Sashe 69
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Bata ce komai ba still, yace "gidan arziki Ruqayyah gaya min me kike nufi da gidan arziki? Hussain? Da ace ni Hussain ne? Me kike nufi da haka?" Tsabar zafin da maganar tayi masa ya hana ya nuna bacin ransa sai ma karyewa da zuciyarsa tayi. So yake tayi magana, so yake ta gaya masa bata fada masa wadannan maganganun ba kawai imagination dinsa ne.
Ta bude idonta ta sauke su a kansa "kayi hakuri mijina ban fada da niyyar in bata maka rai ba, kawai dai ji nayi nawa ran ya baci kuma ban san na fada maka haka ba" ya sake ta, ta fada din kenan, bawai kunnensa ne bai ji masa dai dai ba wai imagination dinsa bane ba Hassana ce tace gidansa ba gidan arziki bane ba, da Hussain ne zaiyi abinda shi ba zaiyi ba.
Tana jin ya sake ta ta juya da sauri ta fita tare da rufe kofar, da ace da key a hannunta ma da rufe shi zata yi ta waje dan ita kan ta tsorata da fuskarsa da kuma rikon da yayi mata. Amma wannan bai hana ta shiga dakin ta ta dauko kudi ta fito gurin kawayenta suka cigaba da hidimar su ba. Sai da suka gama sannan ta fito da kudin ta basu tace inji Hassan yace suyi kudin mota. Minal tace "shi wannan mijin naki wallahi da kayan haushi yake, maimakon ma yace ga driver nan a waje a kai kowa gidansu sai ya wani bamu kudi?" Daya a cikin kawayen ta karbe kudin tana lissafawa tace "mu dai muna so, ke dan kin samu zaki shiga daga ciki shine har zaki yi yanga in an baki kudi?" Suka raba kayansu kowa ta saka a jakarta. Ruqayyah tabi jakankunan su da kallo tana hadiye daci a ranta, ta jima tana tara kudin nan tana son siyan wata sarka.
Da zasu tafi Minal ta jata kefe "to sai kin shigo dinner gobe" Ruqayyah tayi ajjiyar zuciya "dinner nan Minal ba lallai bane in shigo ta" Minal ta bude ido "amma kuwa da kin cika babbar marar m...dinner din bikin nawa zaki ki zuwa" Ruqayyah tace "ba cewa nayi ba zan zo ba, cewa nayi ba lallai bane inzo din, kin san ai komai sai Allah yayi ko? Ku tafi kawai, zamu yi waya zan baki labarin abinda yasa nace haka" Minal ta bata rai "ko ma menene ni ba uzuri bane ba a gurina, kuma in baki zo dinner ba wallahi nasan matsayina a gurin ki kuma na san kema a gurin da zan a jiye ki a zuciyata" Ruqayyah dai ta lallabata ta raka ta waje suka shiga motar da alhajin ta ya aiko ta dauke su.
Ta gefen idonta ta hango Adam yana fitowa daga part din Hussain yana tafiya hanyar shiga part din Aunty, a can yaje tare da sauran yaran Hussain a tsofaffin dakunan su Hassan. Ya saka hannunsa a aljihu yana taku dai dai jikinsa sanye da kaya masu kyau, in ka ganshi zaka iya tunanin kanin mai gidan ne dan yarintar sa ce kawai zata sa ba zaka ce shine mai gidan ba. Tayi tsaki, ta tsane shi har cikin zuciyarta, ya tsani guts dinsa, yadda yake tafiya da yadda yake magana da komai nasa. More importantly ta tsani alakar sa da only sister dinta. God knows tana son Sumayya har cikin ranta kuma zata yi iyakacin kokarin ta ta ga cewa alakar Sumayya da wannan tubabben bata cigaba ba, bata je inda su suke son taje dinba. She can't imagine having nephews and nieces masu Christian blood a jikin su, masu kama da kedarai. Ta kara tsaki tana juyawa cikin gidan ta, dole zata nemi hanyar raba wannan alakar duk da tasan ba zata samu goyon baya daga Sumayyan ba ko Baba ko Inna but duk da haka she will find a way, zata yi shawara da zuciyarta kuma tadan zata samu mafita kamar yadda kullum zuciyar tata take bata mafita a duk problems dinta. Yanzu ma already ta bata mafita akan problem dinta da Hassan.
A palo ta fara tsayawa tana bawa yaran ta directives na yadda zasu gyara gidan, sannan tayi musu sallama ta hau sama. Dakin ta ta shiga ta fara yin wanka ta shirya cikin kayan bacci masu daukan hankali ta dauko ajjiyoyin kayan matan ta ta sha na sha ta shafa na shafawa. Tunda suka yi aure bai taba resisting dinta ba kuma bata jin zai fara daga yau.
