Sashe 110
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hassan ya cikata da sauri yana ja da baya yana girgiza kai, ta durkushe a gurin tana jan numfashi da kyar hawayen azaba yana zubowa daga idonta. Yaran suka tafi da gudu suka fada jikinta suna kuka ita kuma ta rungume su tana kallon Hassan. A hankali yace "Baba da Inna sunyi asarar haihuwa"
Sai ya juya ba tare da ya sake cewa komai ba yabar gidan, ya shiga mota ya dauki hanyar gidan su Ruqayyah a hanya yana iya kacin kokarin sa dan ganin bai concentrating akan maganganun ta ba har yaje kofa gidan yayi packing, yana fitowa Baba yana tsayawa a cikin Napep dinsa, amma ganin yanayin Hassan kadai ya saka hankalin sa ya tashi ya kira Sulaiman da sauri suka kama Hassan din da kyar yake iya taka kafarsa suka shigar dashi cikin gida suka ajiye shi a palo suna ta tambayar shi "lafiya Hassan? Wani abu ne ya faru? Wani ne ya kuma mutuwa? Ko Ruqayyah ce?" Hassan ya dago kai yana kallon Baba yace "Ruqayyah ce Baba, amma ba mutuwa tayi ba, mashi ta dauko ta soke zuciyata da shi" Baba ya dafe kansa, tabbas ranar da yake gudu kuma har ya fara tunanin ba zata zo ba tabbas tazo yau. Ruqayyah tayi aika aika, kuma daga yanayin Hassan yasan abinda tayi yafi abinda yake tunanin zata yi din. Ya wuce duk lissafin sa.
Ya dago kai yana kallon Hassan, yana kara ganin rashin dacewar Hassan da Ruqayyah sai yace "Hassan zan roke ka wata alfarma duk kuwa da bansan abinda Ruqayyah tayi maka ba" Hassan ya fara girgiza kai tun kafin yaji alfarmar dan ba zai iya yafewa Ruqayyah na, amma sai yaji baba yace "Sulaiman dauko min takarda da biro" Sulaiman yaje ya kawo sai Baba ya mika wa Hassan yace "dan Allah Hassan, dan Annabi, ina rokon ka ka saki Ruqayyah" Hassan ya kalli Baba sai yaga cewa har cikin zuciyarsa hakan yake nufi, ya dauki biron ya dora akan takardar, lallai yasan Baba ya gaya masa haka ne dan ya cire masa nauyin sa kar yaga mutumcin su ya kasa sakin Ruqayyah shi yasa ya zamanto shine ma ya roke shi, sai yayi rubutu kamar haka...
"Ni Hassan Aminu Abdullahi na saki matata Ruqayyah Yusuf saki uku"
Wannan littafin na siyarwa ne idan kika ganshi a wani guri na sata ne, in kina son ki sayi halaliyar ki ki yi min magana ta wannan number din through WhatsApp 08067081020
*Ina masu bukatar hadadu kuma ingantatun turarukan wuta da khumra masu dadin kamshi kuma a farashi me sauki to ga dama tazo muku Awwaba scent nada turarukan wuta humra burners kasko shisa coal dorot stool dilka body milk dadai sauransu masu bukatar na iya nemansu a whats app ko kuma kira ta wannan lambar 08034236800*
*bugu da kari duk wanda ya sayi humra ko turaren wuta a cikin wannan watan akwai kyautar dilka me kyau tafiyaya daga kasar chad wadda zata gyara jiki tay expoliating skin acikin minti 20 kawai ku garzayo dan 💕
kwasar garabasa*
*Adress kundila zoo road kano muna tura sako ko ina da iznin Allah**The Fifth Wave*
"Ni Hassan Aminu Abdullahi na saki matata Ruqayyah Yusuf saki uku"
Ya ajiye biron, amma sai ya kasa mikawa Baba takardar duk da yasan baban ba iya karatu yayi ba balle ya karanta abinda ya rubuta, sai dai a ransa da ace ana iya yin saki goma da kuwa tabbas shi zaiyi wa Ruqayyah. Dan babu abinda yake nadama a yanzu irin aurenta, babu abinda yake dana sanin yi irin hada zuri'a da ita, babu kuma abinda yake tausayi irin yayan da suke a tsakanin su.
