Sashe 8
Tagwaye Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Direct gida ya koma, yana ta lissafin abubuwan da suke gabansa abubuwan da ya kamata ya yi kafin dawowar Hussain daga Beijing. Dazu dai yayi wa kananan ma'aikatan da za'a dauka aiki a sabon kamfanin interview kuma har ya riga yayi grading dinsu, sai ya zauna zai yi final zabe sannan sai a kira wadanda aka zaba din a sanar musu. Shi komai yafi so yayi a hankali, ya tuna yadda suka yi da Hussain a lokacin da suke maganar daukan ma'aikatan. "Kaga Hassan, don't stress yourself akan maganar nan. Kananan ma'aikata ake magana fa ba manyan ma'aikata ba, ba takardu zaka duba ba ba komai ba, kawai just look at their physique ka tambaye su akan past experiences dinsu shikenan. Wanda kaga ya dace ka bashi aiki kawai a take wanda bai dace ba ka sallame shi kace masa babu aiki dan kar yaje gida yayi ta saka ran zai samu"
Hassan yace "so kake mu dauki baragurbi kenan mu bar masu kyau? Ai shi lamari na daukan ma'aikata a nutse ake bi ayi interview idan da hali ma sau biyu dan aga mai juriya, ni har medical certificate nake so suje suyi saboda in tabbatar da lafiyar su, sannan sai na zauna a nutse sai in tace wanda naga sun cancanta" Hussain ya mike tsaye yana bude hannu yace "do whatever you want. Ni dai abinda na sani shine, duk wanda Allah ya tsara yana da rabon samun aiki a *H and H* ko ka bashi yau ko kuma kayi ta delaying sai nan da shekara daya still dai sai ya samu. To gwara ka bashi ka huta shima kuma ya huta".
Hassan yayi murmushi yana kashe motar bayan yayi packing a compound din gidan su. Tun suna yara kusan kullum sai sunyi irin wannan musun kuma har yau babu wanda ya taba chanza ra'ayin danuwansa.
Ya shiga gidan. A kan dining ya hango yar autar su Zulaihat da takardu a gabanta tana karatu, shirye shiryen ssce take yi dan yanzu haka sun kusa kammala neco sauran su waec. Dama ita kadai ta rage a secondary School sauran yammatan duk suna jami'a dan Hassana har ta kammala ta kuma yi service dinta, ta kuma samu mijin aure dan yanzu so ake yi ma a hada bikin nata dana Hussain.
Zulaihat ta amsa sallamar sa tana binsa da kallo sannan ta kalli bayansa da sauri sai kuma ta sake kallonsa "ina yake?" Ta fada tana kara kallon kofa. Ya jawo kujera a can karshen dining table din ya zauna tare da jawo food warmer din daya gani a gurin, yasan duk gidan sunfi son Hussain a kansa, sunfi sabawa da Hussain saboda ya fi shi faran faran da wasa da dariya, ya fishi kuma kashe musu kudi da shagwaba su, shima kuma yana taya su son Hussain din. Ta sake tambaya "yaya H1 ina yaya H2 yake? Bai dawo daga kanon ba?" Ya fara zuba abinci sannan yace mata "ya tafi China" ta bude ido da baki tana kallonsa sannan ta ajiye littafin hannunta ta tashi a guje ta tafi saman Aunty. Yayi murmushi yana cigaba da zuba abincinsa. Sai daya fara ci sannan yaji saukowarsu kusan gabaki dayansu . Duk suka taho inda yake, Aunty ta zauna a kujera tana kallonsa "ina Hussaini?" Ya dago kai shima yana kallonta yace "ya tafi China, suna kan hanya ma yanzu".