Tunda Ruqayyah ta juya ta fita Hassan ya zame ya zauna a bakin gado ya dafe kansa da hannayensa biyu. "What just happened? What happened to his perfect precious wife? Did she just said what she said ko kuma zuciyarsa ce take playing tricks on him? Ta tabbas there must be an explanation to her behavior ko dai yayi mata wani laifi ne mai girma da out of anger ta fada masa haka? Amma shi duk a tunaninsa bai tuno wani abu da yayi mata marar dadi ba.
Ya tuna a yanayin da ta gaya masa maganar, babu wani emotions irin kamar normal mutum yana magana ne directly from her heart, daga dukkan alamu itama bata san ta fada ba sai bayan data fada din. Zuciyarsa tana ta kokarin kawo masa wani excuse da zai kare ta amma kwakwalwar sa taki karbar excuse din, sai ma wadansu maganganu da suke fado masa a rai.
Farko maganar Baba "zan so ka janye auren Hassana ka auri Hussaina a madadin ta"
Hussain "in har zata iya yaudarar top criminals ta haka mudu rami su fada ciki why not you?"
Sumayya "kayi ta hakuri, kana addu'a kuma kana saka ido".
Ya mike yana jiyo karar kidan da suka kunna a kasa, Yusuf ya fara kuka, ya dauke shi yana rarrashinsa, Aminu ya saka kuka shima yana miko masa hannu, ya durkusa shima ya dauke shi yana zagaya wa dasu a hannunsa yana raba idonsa a tsakanin fuskokin su. Sai ya samu kansa da tambayar kansa
"Did he make the worse choice for the most important thing?"
"Did he chose a bad wife for himself and a bad mother for his children?"
Where was his carefulness?
Ya shiga da yaran toilet dinsa ya saka su a wash hand basin ya wanke musu jikin su da ruwan dimi, suna ta wasa suma jika shi, ya fito da su ya kashe acn dakin ya goge musu jiki sannan yaje dakinta ya samo musu kaya yazo ya saka musu, ya koma ya dauki madara ya hada musu ya basu, a take suka yi bacci ya kwantar dasu yana kallon su sannan shima ya kwanta a tsakiyar su tare da rufe idonsa, amma bacci shine abu na karshe a zuciyarsa.
"At least haka akeyi a gidan arziki, da Hussain ne da haka zaiyi va wai ya zauna yana complain akan abinda akayi shekara guda data wuce ba"
Ya girgiza kansa yana son ya cire maganar ta daga cikin kansa amma ya kasa. A haka yaji ta bude kofar dakin ta shigo ta tsaya tana kallon su
Ta dan jima a tsaye tana assessing din sa shi da yayansa, yaran bacci suke yi amma shi tana kallonsa ta san idonsa biyu rufe idon kawai yayi. Ta karasa tare da dauke Yusuf ta mayar dashi kusa da dan uwansa sannan ta zauna a inda ta dauke shin tana dora hannunta akan goshin Hassan. Ya bude ido yana kallon ta, tayi masa murmushi "dama nasan ba kayi bacci ba shine ka wani rufe ido ko?" Bai ce mata komai ba amma ta hango wani bakon al'amari a cikin idon nasa, tace "wai fushi kake yi dani mijina? Kayi hakuri mana dan Allah ai kasan dai babu wani wanda yake baya kuskure a rayuwa ko? Nayi kuskure, raina ne naji ya baci a lokacin ka yafe min kaji mijina?" Sai taga yayi dan murmushi, a take taji hankalin ta ya kwanta, dama ta san babu inda fushin nasa zai je in dai har ta bayar da hakuri musamman kuma ace da wannan shigar a jikinta tana kuma wannan kamshin ai magana ta riga ta wuce. Sai taji yace "ranki ne ya baci ko? Kinsan wani abu. A lokacin da ran mutum ya baci a lokacin ne yake fadar duk abinda yake cikin zuciyarsa, so chances are very high cewa abinda yake zuciyarki shi kika fada min" ya fada idanuwan sa cikin nata.
Ta fara jujjuya hannunta tana kokarin controlling anger dinta tace "don't be like that mana, haba mijina, ya kamata kayi min uzuri mana. Nima fa ina da zuciya a kirjina, kuma zuciyata tana son irin rayuwar su Hussain da matarsa yadda suke wadaka da dukiya suna zuwa duk ƙasar da suka ga dama a lokacin da suka yi niyya. What do you expect your wife to do? How do you expect me to feel bayan ka kawo ni ina zaune da kanin ka da yake da everything while you have nothing?"
