqayyah ba wai saba wa suka yi da junansu ba.
Yace "shikenan tunda kunji kuma kun amince, kunga nan gaba ba zaku zo min da korafi ba kuma. Zamuyi ta muku addu'a, Allah yayi mana jagora baki daya, Allah ya hada kanku. Na baka damar ka neme ta, idan kuma ka chanza shawarar a tsakiyar neman ka sani ba zan kullace ka ba sai dai ba kuma zan baka Sumayya ba a lokacin".
Hassan yace "insha Allahu hakan ma ba zata faru ba. Kowa a duniya ai dole yana da wani aibu da wadansu daga cikin mutane ba zasu so ba, ko ba Ruqayyah ba nasan bazan samu mace da take da komai ba dole sai an samu aibu".
Suka yi godiya, sannan Baba ya jero musu doguwar addu'a duk duka shafa suka tashi. Hassan yaso yaga Ruqayyah amma kuma yana jin nauyin Baba, haka ya shiga mota suka tafi yana kallon kofar gidan da fatan ko Allah zai saka yaga giftawar ta.
Ruqayyah tana shiga daki sai ta kwanta akan katifa ta jawo zani ta lulluba duk da ba wai sanyi take ji ba, so take tayi kuka amma kukan yaki zuwa, haka taje ji lokuta da dama idan aka bata mata rai sai dai tayi ta jin zafi a ranta ba zata iya kuka ba har sai ta samu tayi masifa tukunna zata ji ta huce. Idonta ya kada yayi jawur kamar garwashin wuta. Anya kuwa Baba ne ya haife ta? Anya kuwa uban da ya haifi ya zai iya yi mata abinda Baba yake shirin yi mata? Har zai ce zai bawa Hassan Sumayya? Zai ce da Hassan kar ya aure ta? Ita kuwa wanne irin laifi tayi wa Baba da yayi mata irin wannan tsana haka?
A lokacin Sumayya ta shigo dakin, farko bata lura da Ruqayyah ba sai daga baya ta ganta a takure a karshen katifa, ta taba jikinta da sauri "innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Ruqayyah baki da lafiya? Menene ya same ki?" Sai a lokacin Ruqayyah ta samu hawaye suka zubo mata, ai kuma ta fara rera kuka marar sauti kamar zata fito da zuciyarta, Sumayya kawai ya rungume ta ta barta tayi ta kukanta sai data gama sannan tace "Sumayya Baba baya sona ya tsane ni" da sauri Sumayya ta rufe mata baki tace "subhanallah, me kike fada haka? Baba yana son mu mana, yana son mu sosai da sosai" Ruqayyah tana girgiza kai tace "yana sonki dai amma banda ni. Ni ya tsane ni kamar bashi ya haife ni ba" sai ta bata labarin abinda taji.
Sumayya ta dora hannu aka fuskarta rubuce da tashin hankali sannan ta sauke tace "me ya kaiki Ruqayyah? Me ya kai ki zuwa kiji abinda zasu ce, ina ruwanki" Ruqayyah tace "magana ta fa zasu yi, zuciyata tana ta gaya min inje inji abinda zasu ce ashe akwai dalili, ashe zuciyata bata yarda da Baba bane ba"
Sumayya tace "wato ke kuma shikenan duk abinda zuciyarki ta gaya miki shi zakiyi? Ba zaki yi tunani da kwakwalwar ki ba sai kiyi aiki da zuciyarki? Ban shiga ran Baba ba Ruqayyah, bansan menene dalilin sa na fadar abinda ya fada ba amma nasan ba wai dan baya sonki bane ba sai don yana tsoron halinki, yana tsoron kar kije gidan kiyi ta musu halayyar ki azo aji kunya, kuma ni banga laifinsa ba" Ruqayyah ta fara ture ta tana kokarin mikewa tsaye tana kunkuni, Sumayya tace "ko me zaki ce sai dai kiyi ta cewa amma ni dai ba zan daina gaya miki gaskiya ba, kuma ina so ki sani, ko maza sun kare a duniya bazan auri Hassan ba dan haka kar ma ki saka wani abu a ranki, tunda Hassan ya nuna yana sonki to kuwa tabbas ya haramta a gareni. Amma in baki chanja hali ba zaki yi loosing dinsa, ko Baba bai hana shi ke ba shi da kansa zai gudu yace ya fasa"
Ruqayyah tayi hanyar kofa zata fita kuma sai ta tsaya, sai ta juyo tana kallon Sumayya tace "menene zai saka yace ya fasa?" Sumayya ta jawo ta ta dawo da ita zaune tace "halinki. Yadda na fahimce shi shi kamilar mace yake so mai kyawawan dabi'u, to in kina so ya aure ki sai kin zama mai wannan halin, abu mafi muhimmanci kuma sai kin cire son abinsa a zuciyarki, dan in dai ya fahimci kudinsa kike so bashi ba to kuwa zai gudu, ki nuna kudinsa bai dame ki ba, kinuna masa kina sonsa sosai, watakila ma kiga har kin fara son nasa da gaske"
Ruqayyah tace "waye yace miki bana sonsa yanzu" Sumayya tayi murmushi tace "ina fata. In ma kina sonshi to kinfi son dukiyarsa a kansa, ba Hassan kike so ba CEO na H and H kike so, ko ba haka bane ba?" Ruqayyah tace "shi din dai shine duk biyun, to menene abin damuwa a ciki?".