Tunda ya fito daga gidan Hussain yake tambayar kansa dalilin da yasa haka ta faru dashi, ina carefulness dinsa ya tafi lokacin da ya zabi Ruqayyah a matsayin matar aure, ina smartness dinsa da dabarar sa da hangen nesan sa suka tafi, me yasa yayi failing akan abinda yafi komai muhimmanci a rayuwarsa? Ya ninke takardar a hankali ya ajiye a tsakiyar su shida Baba, ya kasa mikawa baban, sai Baba ya saka hannu ya dauka ya warware yana kallonta duk da cewa ba gane rubutun yake yi ba, dai kuma ya mikawa Sulaiman yace "karanta muji" sai Sulaiman ya karanta a fili, Hassan ya sunkuyar da kansa yana jin nauyin Baba amma ko kadan baya jin wani abu mai kama da regret na saki ukun da ya yiwa Ruqayyah.
Inna Ade ta fara kuka, Baba ya dago kai yace "ina rokon ka ka gaya min abinda tayi maka, saboda ina son insan muma iyayenta abinda ya kamata muyi mata" Hassan yana girgiza kansa yace "zuciyar ku ba zata iya dauka ba Baba, nima tawa zuciyar yanzu kuka take yi, Ruqayyah ta riga tayi mata mikin da ba zai taba goguwa ba" Baba yace "tunda har kana numfashi hakan yana nufin zuciyarka ta dauka, kai da ba dolen ta ba ballantana mu da muka haife ta, mu da ba zamu taba iya chanjata ba, ka gaya mana dan Allah dan musam ta yadda zamu taimaka mata".
Sai Hassan ya basu labari, labarin duk abinda Ruqayyah ta gaya msa da bakinta cewa tayi he told them everything har labarin abinda tayi wa Adam da kuma zargin da yake na cewa abinda tayi shine sanadiyyar batan Adam din. But duk wannan ba shine dalilin da ya saka ya sake ta ba, dalilin da ya saka ya sake ta shine abinda tace zata yi, sharrin da tayi ikirarin zata yi wa brother dinsa duk kuwa da cewa yana cikin kabarinsa a kwance, zata bata masa suna ta kuma bata nasabar dan ta data haifa da kanta duk dan saboda kudi. Yana tsoron cewa babu abinda ba zata iya yi ba saboda kudi.
Inna ta kasa juye labarin sai ta tashi ta shiga daki tana kuka, Sumayya da take tsaye a kofar dakinta tun shigowar su tana jin abinda suke cewa ta juya ta koma daki ta turo kofa, sai ta zauna akan gado blindly tana kallon bango sannan sai ta dauko wayarta ta nemo number din Ruqayyah ta saka ta a blacklist sannan ta goge ta daga cikin wayar ta, sai kuma ta ajiye wayar ta kwanta tana tunanin hanyarda zata bi ta tafi imo...
A palo Baba da Sulaiman suna zaune har Hassan ya gama basu labarin duk abinda Ruqayyah tayi. Da kyar yake magana amma bai yi shiru ba sai da ya kai aya sannan yace "kayi hakuri Baba, zaman da nayi ma da Ruqayyah a baya da ace zan iya dawo da hannun agogo baya da banyi shi ba har na hada zuri'a da ita ba, da ace zan mayar da rayuwata baya da nabi zabi irin na Hussain, na zabi mace kamar Fatima ba kamar Hassana ba, na zabi wayayyiya mai zurfin ilimin boko yar gidan masu kudi mai budadden ido irin Fatima ba irin Ruqayyah ba, wata kila da nayi haka da yanzu ban samu kaina a halin da nake ciki yanzu ba" Baba ya girgiza kansa yace "tabbas kayi kuskure a gurin zaben matar aure, amma ba wannan ne kuskuren ka ba. Arzikin mutum, zurfin ilimin bokon sa, yanayin al'ummar daya taso a cikin ta, shekarunsa ko kuma wayewar sa basu suke nuna halayyar sa ba. Ita halayyar mutum da ita ake haifar sa, su duk wadannan abubuwan dana lissafa suna taimakawa ne gurin kara wa ko rage karfin halayyar mutum. Ana samun nagari a cikin kowanne kaso na al'umma kamar yadda ake samun bata gari a cikin kowanne kaso da al'umma. Ana samun shaidanin mutum a cikin malamai kamar yadda ake iya samun salihin mutum a cikin shaidanu. Dan mun kasance malamai hakan baya nufin cewa yayan da zamu haifa lallai zasu kasance na gari ba, mu dai