Ya mike zaune yana kankance idonsa a kanta, "do you just said "nothing"? Do you mean I have nothing?" Ta juya idonta, yau me yake faruwa ne da ita? Me yasa bata da sa'ar magana ne? Daga dukkan alamu yau da hannun hagu ta tashi daga bacci.
Ta bude idonta ta sauke su a kansa "kayi hakuri mijina ban fada da niyyar in bata maka rai ba, kawai dai ji nayi nawa ran ya baci kuma ban san na fada maka haka ba" ya sake ta, ta fada din kenan, bawai kunnensa ne bai ji masa dai dai ba wai imagination dinsa bane ba Hassana ce tace gidansa ba gidan arziki bane ba, da Hussain ne zaiyi abinda shi ba zaiyi ba.
Tana jin ya sake ta ta juya da sauri ta fita tare da rufe kofar, da ace da key a hannunta ma da rufe shi zata yi ta waje dan ita kan ta tsorata da fuskarsa da kuma rikon da yayi mata. Amma wannan bai hana ta shiga dakin ta ta dauko kudi ta fito gurin kawayenta suka cigaba da hidimar su ba. Sai da suka gama sannan ta fito da kudin ta basu tace inji Hassan yace suyi kudin mota. Minal tace "shi wannan mijin naki wallahi da kayan haushi yake, maimakon ma yace ga driver nan a waje a kai kowa gidansu sai ya wani bamu kudi?" Daya a cikin kawayen ta karbe kudin tana lissafawa tace "mu dai muna so, ke dan kin samu zaki shiga daga ciki shine har zaki yi yanga in an baki kudi?" Suka raba kayansu kowa ta saka a jakarta. Ruqayyah tabi jakankunan su da kallo tana hadiye daci a ranta, ta jima tana tara kudin nan tana son siyan wata sarka.
Da zasu tafi Minal ta jata kefe "to sai kin shigo dinner gobe" Ruqayyah tayi ajjiyar zuciya "dinner nan Minal ba lallai bane in shigo ta" Minal ta bude ido "amma kuwa da kin cika babbar marar m...dinner din bikin nawa zaki ki zuwa" Ruqayyah tace "ba cewa nayi ba zan zo ba, cewa nayi ba lallai bane inzo din, kin san ai komai sai Allah yayi ko? Ku tafi kawai, zamu yi waya zan baki labarin abinda yasa nace haka" Minal ta bata rai "ko ma menene ni ba uzuri bane ba a gurina, kuma in baki zo dinner ba wallahi nasan matsayina a gurin ki kuma na san kema a gurin da zan a jiye ki a zuciyata" Ruqayyah dai ta lallabata ta raka ta waje suka shiga motar da alhajin ta ya aiko ta dauke su.
Ta gefen idonta ta hango Adam yana fitowa daga part din Hussain yana tafiya hanyar shiga part din Aunty, a can yaje tare da sauran yaran Hussain a tsofaffin dakunan su Hassan. Ya saka hannunsa a aljihu yana taku dai dai jikinsa sanye da kaya masu kyau, in ka ganshi zaka iya tunanin kanin mai gidan ne dan yarintar sa ce kawai zata sa ba zaka ce shine mai gidan ba. Tayi tsaki, ta tsane shi har cikin zuciyarta, ya tsani guts dinsa, yadda yake tafiya da yadda yake magana da komai nasa. More importantly ta tsani alakar sa da only sister dinta. God knows tana son Sumayya har cikin ranta kuma zata yi iyakacin kokarin ta ta ga cewa alakar Sumayya da wannan tubabben bata cigaba ba, bata je inda su suke son taje dinba. She can't imagine having nephews and nieces masu Christian blood a jikin su, masu kama da kedarai. Ta kara tsaki tana juyawa cikin gidan ta, dole zata nemi hanyar raba wannan alakar duk da tasan ba zata samu goyon baya daga Sumayyan ba ko Baba ko Inna but duk da haka she will find a way, zata yi shawara da zuciyarta kuma tadan zata samu mafita kamar yadda kullum zuciyar tata take bata mafita a duk problems dinta. Yanzu ma already ta bata mafita akan problem dinta da Hassan.
A palo ta fara tsayawa tana bawa yaran ta directives na yadda zasu gyara gidan, sannan tayi musu sallama ta hau sama. Dakin ta ta shiga ta fara yin wanka ta shirya cikin kayan bacci masu daukan hankali ta dauko ajjiyoyin kayan matan ta ta sha na sha ta shafa na shafawa. Tunda suka yi aure bai taba resisting dinta ba kuma bata jin zai fara daga yau.