Sun jima suna hirar abin a tsakanin su, Sumayya tana ta bawa Ruqayyah shawarwari a ranta kuma tana fatan Hassan bai karbi tayin Baba ba saboda in ya karba dole zata yi wa Baba musu, dan ba zata iya auren Hassan din Ruqayyah ba. Ko da ace ita yace yana so zata iya barwa Ruqayyah shi dan a zauna lafiya. Ita farin cikin family dinta shine gaba da komai a gurinta.
A bangaren Ruqayyah kuwa hankalin ta ya kwanta sosai ta jin ikirarin Sumayya na cewa ba zata auri Hassan ba, kuma tasan indai Sumayya tace haka to Baba ba zai matsa mata ba. Sai kuma ta fara duba shawarwarin da Sumayya ta bata, ta kuma yarda lallai Hassan mace ta gari yake nema kuma indai ta nuna masa iri dabiun ta zai iya cewa ya fasa sai dai duk su biyun suyi asarar sa, ita kuma bata fatan wannan irin babbar asara ta same su. Ba dai mace ta gari yake so ba? To kuwa tabbas zai samu mace ta gari. Ita Ruqayyah ta kama shi a cikin faratan ta kuma ba zata taba releasing dinsa ba har sai burin ta ya cika, burinta na zama matar CEO of H and H.
Tagwayen sunyi ta jira suji Baba yayi musu magana akan abinda suka tattauna da Hassan amma bai ce musu komai ba, dan haka suka kasa tantancewa ko Hassan ya karbi tayin Baba ko kuma bai karba ba. Ruqayyah kuma tayi iyakacin kokarin ta na dannewa bata nuna wa Baba cewa taji tayin da yayi wa Hassan ba, sai dai a zuciyarta ta kuduri aniyar cewa zata tabbatar cewa watarana yayi nadama, wata rana sai yayi nadamar zaben Sumayya akan ta.
Jabir yayi gyaran murya yace "Baba ita Ruqayyah tana da wani aibu ne? Wani hali da ya kamata a sani kafin a aure ta? Ko tana da wata cuta ce?" Baba ya girgiza kai, Ruqayyah yarsa ce kuma yana sonta, kuma son da yake mata ne ya saka shi wannan batu, aure ba abin wasa bane ba, ba kuma a gina shi a kan ƙarya da rufa rufa in dai har ana so ya dore. Yana son auren Ruqayyah da Hassan ya dore in dai ya kasance, shi yasa zai gaya masa in zai aure ta a haka shikenan in kuma ba zai iya ba sai ya karbi Sumayya in ita ma baya so shikenan.
Yace "Ruqayyah tana da zafin zuciya sosai, taurin zuciya da kafiya, ko mu iyayenta muna fama da ita a kan hakan. Bata da son mutane sosai saboda tana da fada, bata da tsoro sam. Kai kuma na fahimci mutum ne mai jama'a dan haka nake ganin kamar tafiyar ku ba zata zo daya ba"
Hassan ya shafa kansa yana sauke ajjiyar zuciya, shi baiga aibu a duk abinda Baba ya fada ba, dama ai ya riga yasan da rashin tsoron da taurin zuciyar tun sanda ta taimaka masa, rashin son mutane kuma shi zai iya cewa abin dadi yayi masa dan shi din ma ba mai son mutanen bane ba dan haka kullum yake fatan kar ya samu mace mai kwashe kwashen mutane yadda zasu ji dadin zamansu su kadai.