Ta fara fada "yanzu lamarin Hussain har ya kai haka Hassan? yanzu ni a gidan nan ban ma isa a gaya min in za'ayi tafiya ba ballantana in saka ran za'a nemi izini na kafin ayi? Yanzu har sai yayi tafiyar ma sannan zai aiko ka ka gaya min?" Bai ce komai ba har ta gama fadanta sannan ya ajiye spoon din hannnunsa yana kallonta yace "tsakanin ku ne Aunty, kun fi kusa. Nasan in ya sauka zai kira ki sai ki yi masa fadan. Nima sai dana gaya masa rashin dacewar hakan amma sai yayi min bayanin cewa in ya gaya miki hana shi tafiya zakiyi kuma in kika riga kika hana shi ba zai iya tsallake maganar ki ba, sannan kuma tafiyar mai muhimmanci ce sosai saboda injinan da za'a yi amfani dasu a sabon Companyn yin flour nan su zai siyo, in ya aika kuma za'a iya siyo masa fake shi yasa ya tafi da kansa. Kinsan halin Hussain, he settled for nothing less than the best"
Tayi shiru tana tunani, yayin da yammatan suka fara mita, Safiyya tana korafin ai yayi mata alkawarin tare zasu tafi kuma shine ya tafi ya barta. Aunty tace "yanzu yaushe zai dawo kenan?" Hassan yace "sati daya yace zaiyi" tayi ajiyar zuciya tace "Allah ya kaimu, ya kuma dawo mana dashi lafiya. Ni wallahi na ƙagu azo ayi bikin nan nasa ko zai rage wannan yawon, tunda naga yana son Fatima sosai dole zai ke son zama anan tare da ita" Hassan yayi murmushi yace "in yana son yawon zai iya daukan matarsa su tafi tare, menene a ciki?" Aunty ta bata rai "don't put that idea into his head" yayi dariya yana bude hannu "nayi shiru. Amma ina tunanin already idea din tana cikin kan nasa sai mu jira ayi auren mu gani. Hussain ne fa, bana jin aure zai saka ya zauna guri daya"
Suka yi shiru gabaki daya, Hassan yana cin abincin sa amma kuma yana jin idon Aunty a kansa, take ya fahimci tunanin me take yi, sai yaji tace "kai kuma fa?" Ya gane me take nufi amma sai yayi keeping blank expression yace "ni kuma me aunty? Ni ma yaushe zan tafi chinan?" Ta hade rai tace "kai ma yaushe zaka yi auren? shine abinda nake tambaya, kai ko budurwar nan ma ta zamani baka da ita, kaki kula duk yammatan da suke sonka"
Nafisa tayi saurin cewa "ai kuwa Aunty akwai wata course mate dina, baki ga yadda take son shi ba, kullum sai ta tambaye ni ina yake" ya harare ta yace "hala bata ga Hussain ba? Am sure tana ganin sa zata ce shi take so bani ba" Aunty tace "Hussain ai ya riga ya samu matarsa, a very good girl from a very good family. Family dinta is one of the best a duk fadin kasarnan. Kai ma ya kamata ka kara kokari ka samo wa Fatima yaruwa" ya shafa kai yace "za'a samo wa Fatima yaruwa Aunty, amma sai a hankali, kuma ba irin Fatima za'a samo ba dan ni bana son abinda yake all covered in gold and praises. Saboda nasan most of the books with good cover basu da good contents. Ni am more interested in the content" Aunty tana girgiza kai tace "ai kuwa ana samu Hassan, ana samun wanda yake da goodness in both the cover and the content, ko ita fatiman ai haka muke fata" ya girgiza kansa yace "I am not going to take that risk gaskiya, nafi son in nayi aure ya zamana har abada, mace daya in na samu irin wadda nake so ta ishe ni har abada. Nafi son in auri mace from a lower background than ours, yadda ba xata ke looking down on us ba, yadda zata ke girma ma ku iyaye na kuma ba zata ke yiwa sisters dina magana anyhow ba kamar yadda take yiwa bayin gidansu. Nafi son wadda duk abinda na bata, no matter how small zata yi appreciating ba zata raina ba saboda ta saba da wanda yafi shi. Nafi son me low life style irin nawa not extravagant kamar Fatima"
Aunty tace "to Allah ya kawo mana ita, Allah yayi muku zabin alkhairi baki daya" ya amsa da ameen. Sun jima suna hira, yana updating dinta akan shirye shiryen bude sabon company, sai gata ta dauko masa wani dogon list wai daga Gombe aka aiko dashi inji uncles da auntys dinsu na mutanen da suke so a dauka aiki. Ya karba kawai yayi murmushi amma shi a ransa yasan babu wanda zai bawa aiki sai wanda ya cancanta sai dai duk abinda za'a ce ace.