Tunda Ruqayyah ta juya ta fita Hassan ya zame ya zauna a bakin gado ya dafe kansa da hannayensa biyu. "What just happened? What happened to his perfect precious wife? Did she just said what she said ko kuma zuciyarsa ce take playing tricks on him? Ta tabbas there must be an explanation to her behavior ko dai yayi mata wani laifi ne mai girma da out of anger ta fada masa haka? Amma shi duk a tunaninsa bai tuno wani abu da yayi mata marar dadi ba.
Ya tuna a yanayin da ta gaya masa maganar, babu wani emotions irin kamar normal mutum yana magana ne directly from her heart, daga dukkan alamu itama bata san ta fada ba sai bayan data fada din. Zuciyarsa tana ta kokarin kawo masa wani excuse da zai kare ta amma kwakwalwar sa taki karbar excuse din, sai ma wadansu maganganu da suke fado masa a rai.
Farko maganar Baba "zan so ka janye auren Hassana ka auri Hussaina a madadin ta"
Hussain "in har zata iya yaudarar top criminals ta haka mudu rami su fada ciki why not you?"
Sumayya "kayi ta hakuri, kana addu'a kuma kana saka ido".
Ya mike yana jiyo karar kidan da suka kunna a kasa, Yusuf ya fara kuka, ya dauke shi yana rarrashinsa, Aminu ya saka kuka shima yana miko masa hannu, ya durkusa shima ya dauke shi yana zagaya wa dasu a hannunsa yana raba idonsa a tsakanin fuskokin su. Sai ya samu kansa da tambayar kansa
"Did he make the worse choice for the most important thing?"
"Did he chose a bad wife for himself and a bad mother for his children?"
Where was his carefulness?
Ya shiga da yaran toilet dinsa ya saka su a wash hand basin ya wanke musu jikin su da ruwan dimi, suna ta wasa suma jika shi, ya fito da su ya kashe acn dakin ya goge musu jiki sannan yaje dakinta ya samo musu kaya yazo ya saka musu, ya koma ya dauki madara ya hada musu ya basu, a take suka yi bacci ya kwantar dasu yana kallon su sannan shima ya kwanta a tsakiyar su tare da rufe idonsa, amma bacci shine abu na karshe a zuciyarsa.
"At least haka akeyi a gidan arziki, da Hussain ne da haka zaiyi va wai ya zauna yana complain akan abinda akayi shekara guda data wuce ba"
Ya girgiza kansa yana son ya cire maganar ta daga cikin kansa amma ya kasa. A haka yaji ta bude kofar dakin ta shigo ta tsaya tana kallon su
Ta dan jima a tsaye tana assessing din sa shi da yayansa, yaran bacci suke yi amma shi tana kallonsa ta san idonsa biyu rufe idon kawai yayi. Ta karasa tare da dauke Yusuf ta mayar dashi kusa da dan uwansa sannan ta zauna a inda ta dauke shin tana dora hannunta akan goshin Hassan. Ya bude ido yana kallon ta, tayi masa murmushi "dama nasan ba kayi bacci ba shine ka wani rufe ido ko?" Bai ce mata komai ba amma ta hango wani bakon al'amari a cikin idon nasa, tace "wai fushi kake yi dani mijina? Kayi hakuri mana dan Allah ai kasan dai babu wani wanda yake baya kuskure a rayuwa ko? Nayi kuskure, raina ne naji ya baci a lokacin ka yafe min kaji mijina?" Sai taga yayi dan murmushi, a take taji hankalin ta ya kwanta, dama ta san babu inda fushin nasa zai je in dai har ta bayar da hakuri musamman kuma ace da wannan shigar a jikinta tana kuma wannan kamshin ai magana ta riga ta wuce. Sai taji yace "ranki ne ya baci ko? Kinsan wani abu. A lokacin da ran mutum ya baci a lokacin ne yake fadar duk abinda yake cikin zuciyarsa, so chances are very high cewa abinda yake zuciyarki shi kika fada min" ya fada idanuwan sa cikin nata.
Ta fara jujjuya hannunta tana kokarin controlling anger dinta tace "don't be like that mana, haba mijina, ya kamata kayi min uzuri mana. Nima fa ina da zuciya a kirjina, kuma zuciyata tana son irin rayuwar su Hussain da matarsa yadda suke wadaka da dukiya suna zuwa duk ƙasar da suka ga dama a lokacin da suka yi niyya. What do you expect your wife to do? How do you expect me to feel bayan ka kawo ni ina zaune da kanin ka da yake da everything while you have nothing?"
Ya mike zaune yana kankance idonsa a kanta, "do you just said "nothing"? Do you mean I have nothing?" Ta juya idonta, yau me yake faruwa ne da ita? Me yasa bata da sa'ar magana ne? Daga dukkan alamu yau da hannun hagu ta tashi daga bacci.