iyakacin mu mu bada ilimi mu bada tarbiyya amma ita shiriya ta Allah ce, Allah ne kadai zai iya shiryar da bawansa a lokacin da yaso. Kamar kuma yadda na gaya maka cewa yana yin guri da yanayin al'ummar da mutum ya samu kansa a ciki yana karawa ko rage halayyar mutum, wannan shine abinda ya faru da Hassana. Tun farko Hassana halinta ba mai kyau bane ba, ni da mahaifiyar ta mun sani kuma kamar yadda mahaifiyar ta take yawan fada ita Hassana kamar harabawa ce ubangiji yayi mana dn yaga yadda zamu yi da ita, kuma munyi iyakacin kokarin mu, a inda muka yi kuskure shine da muka biye mata muka hada auren ku kai da ita, komawar ta cikin ku da shiga irin rayuwar ku da bude idon da t kara yi da duniya shi ya kara lalata mata halayyar ta, shi yasa har ta zama abinda ta zama. Wata kila da mun barta a gabanmu, ko kuma mun samu wani mijin wanda ba irin ka ba, mai rufin asiri dai dai gwargwado mun aura masa ita da ba zata ga dukiya irin taku ba har ta saka a ranta sai ta mallake ta. Wannan shine abinda naso in nunawa mahaifiyar ta a lokacin da kake neman aurenta, amm ita kuma sai tayi tunanin idan bamu bawa Ruqayyah abinda take so ba shine zata kara lalacewa. Wannan shine kuskuren mu, wannan shine inda muka fadi jarabawar mu. Amma hakan ba wai yana nufin shikenan mun hakura ba, zamu cigaba da kokarin ganin mun gyara kuskuren mu, abinda zamuyi kuma a yanzu shine zamu barta da duniya, zamu barta ota da kanta ta gane cewa abinda take yi ba dai dai bane ba muyi fatan kuma komai ba jima komai ba daɗe zata yi nadama za kuma ta nemi yafiyar wadanda ta zalunta. Ta haka ne kadai zata samu rahamar ubangiji. Ni ba zance kayi wa Hassana komai ko ince kar kayi mata komai ba, in ka ga dama zaka iya hada ta yan sanda kace ga ikirarin da tayi na cewa zata yiwa dan uwanka kazafi akan dukiyar sa, in kafa dama zaka iya duba ya'yan da suke tsakanin ku ka barta da duniya kamar yadda muma zamu barta din. Duk zabin ka ne."
Sai ya juya ba tare da ya sake cewa komai ba yabar gidan, ya shiga mota ya dauki hanyar gidan su Ruqayyah a hanya yana iya kacin kokarin sa dan ganin bai concentrating akan maganganun ta ba har yaje kofa gidan yayi packing, yana fitowa Baba yana tsayawa a cikin Napep dinsa, amma ganin yanayin Hassan kadai ya saka hankalin sa ya tashi ya kira Sulaiman da sauri suka kama Hassan din da kyar yake iya taka kafarsa suka shigar dashi cikin gida suka ajiye shi a palo suna ta tambayar shi "lafiya Hassan? Wani abu ne ya faru? Wani ne ya kuma mutuwa? Ko Ruqayyah ce?" Hassan ya dago kai yana kallon Baba yace "Ruqayyah ce Baba, amma ba mutuwa tayi ba, mashi ta dauko ta soke zuciyata da shi" Baba ya dafe kansa, tabbas ranar da yake gudu kuma har ya fara tunanin ba zata zo ba tabbas tazo yau. Ruqayyah tayi aika aika, kuma daga yanayin Hassan yasan abinda tayi yafi abinda yake tunanin zata yi din. Ya wuce duk lissafin sa.
Ya dago kai yana kallon Hassan, yana kara ganin rashin dacewar Hassan da Ruqayyah sai yace "Hassan zan roke ka wata alfarma duk kuwa da bansan abinda Ruqayyah tayi maka ba" Hassan ya fara girgiza kai tun kafin yaji alfarmar dan ba zai iya yafewa Ruqayyah na, amma sai yaji baba yace "Sulaiman dauko min takarda da biro" Sulaiman yaje ya kawo sai Baba ya mika wa Hassan yace "dan Allah Hassan, dan Annabi, ina rokon ka ka saki Ruqayyah" Hassan ya kalli Baba sai yaga cewa har cikin zuciyarsa hakan yake nufi, ya dauki biron ya dora akan takardar, lallai yasan Baba ya gaya masa haka ne dan ya cire masa nauyin sa kar yaga mutumcin su ya kasa sakin Ruqayyah shi yasa ya zamanto shine ma ya roke shi, sai yayi rubutu kamar haka...