Daga nan part dinsu ya nufa, ya shiga palo yana karewa luxurious kujerun da suka kawata falon kallo, amma last dawowar Hussain daga Japan yana shigowa palon cewa yayi "what? Wannan kujerun har yanzu ba'a cire suba? Wadannan ai sun zama old models yanzu sam ba'a yayinsu" Hassan yayi murmushi yana jin kewar danuwan nasa, Hussain sarkin rikici. Ya bude kofar dakinsa ya shiga, komai tsaf tsaf kamar yadda ya barshi. Yayi wanka ya chanja kayansa zuwa kanana sannan ya fito ya rufe dakinsa ya shiga na Hussain. Komai na dakin abin kallone, ko bakasan kudin kaya ba kana shiga dakin zaka san cewa tabbas an kashe kudi a gurin tsara dakin zuwa kayan da aka zuba a ciki. Sanda Hussain zaiyi renovating babu yadda baiyi da Hassan ba amma yaki yarda a gyara masa nasa dakin "ni dakina babu abinda yayi bana bukatar a gyara min shi, wannan ai almubazzaranci ne, Ni fa da ka ganni yanzu zan iya yin 10 years nan gaba ba tare dana chanza komai a dakina ba".
Sai dai Kamar yadda Hassan yayi tsammani a hargitse dakin yake, kaya sun kai set goma duk a baje a kan gado kuma yasan duk a kokarin shirin zuwa gurin Gimbiya ne aka hargitsa kayan. Yayi tsaki kawai ya wuce wata drawer ya dauko takardar da yazo nema, sketch ne na sabon companyn da ake gina wa wanda kusan an gama komai yanzu, finishing touches kawai ake yi. Ya dauka ya fita, a compound din gidan ya kira wani amintaccen yaron su Salisu, salisu tun babansu yana da rai yake gidan shi da babansa, bayan rasuwar baban nasa sai Hassan da Hussain suka cigaba da zama dashi a matsayin amintaccen su wanda shi kadai yake da access da dakunan kwanan su da abincin su da komai nasu da yake personal, yace "kaje ka gyarawa Hussain dakinsa, ni zanje site sai magrib zan dawo" sannan ya ja motar ya tafi.
Hassan yace "so kake mu dauki baragurbi kenan mu bar masu kyau? Ai shi lamari na daukan ma'aikata a nutse ake bi ayi interview idan da hali ma sau biyu dan aga mai juriya, ni har medical certificate nake so suje suyi saboda in tabbatar da lafiyar su, sannan sai na zauna a nutse sai in tace wanda naga sun cancanta" Hussain ya mike tsaye yana bude hannu yace "do whatever you want. Ni dai abinda na sani shine, duk wanda Allah ya tsara yana da rabon samun aiki a *H and H* ko ka bashi yau ko kuma kayi ta delaying sai nan da shekara daya still dai sai ya samu. To gwara ka bashi ka huta shima kuma ya huta".
Hassan yayi murmushi yana kashe motar bayan yayi packing a compound din gidan su. Tun suna yara kusan kullum sai sunyi irin wannan musun kuma har yau babu wanda ya taba chanza ra'ayin danuwansa.
Ya shiga gidan. A kan dining ya hango yar autar su Zulaihat da takardu a gabanta tana karatu, shirye shiryen ssce take yi dan yanzu haka sun kusa kammala neco sauran su waec. Dama ita kadai ta rage a secondary School sauran yammatan duk suna jami'a dan Hassana har ta kammala ta kuma yi service dinta, ta kuma samu mijin aure dan yanzu so ake yi ma a hada bikin nata dana Hussain.