Yayi murmushi yana kallon Jabir shima da yake murmushi, sun dai fahimci cewa Baba mutum ne mai karanci da yawa yadda har zai fada musu abinda yake ganin aibu ne akan yar da ya haifa a cikinsa saboda ya kyautata dangantakar sa da su. Hassan yace "Baba ni ina ganin wannan ai duk ba wani abu bane ba, wannan ba abinda zai hana ayi aure bane ba, kuma ni itan dai Baba in za'a bani ita nake so Sumayya kuma sai ta zama kanwata" Jabir yace "wannan haka ne, kuma kusan duk halin daka lissafa irin na Hassan ne" ya fada cikin tsokana, "haka muke ta fama dashi, baya daukan raini ga kafiya, ina jin abin nasu a sunan ne" suka yi dariya su biyu banda Baba, shi gani yake yi kamar basu fahimce shi bane ba, amma zama da Ruqayyah su kansu da suka haife ta dauke kai kawai suke yi a lokuta da dama, suna ta yi mata addu'a kuma suna saka ran idan ta kara girma zata rage, sai dai baiyi tsammanin za'a zo neman aurenta haka da wuri ba. Yayi wa Hassan tayin auren Sumayya ne saboda yana ganin Hassan da Ruqayyah ba wai saba wa suka yi da junansu ba.
Yace "shikenan tunda kunji kuma kun amince, kunga nan gaba ba zaku zo min da korafi ba kuma. Zamuyi ta muku addu'a, Allah yayi mana jagora baki daya, Allah ya hada kanku. Na baka damar ka neme ta, idan kuma ka chanza shawarar a tsakiyar neman ka sani ba zan kullace ka ba sai dai ba kuma zan baka Sumayya ba a lokacin".
Hassan yace "insha Allahu hakan ma ba zata faru ba. Kowa a duniya ai dole yana da wani aibu da wadansu daga cikin mutane ba zasu so ba, ko ba Ruqayyah ba nasan bazan samu mace da take da komai ba dole sai an samu aibu".
Suka yi godiya, sannan Baba ya jero musu doguwar addu'a duk duka shafa suka tashi. Hassan yaso yaga Ruqayyah amma kuma yana jin nauyin Baba, haka ya shiga mota suka tafi yana kallon kofar gidan da fatan ko Allah zai saka yaga giftawar ta.
Ruqayyah tana shiga daki sai ta kwanta akan katifa ta jawo zani ta lulluba duk da ba wai sanyi take ji ba, so take tayi kuka amma kukan yaki zuwa, haka taje ji lokuta da dama idan aka bata mata rai sai dai tayi ta jin zafi a ranta ba zata iya kuka ba har sai ta samu tayi masifa tukunna zata ji ta huce. Idonta ya kada yayi jawur kamar garwashin wuta. Anya kuwa Baba ne ya haife ta? Anya kuwa uban da ya haifi ya zai iya yi mata abinda Baba yake shirin yi mata? Har zai ce zai bawa Hassan Sumayya? Zai ce da Hassan kar ya aure ta? Ita kuwa wanne irin laifi tayi wa Baba da yayi mata irin wannan tsana haka?
A lokacin Sumayya ta shigo dakin, farko bata lura da Ruqayyah ba sai daga baya ta ganta a takure a karshen katifa, ta taba jikinta da sauri "innalillahi wa inna ilaihir rajiun, Ruqayyah baki da lafiya? Menene ya same ki?" Sai a lokacin Ruqayyah ta samu hawaye suka zubo mata, ai kuma ta fara rera kuka marar sauti kamar zata fito da zuciyarta, Sumayya kawai ya rungume ta ta barta tayi ta kukanta sai data gama sannan tace "Sumayya Baba baya sona ya tsane ni" da sauri Sumayya ta rufe mata baki tace "subhanallah, me kike fada haka? Baba yana son mu mana, yana son mu sosai da sosai" Ruqayyah tana girgiza kai tace "yana sonki dai amma banda ni. Ni ya tsane ni kamar bashi ya haife ni ba" sai ta bata labarin abinda taji.