"Ni Hassan Aminu Abdullahi na saki matata Ruqayyah Yusuf saki uku"
Wannan littafin na siyarwa ne idan kika ganshi a wani guri na sata ne, in kina son ki sayi halaliyar ki ki yi min magana ta wannan number din through WhatsApp 08067081020
*Ina masu bukatar hadadu kuma ingantatun turarukan wuta da khumra masu dadin kamshi kuma a farashi me sauki to ga dama tazo muku Awwaba scent nada turarukan wuta humra burners kasko shisa coal dorot stool dilka body milk dadai sauransu masu bukatar na iya nemansu a whats app ko kuma kira ta wannan lambar 08034236800*
*bugu da kari duk wanda ya sayi humra ko turaren wuta a cikin wannan watan akwai kyautar dilka me kyau tafiyaya daga kasar chad wadda zata gyara jiki tay expoliating skin acikin minti 20 kawai ku garzayo dan 💕
kwasar garabasa*
*Adress kundila zoo road kano muna tura sako ko ina da iznin Allah**The Fifth Wave*
"Ni Hassan Aminu Abdullahi na saki matata Ruqayyah Yusuf saki uku"
Ya ajiye biron, amma sai ya kasa mikawa Baba takardar duk da yasan baban ba iya karatu yayi ba balle ya karanta abinda ya rubuta, sai dai a ransa da ace ana iya yin saki goma da kuwa tabbas shi zaiyi wa Ruqayyah. Dan babu abinda yake nadama a yanzu irin aurenta, babu abinda yake dana sanin yi irin hada zuri'a da ita, babu kuma abinda yake tausayi irin yayan da suke a tsakanin su.
Tunda ya fito daga gidan Hussain yake tambayar kansa dalilin da yasa haka ta faru dashi, ina carefulness dinsa ya tafi lokacin da ya zabi Ruqayyah a matsayin matar aure, ina smartness dinsa da dabarar sa da hangen nesan sa suka tafi, me yasa yayi failing akan abinda yafi komai muhimmanci a rayuwarsa? Ya ninke takardar a hankali ya ajiye a tsakiyar su shida Baba, ya kasa mikawa baban, sai Baba ya saka hannu ya dauka ya warware yana kallonta duk da cewa ba gane rubutun yake yi ba, dai kuma ya mikawa Sulaiman yace "karanta muji" sai Sulaiman ya karanta a fili, Hassan ya sunkuyar da kansa yana jin nauyin Baba amma ko kadan baya jin wani abu mai kama da regret na saki ukun da ya yiwa Ruqayyah.
Inna Ade ta fara kuka, Baba ya dago kai yace "ina rokon ka ka gaya min abinda tayi maka, saboda ina son insan muma iyayenta abinda ya kamata muyi mata" Hassan yana girgiza kansa yace "zuciyar ku ba zata iya dauka ba Baba, nima tawa zuciyar yanzu kuka take yi, Ruqayyah ta riga tayi mata mikin da ba zai taba goguwa ba" Baba yace "tunda har kana numfashi hakan yana nufin zuciyarka ta dauka, kai da ba dolen ta ba ballantana mu da muka haife ta, mu da ba zamu taba iya chanjata ba, ka gaya mana dan Allah dan musam ta yadda zamu taimaka mata".
Sai Hassan ya basu labari, labarin duk abinda Ruqayyah ta gaya msa da bakinta cewa tayi he told them everything har labarin abinda tayi wa Adam da kuma zargin da yake na cewa abinda tayi shine sanadiyyar batan Adam din. But duk wannan ba shine dalilin da ya saka ya sake ta ba, dalilin da ya saka ya sake ta shine abinda tace zata yi, sharrin da tayi ikirarin zata yi wa brother dinsa duk kuwa da cewa yana cikin kabarinsa a kwance, zata bata masa suna ta kuma bata nasabar dan ta data haifa da kanta duk dan saboda kudi. Yana tsoron cewa babu abinda ba zata iya yi ba saboda kudi.