Zulaihat ta amsa sallamar sa tana binsa da kallo sannan ta kalli bayansa da sauri sai kuma ta sake kallonsa "ina yake?" Ta fada tana kara kallon kofa. Ya jawo kujera a can karshen dining table din ya zauna tare da jawo food warmer din daya gani a gurin, yasan duk gidan sunfi son Hussain a kansa, sunfi sabawa da Hussain saboda ya fi shi faran faran da wasa da dariya, ya fishi kuma kashe musu kudi da shagwaba su, shima kuma yana taya su son Hussain din. Ta sake tambaya "yaya H1 ina yaya H2 yake? Bai dawo daga kanon ba?" Ya fara zuba abinci sannan yace mata "ya tafi China" ta bude ido da baki tana kallonsa sannan ta ajiye littafin hannunta ta tashi a guje ta tafi saman Aunty. Yayi murmushi yana cigaba da zuba abincinsa. Sai daya fara ci sannan yaji saukowarsu kusan gabaki dayansu . Duk suka taho inda yake, Aunty ta zauna a kujera tana kallonsa "ina Hussaini?" Ya dago kai shima yana kallonta yace "ya tafi China, suna kan hanya ma yanzu".
Ta fara fada "yanzu lamarin Hussain har ya kai haka Hassan? yanzu ni a gidan nan ban ma isa a gaya min in za'ayi tafiya ba ballantana in saka ran za'a nemi izini na kafin ayi? Yanzu har sai yayi tafiyar ma sannan zai aiko ka ka gaya min?" Bai ce komai ba har ta gama fadanta sannan ya ajiye spoon din hannnunsa yana kallonta yace "tsakanin ku ne Aunty, kun fi kusa. Nasan in ya sauka zai kira ki sai ki yi masa fadan. Nima sai dana gaya masa rashin dacewar hakan amma sai yayi min bayanin cewa in ya gaya miki hana shi tafiya zakiyi kuma in kika riga kika hana shi ba zai iya tsallake maganar ki ba, sannan kuma tafiyar mai muhimmanci ce sosai saboda injinan da za'a yi amfani dasu a sabon Companyn yin flour nan su zai siyo, in ya aika kuma za'a iya siyo masa fake shi yasa ya tafi da kansa. Kinsan halin Hussain, he settled for nothing less than the best"
Tayi shiru tana tunani, yayin da yammatan suka fara mita, Safiyya tana korafin ai yayi mata alkawarin tare zasu tafi kuma shine ya tafi ya barta. Aunty tace "yanzu yaushe zai dawo kenan?" Hassan yace "sati daya yace zaiyi" tayi ajiyar zuciya tace "Allah ya kaimu, ya kuma dawo mana dashi lafiya. Ni wallahi na ƙagu azo ayi bikin nan nasa ko zai rage wannan yawon, tunda naga yana son Fatima sosai dole zai ke son zama anan tare da ita" Hassan yayi murmushi yace "in yana son yawon zai iya daukan matarsa su tafi tare, menene a ciki?" Aunty ta bata rai "don't put that idea into his head" yayi dariya yana bude hannu "nayi shiru. Amma ina tunanin already idea din tana cikin kan nasa sai mu jira ayi auren mu gani. Hussain ne fa, bana jin aure zai saka ya zauna guri daya"
Suka yi shiru gabaki daya, Hassan yana cin abincin sa amma kuma yana jin idon Aunty a kansa, take ya fahimci tunanin me take yi, sai yaji tace "kai kuma fa?" Ya gane me take nufi amma sai yayi keeping blank expression yace "ni kuma me aunty? Ni ma yaushe zan tafi chinan?" Ta hade rai tace "kai ma yaushe zaka yi auren? shine abinda nake tambaya, kai ko budurwar nan ma ta zamani baka da ita, kaki kula duk yammatan da suke sonka"