Sumayya ta dora hannu aka fuskarta rubuce da tashin hankali sannan ta sauke tace "me ya kaiki Ruqayyah? Me ya kai ki zuwa kiji abinda zasu ce, ina ruwanki" Ruqayyah tace "magana ta fa zasu yi, zuciyata tana ta gaya min inje inji abinda zasu ce ashe akwai dalili, ashe zuciyata bata yarda da Baba bane ba"
Sumayya tace "wato ke kuma shikenan duk abinda zuciyarki ta gaya miki shi zakiyi? Ba zaki yi tunani da kwakwalwar ki ba sai kiyi aiki da zuciyarki? Ban shiga ran Baba ba Ruqayyah, bansan menene dalilin sa na fadar abinda ya fada ba amma nasan ba wai dan baya sonki bane ba sai don yana tsoron halinki, yana tsoron kar kije gidan kiyi ta musu halayyar ki azo aji kunya, kuma ni banga laifinsa ba" Ruqayyah ta fara ture ta tana kokarin mikewa tsaye tana kunkuni, Sumayya tace "ko me zaki ce sai dai kiyi ta cewa amma ni dai ba zan daina gaya miki gaskiya ba, kuma ina so ki sani, ko maza sun kare a duniya bazan auri Hassan ba dan haka kar ma ki saka wani abu a ranki, tunda Hassan ya nuna yana sonki to kuwa tabbas ya haramta a gareni. Amma in baki chanja hali ba zaki yi loosing dinsa, ko Baba bai hana shi ke ba shi da kansa zai gudu yace ya fasa"
Ruqayyah tayi hanyar kofa zata fita kuma sai ta tsaya, sai ta juyo tana kallon Sumayya tace "menene zai saka yace ya fasa?" Sumayya ta jawo ta ta dawo da ita zaune tace "halinki. Yadda na fahimce shi shi kamilar mace yake so mai kyawawan dabi'u, to in kina so ya aure ki sai kin zama mai wannan halin, abu mafi muhimmanci kuma sai kin cire son abinsa a zuciyarki, dan in dai ya fahimci kudinsa kike so bashi ba to kuwa zai gudu, ki nuna kudinsa bai dame ki ba, kinuna masa kina sonsa sosai, watakila ma kiga har kin fara son nasa da gaske"
Ruqayyah tace "waye yace miki bana sonsa yanzu" Sumayya tayi murmushi tace "ina fata. In ma kina sonshi to kinfi son dukiyarsa a kansa, ba Hassan kike so ba CEO na H and H kike so, ko ba haka bane ba?" Ruqayyah tace "shi din dai shine duk biyun, to menene abin damuwa a ciki?".
Sun jima suna hirar abin a tsakanin su, Sumayya tana ta bawa Ruqayyah shawarwari a ranta kuma tana fatan Hassan bai karbi tayin Baba ba saboda in ya karba dole zata yi wa Baba musu, dan ba zata iya auren Hassan din Ruqayyah ba. Ko da ace ita yace yana so zata iya barwa Ruqayyah shi dan a zauna lafiya. Ita farin cikin family dinta shine gaba da komai a gurinta.
A bangaren Ruqayyah kuwa hankalin ta ya kwanta sosai ta jin ikirarin Sumayya na cewa ba zata auri Hassan ba, kuma tasan indai Sumayya tace haka to Baba ba zai matsa mata ba. Sai kuma ta fara duba shawarwarin da Sumayya ta bata, ta kuma yarda lallai Hassan mace ta gari yake nema kuma indai ta nuna masa iri dabiun ta zai iya cewa ya fasa sai dai duk su biyun suyi asarar sa, ita kuma bata fatan wannan irin babbar asara ta same su. Ba dai mace ta gari yake so ba? To kuwa tabbas zai samu mace ta gari. Ita Ruqayyah ta kama shi a cikin faratan ta kuma ba zata taba releasing dinsa ba har sai burin ta ya cika, burinta na zama matar CEO of H and H.
Tagwayen sunyi ta jira suji Baba yayi musu magana akan abinda suka tattauna da Hassan amma bai ce musu komai ba, dan haka suka kasa tantancewa ko Hassan ya karbi tayin Baba ko kuma bai karba ba. Ruqayyah kuma tayi iyakacin kokarin ta na dannewa bata nuna wa Baba cewa taji tayin da yayi wa Hassan ba, sai dai a zuciyarta ta kuduri aniyar cewa zata tabbatar cewa watarana yayi nadama, wata rana sai yayi nadamar zaben Sumayya akan ta.