Inna ta kasa juye labarin sai ta tashi ta shiga daki tana kuka, Sumayya da take tsaye a kofar dakinta tun shigowar su tana jin abinda suke cewa ta juya ta koma daki ta turo kofa, sai ta zauna akan gado blindly tana kallon bango sannan sai ta dauko wayarta ta nemo number din Ruqayyah ta saka ta a blacklist sannan ta goge ta daga cikin wayar ta, sai kuma ta ajiye wayar ta kwanta tana tunanin hanyarda zata bi ta tafi imo...
A palo Baba da Sulaiman suna zaune har Hassan ya gama basu labarin duk abinda Ruqayyah tayi. Da kyar yake magana amma bai yi shiru ba sai da ya kai aya sannan yace "kayi hakuri Baba, zaman da nayi ma da Ruqayyah a baya da ace zan iya dawo da hannun agogo baya da banyi shi ba har na hada zuri'a da ita ba, da ace zan mayar da rayuwata baya da nabi zabi irin na Hussain, na zabi mace kamar Fatima ba kamar Hassana ba, na zabi wayayyiya mai zurfin ilimin boko yar gidan masu kudi mai budadden ido irin Fatima ba irin Ruqayyah ba, wata kila da nayi haka da yanzu ban samu kaina a halin da nake ciki yanzu ba" Baba ya girgiza kansa yace "tabbas kayi kuskure a gurin zaben matar aure, amma ba wannan ne kuskuren ka ba. Arzikin mutum, zurfin ilimin bokon sa, yanayin al'ummar daya taso a cikin ta, shekarunsa ko kuma wayewar sa basu suke nuna halayyar sa ba. Ita halayyar mutum da ita ake haifar sa, su duk wadannan abubuwan dana lissafa suna taimakawa ne gurin kara wa ko rage karfin halayyar mutum. Ana samun nagari a cikin kowanne kaso na al'umma kamar yadda ake samun bata gari a cikin kowanne kaso da al'umma. Ana samun shaidanin mutum a cikin malamai kamar yadda ake iya samun salihin mutum a cikin shaidanu. Dan mun kasance malamai hakan baya nufin cewa yayan da zamu haifa lallai zasu kasance na gari ba, mu dai iyakacin mu mu bada ilimi mu bada tarbiyya amma ita shiriya ta Allah ce, Allah ne kadai zai iya shiryar da bawansa a lokacin da yaso. Kamar kuma yadda na gaya maka cewa yana yin guri da yanayin al'ummar da mutum ya samu kansa a ciki yana karawa ko rage halayyar mutum, wannan shine abinda ya faru da Hassana. Tun farko Hassana halinta ba mai kyau bane ba, ni da mahaifiyar ta mun sani kuma kamar yadda mahaifiyar ta take yawan fada ita Hassana kamar harabawa ce ubangiji yayi mana dn yaga yadda zamu yi da ita, kuma munyi iyakacin kokarin mu, a inda muka yi kuskure shine da muka biye mata muka hada auren ku kai da ita, komawar ta cikin ku da shiga irin rayuwar ku da bude idon da t kara yi da duniya shi ya kara lalata mata halayyar ta, shi yasa har ta zama abinda ta zama. Wata kila da mun barta a gabanmu, ko kuma mun samu wani mijin wanda ba irin ka ba, mai rufin asiri dai dai gwargwado mun aura masa ita da ba zata ga dukiya irin taku ba har ta saka a ranta sai ta mallake ta. Wannan shine abinda naso in nunawa mahaifiyar ta a lokacin da kake neman aurenta, amm ita kuma sai tayi tunanin idan bamu bawa Ruqayyah abinda take so ba shine zata kara lalacewa. Wannan shine kuskuren mu, wannan shine inda muka fadi jarabawar mu. Amma hakan ba wai yana nufin shikenan mun hakura ba, zamu cigaba da kokarin ganin mun gyara kuskuren mu, abinda zamuyi kuma a yanzu shine zamu barta da duniya, zamu barta ota da kanta ta gane cewa abinda take yi ba dai dai bane ba muyi fatan kuma komai ba jima komai ba daɗe zata yi nadama za kuma ta nemi yafiyar wadanda ta zalunta. Ta haka ne kadai zata samu rahamar ubangiji. Ni ba zance kayi wa Hassana komai ko ince kar kayi mata komai ba, in ka ga dama zaka iya hada ta yan sanda kace ga ikirarin da tayi na cewa zata yiwa dan uwanka kazafi akan dukiyar sa, in kafa dama zaka iya duba ya'yan da suke tsakanin ku ka barta da duniya kamar yadda muma zamu barta din. Duk zabin ka ne."