Nafisa tayi saurin cewa "ai kuwa Aunty akwai wata course mate dina, baki ga yadda take son shi ba, kullum sai ta tambaye ni ina yake" ya harare ta yace "hala bata ga Hussain ba? Am sure tana ganin sa zata ce shi take so bani ba" Aunty tace "Hussain ai ya riga ya samu matarsa, a very good girl from a very good family. Family dinta is one of the best a duk fadin kasarnan. Kai ma ya kamata ka kara kokari ka samo wa Fatima yaruwa" ya shafa kai yace "za'a samo wa Fatima yaruwa Aunty, amma sai a hankali, kuma ba irin Fatima za'a samo ba dan ni bana son abinda yake all covered in gold and praises. Saboda nasan most of the books with good cover basu da good contents. Ni am more interested in the content" Aunty tana girgiza kai tace "ai kuwa ana samu Hassan, ana samun wanda yake da goodness in both the cover and the content, ko ita fatiman ai haka muke fata" ya girgiza kansa yace "I am not going to take that risk gaskiya, nafi son in nayi aure ya zamana har abada, mace daya in na samu irin wadda nake so ta ishe ni har abada. Nafi son in auri mace from a lower background than ours, yadda ba xata ke looking down on us ba, yadda zata ke girma ma ku iyaye na kuma ba zata ke yiwa sisters dina magana anyhow ba kamar yadda take yiwa bayin gidansu. Nafi son wadda duk abinda na bata, no matter how small zata yi appreciating ba zata raina ba saboda ta saba da wanda yafi shi. Nafi son me low life style irin nawa not extravagant kamar Fatima"
Aunty tace "to Allah ya kawo mana ita, Allah yayi muku zabin alkhairi baki daya" ya amsa da ameen. Sun jima suna hira, yana updating dinta akan shirye shiryen bude sabon company, sai gata ta dauko masa wani dogon list wai daga Gombe aka aiko dashi inji uncles da auntys dinsu na mutanen da suke so a dauka aiki. Ya karba kawai yayi murmushi amma shi a ransa yasan babu wanda zai bawa aiki sai wanda ya cancanta sai dai duk abinda za'a ce ace.
Daga nan part dinsu ya nufa, ya shiga palo yana karewa luxurious kujerun da suka kawata falon kallo, amma last dawowar Hussain daga Japan yana shigowa palon cewa yayi "what? Wannan kujerun har yanzu ba'a cire suba? Wadannan ai sun zama old models yanzu sam ba'a yayinsu" Hassan yayi murmushi yana jin kewar danuwan nasa, Hussain sarkin rikici. Ya bude kofar dakinsa ya shiga, komai tsaf tsaf kamar yadda ya barshi. Yayi wanka ya chanja kayansa zuwa kanana sannan ya fito ya rufe dakinsa ya shiga na Hussain. Komai na dakin abin kallone, ko bakasan kudin kaya ba kana shiga dakin zaka san cewa tabbas an kashe kudi a gurin tsara dakin zuwa kayan da aka zuba a ciki. Sanda Hussain zaiyi renovating babu yadda baiyi da Hassan ba amma yaki yarda a gyara masa nasa dakin "ni dakina babu abinda yayi bana bukatar a gyara min shi, wannan ai almubazzaranci ne, Ni fa da ka ganni yanzu zan iya yin 10 years nan gaba ba tare dana chanza komai a dakina ba".
Sai dai Kamar yadda Hassan yayi tsammani a hargitse dakin yake, kaya sun kai set goma duk a baje a kan gado kuma yasan duk a kokarin shirin zuwa gurin Gimbiya ne aka hargitsa kayan. Yayi tsaki kawai ya wuce wata drawer ya dauko takardar da yazo nema, sketch ne na sabon companyn da ake gina wa wanda kusan an gama komai yanzu, finishing touches kawai ake yi. Ya dauka ya fita, a compound din gidan ya kira wani amintaccen yaron su Salisu, salisu tun babansu yana da rai yake gidan shi da babansa, bayan rasuwar baban nasa sai Hassan da Hussain suka cigaba da zama dashi a matsayin amintaccen su wanda shi kadai yake da access da dakunan kwanan su da abincin su da komai nasu da yake personal, yace "kaje ka gyarawa Hussain dakinsa, ni zanje site sai magrib zan dawo" sannan ya ja motar ya tafi.